ZRN Hausa

ZRN Hausa Zuma Reporters Network: Tushen sahihan labarai ne na cikin gida, binciken gaskiya, da tattaunawar jama’a da ke kawo sauyi.

~ Muryar Gaskiya.

24/02/2026

Cikakken rahoto kan rabon kayan tallafi da Gidauniyar Adolescent and Women Empowerment Foundation (AWEF) ta bayar a Garin Sabon Wuse dake Jahar Neja.
👇👇👇👇👇👇👇👇👇

10/01/2026
An gano wani makami mai linzami a yankin Zugurma da ke Karamar Hukumar Mashegu a Jihar Niger.Rahotanni sun bayyana wasu ...
06/01/2026

An gano wani makami mai linzami a yankin Zugurma da ke Karamar Hukumar Mashegu a Jihar Niger.

Rahotanni sun bayyana wasu mazauna yankin ne s**a gano makamin, inda daga bisani s**a sanar da jami’an tsaro domin daukar matakin da ya dace.

Wata majiya ta bayyana cewa ana zargin makamin kanwar wani makami mai linzami ne na Tomahawk, wanda ake kyautata zaton yana daga cikin mak**an da Amurka ta harba a baya.

Da aka tuntube shi, kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Niger, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da gano makamin ga wakilinmu.

Ya ce tuni jami’an tsaro s**a fara gudanar da bincike kan lamarin.

A cewarsa, “A ranar 5 ga Janairu, 2026, da misalin karfe 2 na rana, mun samu rahoto daga yankin Zugurma na Karamar Hukumar Mashegu cewa wasu mazauna yankin sun hangi wani abu da ake zargin makami mai linzami ne a cikin daji.

’Yan sandan da ke aiki a karkashin sashen Ibbi Div sun garzaya wurin, s**a killace tare da tabbatar da tsaron makamin, yayin da aka tura sashen EOD-CBRN na rundunar domin bincike, tantancewa da kwashe makamin.

Ana ci gaba da bincike kan lamarin, kuma za a sanar da jama’a duk wani sabon bayani da aka samu.”

Majiyar labari: Daily Trust

Sanatan Ogun ta Yamma kuma Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Kasafin Kuɗi, Sanata Solomon Adeola, ya ce cire talla...
04/01/2026

Sanatan Ogun ta Yamma kuma Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Kasafin Kuɗi, Sanata Solomon Adeola, ya ce cire tallafin mai da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi na samarwa Najeriya sama da tiriliyan ₦10 a duk shekara. Ya bayyana hakan ne a yayin bikin godiya na sabuwar shekara da aka gudanar a Ilaro, ƙaramar hukumar Yewa ta Kudu a jihar Ogun.

Adeola ya ce kafin cire tallafin, gwamnati na kashe biliyoyin naira duk wata wajen tallafin mai, lamarin da ke tara asara mai yawa a shekara. Ya ƙara da cewa Majalisar Tarayya da fadar gwamnati suna aiki tare kan sabbin dokokin haraji, inda ya musanta jita-jitar yin gyara a bayan fage, yana mai cewa abin da aka amince da shi ne za a aiwatar.

Sanatan ya bayyana cewa tattalin arzikin ƙasa na samun daidaito, tare da ci gaba a ƙananan harkokin kasuwanci da kuma ƙoƙarin inganta babban tattalin arziki. Ya yabawa Shugaba Tinubu kan manyan ayyukan more rayuwa k**ar titin Lagos–Calabar da Sokoto–Badagry, yana mai cewa za su ƙarfafa tattalin arzikin ƙasa.

Haka kuma, Ministan Ƙananan Ayyukan Lafiya, Dakta Ishiaq Salako, ya ce manufofin Tinubu na haifar da sauyi mai kyau, inda babu dogayen layukan mai a bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara. Ya ƙara da cewa ana sa ran tattalin arzikin ƙasa zai bunƙasa, yayin da hauhawar farashi ke raguwa. Salako ya yi kira ga ’yan Najeriya da su mara wa gwamnati baya domin ci gaba da gina ƙasa mai wadata.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya ce zuba jari a fannin ilimi muhimmiyar kudirin gwamnati ne domin tabbatar ...
04/01/2026

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya ce zuba jari a fannin ilimi muhimmiyar kudirin gwamnati ne domin tabbatar da kyakkyawan makomar Najeriya. Ya bayyana ilimi a matsayin muhimmin ginshiƙi na ci gaba, ƙarfafa tattalin arziki da ‘yantar da al’umma, yana mai cewa ba a taɓa yin asara da zuba jari a ilimi ba; tsari ne na gina makoma mai tsaro.

Shettima ya faɗi hakan ne a bikin yaye ɗalibai na Jami’ar Kashim Ibrahim a Borno, inda ɗalibai 2,294 s**a kammala karatu daga zangon 2022/2023 zuwa 2024/2025. Ya tuna da illar da Borno ta sha sak**akon katsewar ilimi saboda rikicin tsaro, amma ya yaba da juriya da jajircewar al’ummar jihar.

Ya shawarci waɗanda s**a kammala karatu da su kasance jakadun gaskiya, hidima da ƙwarewa, yana mai gargadin kauce wa lalacewar ɗabi’a, domin halayyarsu ce za ta ƙayyade martabar jami’ar a nan gaba.

28/12/2025

Faduwar farashin amfanin Gona a bana ya tilastawa wasu manoma a yankin Taraba barin amfanin gonansu a Daji, inda s**a hakura da gonakin ba tare da yin girbi ba .

Shin meye ra'ayinku kan hakan ?

ZRN Hausa

25/12/2025

Karshen shekara: Babban Daraktan Hukumar Kula da Tsaron Halittu ta Ƙasa, Barr. Bello Bawa Bwari ya raba tallafin shinkafa a ƙananan hukumomin Gabashin Jahar Neja.

Ga cikakken rahoton
👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾

18/11/2025

Mayakan ISWAP sun k**a Brigadier General M. Uba daga bisani s**a harbe shi a bidiyo — lamarin da ya kasance karo na farko da ’yan ta’adda s**a yi garkuwa da Janar mai aiki sannan s**a kashe shi a haka.

Wannan al’amari ya tayar da hankula a fadin ƙasa, tare da kira ga ƙarfafa leƙen asiri, inganta dabarun yaki, da kuma ƙara kariya ga sojojin da ke fagen fama.

04/11/2025

Kaakakin Majalissar Jahar Niger, Barr. Abdulmalik Sarkin Daji ya gwangwaje zaɓaɓɓen shugaban ƙaramar hukuma da mataimakiyarsa da motocin Alfarma………
👇🏾👇🏾👇🏾

04/11/2025

Kakakin Majalisar Jahar Niger, Barr. Abdulmalik Sarkin Daji ya gwangwaje zaɓaɓɓen shugaban karamar hukuma da mataimakiyarsa da motoci na Alfarma don gujewa sa ido ga dukiyar Al’umma.

Address

Second Gate
Suleja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ZRN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share