ZRN Hausa

ZRN Hausa Zuma Reporters Network: Tushen sahihan labarai ne na cikin gida, binciken gaskiya, da tattaunawar jama’a da ke kawo sauyi.

~ Muryar Gaskiya.

Kakakin Majalisar Wakilai ta Ƙasa, Tajudeen Abbas, ya nuna damuwa kan yawaitar rashin aikin yi da ake fama da shi tsakan...
30/07/2025

Kakakin Majalisar Wakilai ta Ƙasa, Tajudeen Abbas, ya nuna damuwa kan yawaitar rashin aikin yi da ake fama da shi tsakanin matasa, inda ya bayyana cewa kashi 55% na matasan Najeriya ba su da aikin yi ko kuma ba su da cikakkiyar damar yin aiki saboda rashin kwarewar fasaha da ake buƙata a kasuwar aiki ta zamani. Yayin wani zaman sauraron ra’ayoyi da Kwamitin Majalisar kan Makarantun Fasaha da Na’urorin Zamani ya shirya a Abuja, Kakakin ya jaddada bukatar samar wa matasa horo da ƙwarewar hannu don su dace da buƙatun kasuwar aiki da ke ci gaba da sauyawa sak**akon fasahohin zamani k**ar Artificial Intelligence, Robotics, da Big Data.

wakilci Kakakin Majalisar daga Auwal Gwadabe (PDP, Bauchi), wanda ya ce Majalisar ta 10 tana da cikakken shiri na inganta ilimin fasaha da na ƙwarewar hannu ta hanyar ajandar dokokinta. Ya ce an kafa cibiyoyin fasaha ne domin ba matasa damar samun ilimi mai inganci da zai ba su ƙwarewar da za su iya dogaro da kansu a rayuwa. Shugaban kwamitin, Kayode Laguda, shi ma ya jaddada muhimmancin bunkasa ilimin kasuwanci da ƙwarewar hannu a tsakanin matasa domin rage rashin aikin yi da samar da hanyoyin dogaro da kai.

A nasa bangaren, Solomon Wombo, wanda ya dauki nauyin kudurin kafa Kwalejin Koyar da Sana’o’i da Kasuwanci a Zaki Biam, Jihar Benue, ya bayyana cewa wannan kwaleji za ta cike gibi a ilimin sana’a da kasuwanci. Ya ce za ta ba da horo na musamman a fannoni da dama k**ar noma, kasuwanci da fasaha, tare da karfafa gwiwar matasa su dogara da kansu maimakon jiran aikin gwamnati. Ya kara da cewa hakan zai taimaka wajen rage rashin aikin yi, bunkasa tattalin arzikin yankuna, da kuma amfani da hazaka da kuzarin matasa don ƙirƙirar arziki.

Shugaban Rundunar Tsaro na Najeriya, Janar Christopher Musa, ya bukaci karin inganci wajen tunani na dabaru da kuma karf...
29/07/2025

Shugaban Rundunar Tsaro na Najeriya, Janar Christopher Musa, ya bukaci karin inganci wajen tunani na dabaru da kuma karfafa hadin gwiwa tsakanin dakarun sojin kasar domin fuskantar kalubalen tsaro na zamani. Janar Musa, wanda Babban Jami’in Horarwa na Tsaro, Rear Admiral Ibrahim Shettima, ya wakilta, ya bayyana haka a lokacin bude babban atisayen tsaro na kasa (STRANEX) da aka shirya a Abuja, wanda Hukumar Koli ta Tsaro (National Defence College) da Makarantun Yakin Sojoji s**a shirya. Ya bayyana atisayen a matsayin ginshikin nagarta da dabarar aiki a fagen tsaron karni na 21.

Atisayen STRANEX ya tattaro kwararrun shugabannin soja, manyan jami’an gwamnati, da wakilai daga kasashen duniya, ciki har da Majalisar Dinkin Duniya, domin gudanar da atisayen kwaikwayo kan yadda za a fuskanci rikice-rikicen tsaro na kasa. Janar Musa ya bayyana cewa hadin kai da kwarewar dabarun aiki a irin wannan mataki yana taimakawa wajen karfafa tsare-tsare, hadin kai, da kuma cimma manufa daya a cikin rundunonin tsaro. Ya yaba da kasancewar masu lura daga kasashen waje, yana mai cewa hakan alama ce ta hadin gwiwar kasa da kasa wajen zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Kwamandan Makarantar Tsaro ta Kasa, Rear Admiral James Okosun, ya bayyana cewa atisayen na STRANEX na nufin shirya shugabannin soja na gaba wajen shawo kan rikice-rikicen tsaro a yanayi mai cike da rudani da rashin tabbas. Ya ce atisayen yana taimakawa wajen kwarewa a yanke shawara cikin gaggawa, da fahimtar yadda hukumomi ke fuskantar matsaloli, tare da karfafa tunanin aiki tare tsakanin bangarorin tsaro. A cewarsa, dole ne a dauki matakai na hadin gwiwa da tsare-tsare masu zurfi domin shawo kan matsalolin tsaro da s**a ketare iyakoki.

