ALMIZAN TV Hausa

ALMIZAN TV Hausa Jarida don Karuwar Al'umma

Kotun Daukaka Kara dake zamanta a Owerri ta Yanke Hukunci Cewa A Biya wani Bawan Allah mai suna Dr. Emmanuel Ugochukwu S...
28/07/2025

Kotun Daukaka Kara dake zamanta a Owerri ta Yanke Hukunci Cewa A Biya wani Bawan Allah mai suna Dr. Emmanuel Ugochukwu Shebbs Naira Million Goma (N10,000,000) Akan cin zarafinsa da Hukuma Federal Road Safety Corps Sukayi da keta mishi datayi na hakkinsa na dan Adam.

Abun ya faru ne tun 2020, Lokacin da jami’an Road safety s**a tsaida shi s**a kwace mishi Driving licience nashi da takardun motanshi! Sai ya kai karansu zuwa High Court, High court ta yanke Hukuncin cewa Abiyashi Naira Mllion 30
Anma kotun Daukaka kara ta rage kudin zuwa Million 10

Kotu Daukaka karan ta Ayyaba cewa Hukumar Road Safety ba ta Ikon Rike Driving license ko Takardun motan mutum ko rike motan mutum muddin ba kotu zata kaishi ba!

Gani ga wane ya ishe wane tsoron Allah.

Daga shafin: Barrista Hamza Nuhu Ɗantani.

An Yi Taron Tunawa Da Shekaru 11 Da Kisan Gillar Da Aka Yi Wa ‘Yan Shi’a 34 A ZariyaDaga Wakilinmu A wani taro mai cike ...
28/07/2025

An Yi Taron Tunawa Da Shekaru 11 Da Kisan Gillar Da Aka Yi Wa ‘Yan Shi’a 34 A Zariya

Daga Wakilinmu

A wani taro mai cike da alhini da juyayi da aka gudanar a ranar Juma’a, 25 ga watan Yuli, 2025 a muhallin Jannatu Darur Rahma dake Dembo a Zariya, Harkar Musulunci a ƙarƙashin jagorancin Shaikh Ibraheem Zakzaky ta gudanar da taron tunawa da cika shekaru 11 da kisan gillar da aka yi wa membobinta 34 a Zariya a yayin wani zanga-zangar lumana ta ranar Qudus a shekarar 2014.

Taron ya kasance cike da jimami da alhini tare da karramawa ga waɗanda s**a rasa rayukansu, kazalika an sake jaddada kiran neman adalci.

Sannan, Harkar Musuluncin ta bayyana goyon bayanta na dindindin ga al’ummar Falasɗinu da ake zalunta, tana mai cewa ƙudurinta na tsaya musu tsayin daka bai sauya ba, kuma ba zai taɓa gushewa ba.

A yayin ganawarsa da manema labarai a yayin taron, Sayyid Badamasi Yaqoub, ɗan uwa ga jagoran Harkar Musulunci, ya jaddada cewa; “Wannan gwagwarmaya da muke yi ta neman adalci, dama ta gaji kule daga mahukunta; “Dama ita wannan hanya, ita ke nan ba ta da canji. Hanya ce ta kira zuwa ga addinin Allah, tabbas akwai mutuwa a cikinta.”

Ya ci gaba da cewa; “Wannan abin da Annabawa s**a sha gwagwarmaya a kai ke nan. Saboda haka da zarar ka ce Allah da ma’anarsa, to za ka haɗu da fushin waɗanda ba su yarda da wannan ba. Suna ganin su mulkinsu kake ƙalubalanta, saboda haka lallai ba za su barka ba”, in ji shi.

Sai dai ya ce waɗanda aka kashe ba su yi laifin komai ba, illa kawai; “sun ce Ubangijinsu Allah ne, ba su yarda da zalunci ba, s**a tsaya a kai”.

Dangane da matakin da za su ɗauka kuwa, Shaikh Badamasi ya tabbatar da cewa su dai za su ci gaba da gwagwarmayarsu, kuma da wannan gwagwarmayar ne ƙarshen zalunci zai zo, kamar yadda ya ce; “Da wannan gwagwarmayar ne ƙarshen zalunci zai zo. Ta wannan yunkurin da suke yi na kisa, ta wannan hanyar ce ƙarshen su zai zo”.

