Suleja Media Watch

Suleja Media Watch Suleja News Update

HOTUNA: YADDA ALMAJIRAN SAYYID IBRAHEEM ZAKZAKY (H) A CHIMBI KORO S**A GUDANAR DA MUZAHARAR MAULUDIDaga Aliyu Basiru Chi...
26/08/2026

HOTUNA: YADDA ALMAJIRAN SAYYID IBRAHEEM ZAKZAKY (H) A CHIMBI KORO S**A GUDANAR DA MUZAHARAR MAULUDI

Daga Aliyu Basiru Chimbi

yadda ’yan uwa Musulmi Almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) na garin Chimbi Koro, da ke ƙaramar hukumar Paikoro a Jihar Neja, s**a gudanar da Muzaharar Mauludin fiyayyen halitta, Annabi Muhammad (S.A.W.W), tare da sauran al’ummar garin Chimbi da kewaye.

Muzaharar ta samu halartar ɗimbin al’umma da s**a haɗa da daliban makarantun Islamiyoyi, Zakirai, da ’yan kabilun Fulani da Gwari, waɗanda s**a fito daga kauyuka daban daban, domin nuna farin ciki da murnar zagayowar ranar haihuwar Manzon Allah (S.A.W.W).

An gudanar da muzaharar ne a yau Laraba, 13 ga Rabi’ul Awwal, 1448H, wanda ya yi daidai da 26 ga Agusta, 2026.

- Suleja Media watch

INNĀ LILLĀHI WA INNĀ ILAYHI RĀJI’ŪNWASU DAGA CIKIN ’YAN UWA NA GARIN IWA SUN YI HADARI A HANYAR ZUWA SULEJA DOMIN MUZAHA...
25/08/2026

INNĀ LILLĀHI WA INNĀ ILAYHI RĀJI’ŪN

WASU DAGA CIKIN ’YAN UWA NA GARIN IWA SUN YI HADARI A HANYAR ZUWA SULEJA DOMIN MUZAHARAR MAULUDI

Wata motar ’yan uwa Almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) daga garin Iwa ta yi hatsari a hanyarsu ta zuwa Muzaharar Mauludi da aka gudanar yau a garin Suleja.

Rahotanni sun bayyana cewa, hatsarin ya yi sanadiyyar rasuwar mutum ɗaya daga cikin ’yan uwan, mai suna Ammar Sani.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya karɓi uzurinsa, Ya gafarta masa kurakuransa, Ya jiƙansa da rahama, Ya sanya Aljannar Firdausi ce makomarsa, sannan Ya bai wa sauran waɗanda abin ya shafa lafiya da sauƙi.

Muna kuma miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalan marigayin da ’yan uwa baki ɗaya bisa wannan babban rashi.

Innā lillāhi wa innā ilaihi rāji’ūn.

Hoton dake kasa ba na hadarin bane
— Suleja Media Watch
12 Rabi’ul Awwal 1448H
25th August 2026

DAGA GARIN SULEJA: ’YAN UWA ALMAJIRAN SAYYID IBRAHIM YAQUB ZAKZAKY (H) NA DA’IRAR SULEJA DA KEWAYA SUN GABATAR DA MUZAHA...
25/08/2026

DAGA GARIN SULEJA: ’YAN UWA ALMAJIRAN SAYYID IBRAHIM YAQUB ZAKZAKY (H) NA DA’IRAR SULEJA DA KEWAYA SUN GABATAR DA MUZAHARAR MAULUD

— Müsty M ßôy

A yau Talata, da misalin ƙarfe 10:00am, ’yan uwa Almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) na da’irar Suleja da kewaye, s**a gabatar da Muzaharar Maulidin Manzon Allah (S.A.W.W), domin nuna farin ciki da wannan rana ta haihuwar fiyayyen halitta, Annabi Muhammad (S.A.W.W).

A yayin da dubban ’yan uwa Musulmi Almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) s**a halarci muzaharar, ta cigaba da tafiya cikin lumana, a yayin da ake tafiya ana rerawaƙokin murna da bege ga fiyayyen halitta, Manzon Allah (S.A.W.W). An dauki dogon lokaci ana tafiya, sai daga ƙarshe aka zo inda za a kammala muzaharar, sai aka bude da addu’a, aka gabatar da jawabi. Daga ƙarshe aka rufe, aka sallami ’yan uwa.

