
30/07/2025
Kakakin Majalisar Wakilai ta Ƙasa, Tajudeen Abbas, ya nuna damuwa kan yawaitar rashin aikin yi da ake fama da shi tsakanin matasa, inda ya bayyana cewa kashi 55% na matasan Najeriya ba su da aikin yi ko kuma ba su da cikakkiyar damar yin aiki saboda rashin kwarewar fasaha da ake buƙata a kasuwar aiki ta zamani. Yayin wani zaman sauraron ra’ayoyi da Kwamitin Majalisar kan Makarantun Fasaha da Na’urorin Zamani ya shirya a Abuja, Kakakin ya jaddada bukatar samar wa matasa horo da ƙwarewar hannu don su dace da buƙatun kasuwar aiki da ke ci gaba da sauyawa sak**akon fasahohin zamani k**ar Artificial Intelligence, Robotics, da Big Data.
wakilci Kakakin Majalisar daga Auwal Gwadabe (PDP, Bauchi), wanda ya ce Majalisar ta 10 tana da cikakken shiri na inganta ilimin fasaha da na ƙwarewar hannu ta hanyar ajandar dokokinta. Ya ce an kafa cibiyoyin fasaha ne domin ba matasa damar samun ilimi mai inganci da zai ba su ƙwarewar da za su iya dogaro da kansu a rayuwa. Shugaban kwamitin, Kayode Laguda, shi ma ya jaddada muhimmancin bunkasa ilimin kasuwanci da ƙwarewar hannu a tsakanin matasa domin rage rashin aikin yi da samar da hanyoyin dogaro da kai.
A nasa bangaren, Solomon Wombo, wanda ya dauki nauyin kudurin kafa Kwalejin Koyar da Sana’o’i da Kasuwanci a Zaki Biam, Jihar Benue, ya bayyana cewa wannan kwaleji za ta cike gibi a ilimin sana’a da kasuwanci. Ya ce za ta ba da horo na musamman a fannoni da dama k**ar noma, kasuwanci da fasaha, tare da karfafa gwiwar matasa su dogara da kansu maimakon jiran aikin gwamnati. Ya kara da cewa hakan zai taimaka wajen rage rashin aikin yi, bunkasa tattalin arzikin yankuna, da kuma amfani da hazaka da kuzarin matasa don ƙirƙirar arziki.