Brigadier Janar Olumide Ojo, Daraktan Tsare-Tsaren Soji da Ayyukan Rundunoni a NDC, ya bayyana STRANEX a matsayin wani shiri na musamman da ke horar da jami’an tsaro a fannonin dabarun tsare-tsare, gudanar da rikici, yanke shawara, da sulhu. Ya ce atisayen yana da nufin karfafa fahimta daga matakin dabarun kasa har zuwa matakin gudanar da aiki, domin daidaita kokari a tsakanin bangarorin soja k**ar yadda hangen Shugaban Tsaro ya tanada. Ya bukaci mahalarta da su binciki ra’ayoyinsu, su zurfafa tunani, kuma su dauki darasi daga atisayen domin fuskantar kalubale na gaba a cikin harkokin tsaro da ci gaban kasa.

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya rantsar da sababbin shugabannin ƙananan hukumomi da na yankunan ci gaba guda...
27/07/2025

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya rantsar da sababbin shugabannin ƙananan hukumomi da na yankunan ci gaba guda 57 a wani biki da aka gudanar a gidan gwamnati dake Ikeja, ranar Lahadi. Wadannan shugabanni sun lashe zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a faɗin jihar a ranar 12 ga Yuli, 2025.

Kwamishinan harkokin ƙananan hukumomi, al’adu da cigaban karkara na jihar, Bolaji Robert, ya taya shugabannin murna tare da bayyana nasarar su a matsayin sak**akon ƙaunar da jama’a ke nuna musu da kuma sahihancin tsarin zaɓen. Ya ce nasu nasara alama ce ta dorewar dimokuraɗiyya a jihar.

Robert ya yaba wa Gwamna Sanwo-Olu bisa ƙoƙarinsa na tabbatar da dimokuraɗiyya a matakin tushe, tare da jinjinawa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa jagorancin da ya kafa wanda ke ci gaba da inganta harkar dimokuraɗiyya a ƙasa. Daga bisani, ya gabatar da sabbin shugabannin 57 ga gwamnan domin a rantsar da su k**ar yadda doka ta tanada.

Majalisar Wakilai ta tarayya ta yi gargaɗi ga Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Mista Olayemi Cardoso, tana barazana...
25/07/2025

Majalisar Wakilai ta tarayya ta yi gargaɗi ga Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Mista Olayemi Cardoso, tana barazanar bayar da sammacin k**a shi saboda kin halartar zaman kwamitin haɗaka da ke binciken rashin bin dokokin da s**a shafi biyan ragowar kuɗaɗen da aka tara daga 2016 zuwa 2022. Kwamitin Haɗin Gwiwa na Asusun Jama’a da Kadarorin Gwamnati yana binciken yadda CBN ta gaza cika ka’idodin dokar da ke buƙatar a tura ragowar kuɗin aiki zuwa baitul-mali da kuma sarrafa asusun da ba a taɓa ba da ribar hannun jari da ba a karɓa ba.

A wata sanarwa da aka fitar a ranar Juma’a, wadda shugabannin kwamitin, Bamidele Salam da Ademorin Kuye, s**a sanya wa hannu, ‘yan majalisar sun bayyana bacin ransu kan yadda Gwamnan CBN ke ci gaba da watsi da gayyatarsu. Kwamitin ya ce rahoton da Ofishin Mai Binciken Asusu na Ƙasa da Hukumar Bin Doka Kan Kuɗi s**a bayar ya nuna cewa akwai ragowar kuɗin aiki na Naira tiriliyan 5.2 da CBN ta kasa tura wa Gwamnatin Tarayya. Dokar Kuɗi ta 2020 ta bayyana cewa duk wata riba ko asusun da ba a taɓa ba tsawon shekara shida ya zama dole a tura shi zuwa Asusun Amana na Kuɗaɗen da Ba a Karɓa ba.

