03/11/2020
J A N H A N K A L I T A R E D A N A S I H A Z U W A G A D U K’K A N I N A L’ U M M A R I S L A M A.
Yin barna ko yadata ko wacce iri ce bana goyon bayanta.
Lallai shigar tsiraici ga mace musulma, sharri ne mummuna mai girma gareta, da kuma Al’ummar da take cikinsu. Kuma shigar zubar da mutuncin family din ta ne.
Rashin Magana akan wannan yana daidai da kace a cigaba da aikatawa. Ita kuma Uqubar Allah in ta tashi zuwa zata shafi kowa da kowa’ne. Badoline sai kasan menene mafarinta’ba.
Allah yakara shiryardamu.
Nasiha da jan hankali ba da tozarci ba.
Itace hanya mafi kyau da tadace musulmi yayiwa dan uwansa musulmi Nasiha, akan wata barna da yake aikatawa.
Ita dai Dabi’ar shigar banza nema take ta zama ruwan dare, konace tazama ruwan’daren ga Al’ummarmu.
Abu ne da yake faruwa a rayuwar Yau da kullum, mu duba gidajen biki, Gidan suna, tarurruka, makarantu, tun daga primary zakaga wasu yara mata na tafiya kansu babu DANKWALI sai gashin kansu a daure, ballantana aje secondary ko Universities, kuma dukkan wadan’nan abubuwa suna faruwane a gaban.👇🏻👇🏻👇🏻
IYAYE, MALAMAI, YAYYE, KAWUNNAI, DA KUMA SHUWAGABAN’NINMU.
MACCE TANADA DARAJA. A Gyaruwarta kuma a gyaruwar Al’ummarmu, mu tashi tsaye akan fahimtar’dasu, kunyarsu da mutuncinsu. Domin gyaran ‘Yayanmu masu zuwa anan gaba.
RASULILLAH ANNABI MUHAMMAD (S.A.W)
Yace”👇🏻👇🏻👇🏻
Dukkaninku masu kiwo ne, kuma kowannenku za a tambayeshi game da abin da aka bashi kiyo, a ranar gobe al’qiyama.
Kofar tuba a bude take ga dukkan wanda yayi kuskure, yayi gaggawar Istighfari yafi Jinkirin yinsa.
Dukkanin’mu masu aikata laifuka ne, Allah ne yake rufamuna asirin. Ya Allah kakara karemu ka’kare mutuncinmu. Duniya da lahira Ameen ya rabbi 👏🏻👏🏻👏🏻
A cigaba da addu’ar neman yafiyar Allah, tareda gafararsa. Ina fatan Allah yakara rufamuna asiri, duniya da lahira Ameen ya hayyu ya qayyimu.🤲🏻
DAGA KARSHE.
Ga Hadisin Annabin tsira (S.A.W) akan masu FIDDA TSIRAICI👇🏻👇🏻👇🏻
Yace;👇🏻👇🏻👇🏻
"A karshen zamani za’a samu wasu mata ga tufafi a jikinsu amma tsirara suke, tufafinsu bai rufe tsiraicin suba."
RASULULLAH (S A W)Yace;👇🏻👇🏻👇🏻
“A TSINE musu, domin su din TSINANNUNE."
RASULULLAH (S A W) Yakara da cewa;👇🏻👇🏻👇🏻
Wallhi ko Kamshin ALJANNA baza su ji ba.”😢😫
Ina addu’ar;” Ubangiji Allah yakara fahimtardamu yakara shiryardamu, tareda zuriarmu da dukkan al’ummar musulmi baki daya. Allahumma Ameen ya Allah.🤲🏻🤲🏻🤲🏻
Wajibine Mazanmu da Matanmu mu tashi mu yaki Shaidan La’anannen Allah, Yadda baibar Uban Talikai Annabi Adamu ba, haka muma bazai bar mu ba. Yakinsa kullum shine yasa mu kaucewa hanyar Allah mubi tasa batacciyar hanya marar bullewa.
Allah ya shiryemu baki daya ya tsare mu biyewa son zuciyarmu.
Ameen ya Allah 👏🏻👏🏻👏🏻