Ya jaddada cewa suna alfahari da waɗanda aka kashe, kuma ba za su taɓa mantawa da su ba. Inda ya jaddada aniyar cewa, wannan ba zai sanyaya musu guiwa ba, za su ci gaba da kasancewa da al’ummar Falasdinu; “Waɗannan yara an shahadantar da su ne a kan Qudus. Yanzu al’ummar Musulmi su dubi abin da yake faruwa a Gaza. Yanzu mutum ba zai iya kallon abin da yake faruwa a Gaza ba, duk magoya bayansu a kewaye da su, duk ƙasashen Musulmi ne. Ita kanta Isra’ila an kafa ta a ƙasar Musulmi ne, Masar Musulmi ne, amma kuma sun kewaye sun hana a shiga da abinci, Jordan Musulmi ne, sun kewaye sun hana abinci; kullum ana mutuwa da yunwa, ba abinci, ba ruwa, ba komai. Suna bin goyon bayan waɗannan azzaluman mahukunta”.

Ya ƙara da cewa; “Wannan zaluncin da ake yi wa ‘yan’uwanmu a Gaza, muna nan tare da su, kuma Wallahi Summa Tallahi, da za mu samu dama, za mu je Gaza mu bayar da jininmu a kan su”, ya jaddada.

Malam Ibrahim Abubakar, ɗaya daga cikin masu shirya wannan taron, ya tabbatar da cewa suna tuna wannan kisan gilla a duk ranar 25 ga watan Yulin kowacce shekara; “A wannan rana ta 2014 sojojin Nijeriya s**a kashe mana mutum 34, s**a raunata aƙalla 80; masu ƙaramin’ da manyan raunuka. Duk a irin wannan rana idan ta zagayo duk shekara muna haɗuwa a wannan muhallin mu yi musu addu’o’i da saukar Alƙur’ani. Sannan mu yi taruka da jawabai na tuna su”.

Ya ce duk wanda ya tsayawa gaskiya zai fuskaci irin wannan. Ya ce a duk inda kake dole a ci gaba da neman haƙƙin al’ummar Falasdinu.

Tunda farko an soma taron da addu’o’i da karatun Alƙur’ani mai girma, tare da gabatar da fareti da kuma jawabai daga Malamai.

Maryam Ɗalhatu, ɗaya ce daga cikin ‘yan’uwan waɗanda aka kashe a wannan rana, ta ce; ta yi farin ciki cewa ana tunawa da su a kowacce shekara, sai dai har yanzu tana kukan rashin su.

Sai dai ta ce; “Saƙona ga azzalumai shi ne, wannan hanyar da s**a ɗauka ta kashe mutane, ba hanya ce mai ɓullowa ba, su sani cewa wannan abin da suke yi ba zai kai su ga ko’ina ba sai asara, tun daga duniya har lahira”, in ji ta.

Kazalika, Alƙasim Muhammad Gyallesu, ɗaya daga cikin waɗanda aka raunata a wannan rana, shekaru 11 da s**a gabata, amma har yanzu illar harbin da aka yi masa na ci gaba da nunawa.

“Ina cikin waɗanda sojoji s**a harba a lokacin. Ba mu ɗauke da komai a hannunmu a lokacin, illa iyaka kawai mun fito domin jajen mu da nuna goyon baya tare da Allah-wadai da zaluncin da ake yi wa al’ummar Falasdinu.

28/07/2025
27/07/2025

Iran ta yi gargaɗin cewa idan Amurka da Isra'ila s**a keta yarjejeniyar tsagaita wuta, za ta mai da masu martani mai gauni.

27/07/2025

Mayaƙan Yemen zuwa gwamnatocin Larabawa; "Ku buɗe mana kan iyakoki mu yi Tattaki zuwa Palastinu (ko kuma) za mu buɗe su da ƙarfi mu shiga."

International conference  Na waki'ar 25july Karo Na 11 A Abuja.Harkar Musulunci karkashin jagorancin Sayyid Ibraheem Yaq...
27/07/2025

International conference Na waki'ar 25july Karo Na 11 A Abuja.