Kwamitin ya umurci Babban Bankin Najeriya da ya biya Naira tiriliyan 3.64 cikin kwanaki 14 daga ranar 27 ga Yuni, 2025 – kashi 70% na adadin da ba a sabani akai. Haka kuma, an bukaci CBN da ta bayyana jimillar ribar hannun jari da asusun da ba a taɓa ba kafin 30 ga Yuni, 2025. ’Yan Majalisar sun jaddada cewa CBN dole ne ta bi dokar da ta dace, wato Finance Act 2020, ba Financial Institution Act ba k**ar yadda take ƙoƙarin nuna. Idan Gwamnan CBN ya ci gaba da watsi da gayyata, Majalisar ta ce za ta yi amfani da ikon da Kundin Tsarin Mulki na 1999 ya ba ta domin tilasta masa halarta.

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya nada Dr. Nentawe Goshwe Yilwatda, Ministan Harkokin Jinƙai da Bala’o’i, a matsayin sa...
24/07/2025

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya nada Dr. Nentawe Goshwe Yilwatda, Ministan Harkokin Jinƙai da Bala’o’i, a matsayin sabon Shugaban Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na ƙasa.

Nadinsa ya zo ne kafin taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na jam’iyyar da ake shirin gudanarwa, kuma yana kawo ƙarshe ga jita-jitar da ta dabaibaye wanda zai maye gurbin Dr. Abdullahi Umar Ganduje, wanda ya ajiye mukaminsa bisa dalilan lafiya.

Rahotanni daga cikin jam’iyyar sun nuna cewa zaɓen Yilwatda wani mataki ne na gyara tsarin shugabanci da kuma daidaita bambancin addini a cikin shugabannin jam’iyyar. Yilwatda, wanda ƙwararren injiniya ne kuma tsohon kwamishinan zaɓe na INEC, yana da ɗimbin gogewa a fannin gudanarwa da harkokin zaɓe.

Zaɓensa na nuni da sabon salo da jam’iyyar ke shirin ɗauka yayin da take shiryawa don gaba a fagen siyasa.

Wata kotu a Ilorin, Jihar Kwara, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Abimbola Awogboro, ta yanke wa wani matashi mai shekar...
24/07/2025

Wata kotu a Ilorin, Jihar Kwara, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Abimbola Awogboro, ta yanke wa wani matashi mai shekaru 20, Mathew Yaba, hukuncin zaman gidan yari na watanni tara ba tare da zaɓin biyan tara ba, bayan ta same shi da laifin zamba ta yanar gizo da boye kudaden da ya samu daga ayyukan haramtattu.

Yaba ya amsa cewa ya karɓi Naira miliyan 7.38 ta asusun Kuda Bank da kuma amfani da sunan wani Raleigh Jredd domin yaudarar mutane.

A cewar Dele Oyewale, Shugaban Sashen Yaɗa Labarai na Hukumar EFCC, Mathew Yaba na daga cikin mutane 11 da hukumar ta EFCC ta samu da laifi a Ilorin, a wani samame da Sashen Ilorin na hukumar ya kaddamar domin dakile ayyukan zamba da damfara ta intanet. Sauran wadanda aka yankewa hukunci sun hada da Samuel Ayomide, Bamidele Olajide, Isah Kadir, Jubril Abdulrasaq, Peter Juwon, Stephen Benefit, Kayode Opeyemi, Lasisi Abdulrahim, Michael Ikechukwu, da Abduljawad Moshood. Hukuncin ya haɗa da zaman kurkuku daga wata shida zuwa shekara guda, wasu kuma an yanke musu aikata aikin sa-kai (community service), tare da umarnin kwace dukiyoyin da s**a samu ta haram.

Mai Shari’a Awogboro da Mai Shari’a Mahmud Abdulgafar, wanda ya jagoranci shari’ar guda, sun tabbatar da hukuncin ne bayan waɗanda ake zargin sun amsa laifin da ake tuhumar su da shi, kuma an gabatar da shaidun da s**a haɗa da takardun amsa laifi, wayoyi, kwamfutoci, da kudaden fansa. Yaba, musamman, ya rasa iPhone 13 dinsa da kuma Naira 200,000 da ya dawo da su a matsayin fansa ga Gwamnatin Tarayya. Hukumar EFCC ta bayyana cewa wannan nasara wata babbar alama ce ta ƙoƙarin tabbatar da tsafta a sararin intanet da kuma hana matasa fadawa tarkon damfara.