25/08/2026
12/Rabi’ul Awwal, 1448H



AL’UMMAR MUSULMI A LAMBATA SUN GUDANAR DA GAGARUMIN MUZAHARAR MURNAR HAIHUWAR MANZON ALLAH (S.A.W.W)Daga Aliyu Abdullah ...
25/08/2026

AL’UMMAR MUSULMI A LAMBATA SUN GUDANAR DA GAGARUMIN MUZAHARAR MURNAR HAIHUWAR MANZON ALLAH (S.A.W.W)

Daga Aliyu Abdullah Lambata

A Safiyar yau Talata, 25 ga Agusta, 2026, wanda ya yi daidai da 12 ga Rabi’ul Awwal, 1448H, Almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) da sauran al’ummar Musulmi maza da mata, yara da manya, a garin Lambata da ke Jihar Neja, sun gudanar da gagarumin taron gangami da tattaki domin murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta, Annabi Muhammad (S.A.W.W).

Taron ya samu halartar ɗimbin al’ummar Musulmi daga garin Lambata da kewaye, inda mahalarta s**a gudanar da Muzaharar a cikin garin, s**a ratsa lungu da saƙo cikin yanayi na farin ciki da murna, domin nuna ƙauna da girmamawa ga Manzon Allah (S.A.W.W).

Mahalarta Muzaharar sun haɗa da yara da manya, maza da mata, tare da sauran al’ummar Musulmi, inda jama’a s**a fito domin nuna farin cikinsu da zagayowar wannan rana mai albarka ta Mauludi.

An fara Muzaharar ne daga filin Primary School na garin Lambata, inda mahalarta s**a taru kafin fara zagayen. Daga nan ne s**a bi wasu sassa daban-daban na garin Lambata.
Bayan kammala zagayen, mahalarta sun koma Babban Masallacin Juma'a na garin da ke cikin Gawu Baban Gida, inda aka gudanar da addu’o’i tare da sallamar mahalarta.

Kafin gudanar da addu’ar rufe wa , wakilin ’yan uwa musulmi Almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (h) na garin Lambata, Malam Adamu Ahmad, ya gabatar da jawabi inda ya bayyana muhimmancin fitowar al’ummar Musulmi domin murnar zagayowar ranar haihuwar Manzon Allah (S.A.W.W).

Malam Adamu Ahmad ya ƙara yin kira ga al’umma da su ci gaba da nuna ƙauna da girmamawa ga Manzon Allah (S.A.W.W), yana mai bayyana ranar Mauludi a matsayin rana mai albarka da farin ciki ga al’ummar Musulmi baki ɗaya.

Ya kuma jaddada muhimmancin tunawa da rayuwa da koyarwar Manzon Allah (S.A.W.W), tare da ƙarfafa al’umma kan haɗin kai, zaman lafiya da bin kyawawan ɗabi’un da Manzon Allah (S.A.W.W) ya koyar.

Daga bisani, an gudanar da addu’a ga al’ummar Musulmi da ƙasa baki ɗaya, sannan aka sallami mahalarta cikin ƙoshin lafiya da kwanciyar hankali.

— Suleja Media Watch

12 Rabi’ul Awwal, 1448H
25 ga Agusta, 2026

MUZAHARAR MAULUDIN MANZON ALLAH (S.A.W.W) A SULEJA TA KAYATAR- Daga Idris Muhammad Katusha A safiyar yau Talata, 25 ga A...
25/08/2026

MUZAHARAR MAULUDIN MANZON ALLAH (S.A.W.W) A SULEJA TA KAYATAR

- Daga Idris Muhammad Katusha

A safiyar yau Talata, 25 ga Agusta, 2026, wanda ya yi daidai da 12 ga Rabi’ul Awwal, 1448H, da misalin karfe 11:00am na safe al’ummar Musulmi s**a gudanar da gagarumar Muzaharar Maulidin Manzon Allah (S.A.W.W) a garin Suleja, domin nuna farin ciki da murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta, Annabi Muhammad (S.A.W.W).

Muzaharar ta samu halartar ɗimbin al’ummar Musulmi, ciki har da Almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) da mabiya ɗariku daban-daban, waɗanda s**a fito daga sassa daban-daban na garin Suleja da ƙananan garuruwan da ke kewaye da ita, ciki har da wasu daga yankin Abuja.