Jam’iyyar APC ta sanar da sauya wurin gudanar da taron ta na National Executive Council (NEC) da aka shirya yi a ranar A...
23/07/2025

Jam’iyyar APC ta sanar da sauya wurin gudanar da taron ta na National Executive Council (NEC) da aka shirya yi a ranar Alhamis mai zuwa. Da farko an tsara taron ne a Hedkwatar Jam’iyyar da ke titin Blantyre, Wuse II, Abuja, amma yanzu an mayar da shi zuwa Dakin Taruka na Fadar Shugaban Ƙasa, Abuja.

Wannan sauyin wurin ya fito ne daga cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na jam’iyyar, Felix Morka, ya fitar, inda ya bayyana cewa “dalilai na shirye-shirye da tsari” ne s**a tilasta hakan.

Ana sa ran babban taron NEC ɗin zai amince da sabon Shugaban Jam’iyya na kasa, domin cike gurbin da Dr. Abdullahi Ganduje ya bari bayan murabus da ya yi a watan Yuni saboda dalilan lafiya. Tun bayan saukarsa, jam’iyyar na tafiya ba tare da sahihin shugaba ba.

Majalisar Wakilan Tarayya ta gudanar da zaman bankwana na musamman domin girmama marigayi Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari...
23/07/2025

Majalisar Wakilan Tarayya ta gudanar da zaman bankwana na musamman domin girmama marigayi Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, GCFR (1942–2025), inda aka tunatar da tarihin rayuwarsa, jagoranci da gudunmawar da ya bayar ga Najeriya.

Zaman na musamman, wanda ya ɗauki kusan sa’o’i shida, na daga cikin abubuwan da s**a gudana a zauren majalisar, kuma Mataimakin Kakakin Majalisar, Rt. Hon. Benjamin Kalu, CFR, ne ya jagoranta, haka zalika ya karanta saƙon ta’aziyya mai zurfi daga Kakakin Majalisar, Rt. Hon. Abbas Tajudeen, PhD, GCON.

“A matsayinsa na shugaban ƙasa da aka zaɓa ta hanyar dimokuraɗiyya, ya kasance amintaccen abokin hulɗa ga majalisar nan. Ya mutunta ikon majalisa kuma ya ƙarfafa tsarin raba madafun iko a Najeriya,” in ji Kakaki Abbas.

“A lokacin mulkinsa, an rattaba hannu kan dokoki 129, mafi yawansu na gyaran fuska ne da s**a shafi matsalolin tarihi kuma s**a sake fasalin tsarin doka na ƙasar.”

Shugaba Muhammadu Buhari, wanda ya kasance Shugaban Ƙasa na 15 daga shekarar 2015 zuwa 2023, ya rasu a ranar Lahadi, 13 ga Yuli, 2025, kuma an binne shi da girmamawar ƙasa a garinsa na Daura, Jihar Katsina.

Wakilai daga jam’iyyu da yankuna daban-daban sun bayyana irin girmamawa da yabo ga marigayin, inda s**a yi bayani kan salon shugabancinsa da halayensa na mutum. Daga cikin waɗanda s**a yi jawabi akwai:
• Rt. Hon. Ahmed Idris Wase (Filato), tsohon Mataimakin Kakakin Majalisa ta 9
• Hon. James Abiodun Faleke (Legas)
• Hon. Sada Soli (Katsina)
• Hon. Abubakar Hassan Nalaraba (Nasarawa)
• Hon. Ahmed Jaha (Borno)
• Hon. Miriam Onuoha (Imo)
• Hon. Aminu Jamo (Katsina)
• Hon. Lanre Okunola (Legas)

Sauran da s**a yi jawabi sun haɗa da Hon. Eze Nwachukwu (Ebonyi), Hon. Etim Martins Esin (Akwa Ibom), Hon. Muktar Tolani Shagaya (Kwara), da Hon. Mohammed Bello El-Rufai (Kaduna).

Wakilan sun yaba da ƙasaitaccen rayuwar Buhari na sauƙin kai, ƙaunar ƙasa, da ƙarfafa ikon dokoki da tsari. Sun bayyana shi a matsayin shugaba mai natsuwa da tawali’u, wanda ya haɓaka tsaron asusun gwamnati da inganta gaskiya a cikin tsarin mulki.

Zaman bankwanan ya kasance lokaci na nazari da tunawa da irin cigaban da marigayin ya samar. Majalisar ta kuduri aniyar ci gaba da tafiya kan tubalin gaskiya, rikon amana da sadaukarwa da Shugaba Buhari ya shimfiɗa

JAMI’AR IBBUL TA ƘADDAMAR DA SABBIN MUƘAMAI: FARFESOSHI 7 DA MASU DIGIRIN READER 16 SUN YI NASARAJami’ar Ibrahim Badamas...
23/07/2025

JAMI’AR IBBUL TA ƘADDAMAR DA SABBIN MUƘAMAI: FARFESOSHI 7 DA MASU DIGIRIN READER 16 SUN YI NASARA

Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBBUL), Lapai ta sanar da karin girma ga malamai bakwai zuwa matsayin Farfesa da kuma malamai goma sha shida zuwa matsayin Reader (Associate Professor).

Sanarwar ta fito ne a yayin taron Majalisar Tattaunawa (Senate) karo na 100, wanda aka gudanar a zauren majalisar da ke babban harabar jami’ar da ke Lapai. Shugaban Jami’ar, Farfesa Mohammed Hadi Sulaiman, ya bayyana cewa Majalisar Gudanarwar Jami’ar (Governing Council) ta amince da karin girman ne tun a taron ta karo na 60 da aka yi a ranar Talata, 27 ga Mayu, 2025.

Wadanda Aka Ƙara Wa Matsayin Farfesa:
• Dr. Shuaibu Ndagi Sayedi – Farfesa a fannin Kasuwanci da Kudi
• Dr. Adebiyi Alini Adelakun – Farfesa a Ilimin Nesa da Na Kan Layi (e-Learning)
• Dr. Mohammed Ibrahim Baji – Farfesa a fannin Ilimin Ƙwaƙwalwa (Educational Psychology)
• Dr. Aliyu Mohammed – Farfesa a fannin Ilimin Lafiya (Bangaren Hankali da Zamantakewa)
• Dr. Olajide Muili Folaranmi – Farfesa a fannin Ilimin Manya da Na Ba daɗe ba
• Dr. Mathew Tersoo Tsepav – Farfesa a fannin Geo-Physics (Na Aiki)
• Dr. James Obilikwu – Farfesa a fannin Tattalin Arzikin Kudi

Wadanda Aka Ƙara Wa Matsayin Reader (Associate Professor):
• Dr. Muktar Bala – Ilimin Lafiya da Tattalin Arziki
• Dr. Hussaini Mohammed Majiya – Kwayoyin Cututtuka da Kimiyyar Halittu (Public Health Microbiology & Biotechnology)
• Dr. Adisa Mohammed Jimoh – Kimiyyar Kayayyakin Halitta
• Dr. Nmadu Timothy – Gudanar da Ma’aikata (Human Resource Management)
• Dr. Muhammed Habiba Maikudi – Ilimin Daskararrun Tsirrai (Mycology)
• Dr. Mohammed Jiya Lakan – Ilimin Taimakon Al’umma da Ci Gaban Ƙauyuka
• Dr. Suleiman Yusuf Bagerei – Kimiyyar Abinci
• Dr. Ibrahim Suleiman Kuta – Kimiyyar Radiation da Nukiliya
• Dr. Amuzat Aliyu – Kimiyyar Abinci da Magungunan Tsirrai
• Dr. Musa Emanuel Umaru – Criminology da Tsaron Jama’a
• Dr. Aishat Rabiu Sani – Kwayoyin Bakteriya (Medical Microbiology)
• Dr. Yahaya Say Yadi Mohammed – Injiniyan Muhalli
• Dr. Ndanusa Babakatcha – Injiniyan Watsa Sadarwa
• Dr. Usman Naji Gimba – Kwayoyin Cututtuka na Jama’a
• Dr. Mohammed Isah Legbo – Kwayoyin Cututtuka na Magunguna
• Dr. Musa Usman – Gudanarwar Kananan Hukumomi

A cikin saƙon taya murna da ya fitar, Shugaban Jami’ar, Farfesa Sulaiman, ya yaba da irin namijin kokarin malamai da aka kara wa girma, yana mai jaddada musu bukatar ci gaba da gudanar da ayyukansu da kwazo, musamman a fannonin koyarwa da bincike.