An fara muzaharar ne daga Auwal Ibrahim Primary School da ke Suleja, inda mahalarta s**a taru domin fara tattakin. Daga nan ne aka ɗauki hanyar da aka saba bi wajen gudanar da wannan muzahara a kowace shekara, yayin da ɗumbin mahalarta ke tafiya cikin tsari da haɗin kai.

A yayin muzaharar, an rika gudanar da waƙoƙin yabo da girmama Manzon Allah (S.A.W.W), tare da ɗaga taken “Labbaika Ya Rasulallah”, wanda ke bayyana ƙauna, girmamawa da amsa kiran Manzon Allah (S.A.W.W). Mahalarta sun kuma bayyana farin cikinsu da zagayowar wannan rana mai albarka ta Mauludi.

Muzaharar ta kasance wata dama da al’ummar Musulmi ke amfani da ita wajen tunawa da rayuwar Manzon Allah (S.A.W.W), koyarwarsa, kyawawan halayensa da kuma muhimmiyar rawar da ya taka wajen isar da saƙon Musulunci ga bil’adama.

Haka kuma, muzaharar ta kasance wata dama ta ƙarfafa haɗin kai da zumunci tsakanin al’ummar Musulmi, inda Musulmi daga ɓangarori daban-daban, ciki har da ’yan Shi’a da mabiya ɗariku na Sunnah, maza da mata da matasa, tare da mutane daga kabilu daban-daban, s**a fito domin gudanar da bikin Mauludi cikin kwanciyar hankali.

Wannan gagarumar muzahara ta sake bayyana irin muhimmancin da al’ummar Musulmi ke bai wa ranar haihuwar Manzon Allah (S.A.W.W), tare da jaddada ƙauna da girmamawa gare shi da kuma buƙatar bin koyarwarsa a rayuwar yau da kullum.

— Suleja Media Watch

12 Rabi’ul Awwal, 1448H
25 ga Agusta, 2026


YADDA AKA GUDANAR DA MUZAHARAR MAULUDI A BABBAN BIRNIN TARAYYAR NAJERIYA ABUJA- Daga Bilyaminu Ɗan JaridaDa misalin ƙarf...
25/08/2026

YADDA AKA GUDANAR DA MUZAHARAR MAULUDI A BABBAN BIRNIN TARAYYAR NAJERIYA ABUJA

- Daga Bilyaminu Ɗan Jarida

Da misalin ƙarfe 10:00 na safiyar yau Talata, 25 ga Agusta, 2026, wanda ya yi daidai da 12 ga Rabi’ul Awwal, 1448H, al’ummar Musulmi s**a gudanar da gagarumar Muzaharar Maulidin Manzon Allah (S) a babban birnin tarayyar Najeriya, Abuja, domin nuna farin ciki da murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta, Annabi Muhammad (S).

Muzaharar ta samu halartar ɗimbin al’ummar Musulmi Almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (h) da Mabiya Dariku daga sassa daban-daban na Abuja da kewaye, inda mahalarta s**a fito cikin yanayi na farin ciki da annashuwa, suna ɗauke da tutoci da alluna masu ɗauke da saƙonnin girmamawa da ƙauna ga Manzon Allah (S).

An fara Muzaharar ne daga Mabushi Junction, Abuja, inda mahalarta s**a taru kafin fara tafiyar. Daga nan ne muzaharar ta ɗauki hanyar da aka tsara, tare da mahalarta suna tafiya cikin tsari da haɗin kai, suna bayyana ƙaunarsu ga Annabi Muhammad (S) da kuma jaddada muhimmancin koyarwarsa ga al’ummar Musulmi.

A yayin muzaharar, an rika gudanar da kiraye-kirayen yabo da girmama Manzon Allah (S), tare da ɗaga taken “Labbaika Ya Rasulallah”, wanda ke nuna amsa da biyayya ga kiran Manzon Allah (S). Mahalarta sun kuma bayyana farin cikinsu da wannan rana mai girma ta Mauludi.

Muzaharar ta kasance wata dama da al’ummar Musulmi s**a yi amfani da ita wajen tunawa da rayuwar Manzon Allah (S), koyarwarsa, halayensa na gari da kuma irin muhimmiyar rawar da ya taka wajen isar da saƙon Musulunci ga al’umma.

Haka kuma, taron ya kasance na haɗa kan al’ummar Musulmi Shi'a da Sunnah, inda maza da mata da Matasa, kabilu ma banbanta s**a fito domin gudanar da bukin Mauludi cikin kwanciyar hankali da lumana.

Bayan shafe sa’o’i ana gudanar da muzaharar a cikin babban birnin tarayya, an kawo ƙarshenta ne da misalin ƙarfe 4:00 na yammacin yau, a Tsohon Filin Fareti na Ƙasa da ke Abuja, inda mahalarta s**a kammala Muzaharar cikin tsari.

An gudanar da muzaharar ne a daidai lokacin da Musulmi a sassa daban-daban na duniya ke bikin zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad (S), tare da nuna ƙauna da girmamawa gare shi da kuma tunatar da al’umma muhimmancin bin koyarwarsa.

Mahalarta sun bayyana farin cikinsu da samun damar gudanar da wannan gagarumar muzahara a babban birnin tarayyar Najeriya, inda s**a yi addu’ar Allah Ya ƙara haɗa kan al’ummar Musulmi, Ya sanya koyarwar Manzon Allah (S) ta zama jagora ga rayuwarsu, Ya kuma dawo da wannan rana cikin aminci da albarka.
- Suleja Media watch
12 Rabi’ul Awwal, 1448H
25 ga Agusta, 2026

25/08/2026

Kaitsaye daga Suleja

GOBE MUZAHARAR ZAGAYEN MAULUDIN MANZON ALLAH (S.A.W.W) A GARIN SULEJAƳan uwa Musulmi, Almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky ...
24/08/2026

GOBE MUZAHARAR ZAGAYEN MAULUDIN MANZON ALLAH (S.A.W.W) A GARIN SULEJA

Ƴan uwa Musulmi, Almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H), na gayyatar ɗaukacin al’umma Masoya Manzon Allah (s.a.w.w), zuwa gagarumar Muzaharar Zagayen Mauludin Manzon Allah (S.A.W.W).

Rana: Talata, 12 ga Rabi’ul Auwal, 1448H
Daidai da: 25 ga Agusta, 2026
Wurin farawa: Auwal Ibraheem Primary School, Suleja
Lokaci: Ƙarfe 10:00 na safe

Muna kira ga ɗaukacin al’umma da su halarta domin nuna farin ciki da ƙauna ga fiyayyen halitta, Annabi Muhammad (S.A.W.W).

- Suleja Media Watch
11 Rabi'ul Auwal 1448H
24th August 2026

21/08/2026

Kamar kowanne mako yau ma yan uwa musulmi Almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (h) na suleja sun gudanar Wa'azzin bayan Idar da Sallar Juma'a (Pre-Khudba)
Wanda Malam Umar Abdullahi Saqafa ya gabatar a masallacin fada dake garin Suleja.
21st August 2026

YANDA AKA GUDANAR DA TARON TUNAWA DA WAƘI’AR BUHARI (LA’ANATULLAH) A SULEJA- Daga: Al-Haqiqy A yau, Asabar, 15 ga Agusta...
15/08/2026

YANDA AKA GUDANAR DA TARON TUNAWA DA WAƘI’AR BUHARI (LA’ANATULLAH) A SULEJA

- Daga: Al-Haqiqy

A yau, Asabar, 15 ga Agusta 2026, an gudanar da taron tunawa da waƙi’ar Buhari (La’anatullah) a garin Suleja, Jihar Neja, a harabar Makarantar Ameerul Muminin (A.S).

Taron ya samu halartar ɗimbin al’umma, musamman mabiya da masoyan Ahlul Baiti (A.S) Almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (h), inda aka gudanar da jawabai da kuma tunatarwa kan abubuwan da s**a shafi waƙi’ar da kuma darussan da ya kamata al’umma su ɗauka daga irin waɗannan abubuwa.

Masu gabatar da jawabai sun bayyana muhimmancin tunawa da tarihi da kuma kiyaye koyarwar Ahlul Baiti (A.S), tare da yin kira ga mahalarta da su kasance masu tsayawa kan gaskiya da adalci ko da kuwa za'a rasa rai.

An kuma yi addu’o’i ga shahidan da s**ayi shahahada a wannan waƙi’a, tare da fatan Allah Ya ɗaukaka darajarsu, sannan Ya ba wa iyalansu da sauran al’umma haƙurin jure rashinsu, kuma ya Kara tsinuwa ga Azzalumain da s**a ka*&hesu.

- Suleja Media Watch

Address

Suleja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Suleja Media Watch posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share