Ya kuma isar da sakon taya murna daga Mai Ziyarar Jami’ar (Visitor), Mai Girma Gwamnan Jihar Neja, Alhaji Muhammad Umaru Bago, da kuma Kwamishinan Harkokin Ilimi na Manyan Makarantu, Hon. Abdullahi Adamu Mammagi, inda s**a bukaci malamai su kara himma da sadaukarwa wajen inganta ilimi da ci gaban al’umma baki daya.

Jam’iyyar PDP ta sake fuskantar babban koma baya a ranar Laraba yayin da mambobi uku na Majalisar Wakilai s**a sauya she...
23/07/2025

Jam’iyyar PDP ta sake fuskantar babban koma baya a ranar Laraba yayin da mambobi uku na Majalisar Wakilai s**a sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki. Wadanda s**a fice sun hada da Taofeek Ajilesoro da Omirin Emmanuel Olusanya daga Jihar Osun, da kuma Marcus Onobun daga Edo.

Wasikun sauya shekar su da Shugaban Majalisar, Hon. Tajudeen Abbas, ya karanta a zaman majalisar, sun bayyana rikice-rikicen cikin gida da rashin daidaito a cikin PDP a matsayin dalilin ficewar su. Sakataren Tsare-Tsare na APC na kasa, Sanata Ajibola Bashiru, ya halarci zaman domin shaida sauya shekar.

Da yake mayar da martani, Jagoran ƴan adawa a Majalisar, Kingsley Chinda, ya bukaci Kakakin Majalisar da ya ayyana kujerun wadanda s**a sauya sheka a matsayin babu kowa, bisa ga tanadin kundin tsarin mulki. Wannan mataki ya ƙara raunana matsayin jam’iyyar adawa a majalisar wakilai, yayin da ake kallon yadda zata fuskanci zaben 2027.

Gwamnan Jihar Bauchi kuma Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP, Sanata Bala Mohammed, ya bayyana sauya sheka daga jam’iyyar P...
23/07/2025

Gwamnan Jihar Bauchi kuma Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP, Sanata Bala Mohammed, ya bayyana sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa African Democratic Congress (ADC) da wasu manyan ‘yan siyasa s**a yi a matsayin kuskuren siyasa da kuma abin da ya sabawa ka’ida. A wani taron tuntuba na tsofaffin shugabanni da masu ruwa da tsaki na PDP da aka gudanar a Abuja, Gwamna Bala ya gargadi masu sauya sheka cewa ba za su iya zama ‘yan jam’iyyu biyu a lokaci guda ba.

A gaban manyan jiga-jigai da s**a hada da tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, wadanda s**a shiga sabuwar hadakar jam’iyyun adawa, Gwamna Bala ya ce sauya sheka zuwa jam’iyya da ba ta da tushe a kasa ba wata ruɗaniyar dabara ce. “Yanzu kuna barin jam’iyya mai tarihi da ginin tsari, wadda ke da gwamnoni da ‘yan majalisa da ofisoshi a duk faɗin ƙasa, kuna komawa jam’iyya da ba ta da tushe. Wannan ba hikima ba ce,” in ji shi.

Duk da wannan s**a, Gwamnan ya nuna mutunci ga wadanda s**a fice, yana rokon su su dawo gida. “Wannan ita ce jam’iyyar da ta gina su — wasu sun zama gwamnoni, ‘yan majalisa, wasu sun sami tikitin takara. Idan kuna da buri, kada ku rusa gadar da ta hayar da ku zuwa nan,” in ji Bala. Ya jaddada cewa siyasa tana bukatar tsari da gaskiya, yana mai cewa: “Ba za ka iya zama a PDP kana tare da ADC ba. Ka zaɓi inda kake. Jam’iyya daya kawai. Hadaka da jam’iyyar waje ba za ta haifar da da mai ido ba.”

Wani Matashi Ya Gyara Rijiyar Burtsatse Domin Ya Zama Sadakatul Jariya Ga Marigayi BuhariWani haziƙin matashi ɗan asalin...
23/07/2025

Wani Matashi Ya Gyara Rijiyar Burtsatse Domin Ya Zama Sadakatul Jariya Ga Marigayi Buhari

Wani haziƙin matashi ɗan asalin jihar Adamawa, wanda yake zaune a garin Uɓa mai suna Luqman Suleiman ya gyara wata rijiyar burtsatse da ta lalace na tsawon lokaci a matsayin sadakatul jariya ga marigayi tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, da fatan Allah yajikans kuma ya kai ladan zuwa kabarinsa.

Wace fata za ku yi masa?


WTV

Address

Second Gate
Suleja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ZRN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share