Harkar Musulunci karkashin jagorancin Sayyid Ibraheem Yaqoub Zakzaky (H) ta gudanar da taron Tunawa da waki'ar 25july tasu Shahid Ahmad, Hameed, Mahmud, da sauran shahidai 31 karo na 11 a Abuja

Taron wanda ya samu halartar yan'uwa da al'ummar gari, wanda aka gabatar da jawabai da dama, akan maudu'eh mabanbanta, cikin masu jawabi hadda bakin da aka haska jawabansu daga ketaren kasa, sannan Malama Zeenah Ibrahim ta gabatar da jawabi

Taron ya gudana ne a wani babban dakin taro dake Birnin Tarayya Abuja

A GUDANAR DA  MUZAHARAR ASHURA A GARIN DAWAKIN KUDU DA KE KANO.Bayan shafe tsawon watan Muharram, a ranakun Litinin, Lar...
27/07/2025

A GUDANAR DA MUZAHARAR ASHURA A GARIN DAWAKIN KUDU DA KE KANO.

Bayan shafe tsawon watan Muharram, a ranakun Litinin, Laraba da Alhamis, na wannan shekara ta 1447, ana gabatar da zaman juyayin Waki'ar Ashura, a garin Dawakin kudu dake yankin Kura, da'irar Kano da kewaye, an gabatar da gagarumar muzaharar da ta samu wakilcin dukkan masoya gidan Manzon Allah daga lungu da sako na yankin.

Muzaharar da aka fara ta da misalin karfe 5:00 na yammacin ranar Asabar 1 ga watan Safar 1447 ( 26/07/2025), ta daga ne daga Muhallin makarantar Fudiyya Dawaki.

Daga nan sai mahalarta muzaharar, da s**a kunshi maza da mata, yara da manya, sanye da bakaken kaya, rike da bakaken tutoci, rubuce da kalmar 'labbaika ya Hussain', don bayyanar da juyayin kisan jikan Manzon Allah imamu Hussaini (AS), s**a gangara izuwa hanyar da ta nufi Kofar Arewa ta gaban Dawaki Unity Bank. Sai Unguwar Na'ibawa, izuwa kan kwana da kuma Galadanchi, ta biyo ta gaban gidan Hakimin Dawaki.

Muzaharar ta nausa izuwa Unguwar Maliki, sai Masaka da kuma Kofar kudu. Hakan nan muzaharar ta shiga Unguwar Dabino da kuma Rinji. Sai Unguwar Kuka, izuwa Kofar Gabas, inda ta biyo ta gaban asibitin Dawakin kudu General Hospital.

Misalin karfe shida da rabi, muzaharar ta iso wani katon fili, kafin ka karasa asibitin Sani tiyata (Dawaki Nursing Home), inda aka rufe ta.

A wajen rufe muzaharar, kafin jawabin wakilin yan'uwa na garin Dawaki, Malam Abubakar Takiyyu Dawaki tare da Malam Arma Kura, sun fadakar da yan'uwa akan daukar takalifin iyalan shahidai.

Malam Ibrahim Abdu D/kudu, wakilin yan'uwa almajiran Sayyeed Ibraheem Zakzaky (H) na garin Dawakin kudu, ya fara jawabin rufe muzaharar ne da godewa Allah (T) da ya tsawaita rayuwarmu har muka ga wannan rana ta gabatar da muzaharar Ashura ta Dawakin kudu, bayan share wata guda ana zaman juyayi.

Daga nan sai malamin ya labartawa mahalarta, hakikanin abin da ya faru a ranar Ashura, inda yace, 'babu shakka rundunar makiya Allah, mai dauke da dubban mayaka karkashin jagorancin Yazidu dan Mu'awiyya la'ananne sun zubda jinin jikan Manzon Allah ta hanyar yanke kansa mai albarka, da kuma kisan Iyalansa da Sahabbansa da basu wuce su saba'in da 'yan kai ba. Sannan yace, " Imamu Hussaini da wadanda suke tare dashi sun sadaukar da rayukansu ne domin ceto wannan addini ga barin shafewa daga doron kasa." Ya kara da cewa, "da ace Imamu Hussaini da wadanda ke tare dashi sunyi bai'a ga Yazidu, da wallahi sai dai mu ringa jin labarin anyi wani addini wai sunansa Musulunci", inji malamin.

Daga nan sai ya bayyana cewa duk wanda ke kiran kansa musulmi, wanda yai imani da Manzon Allah (S.A.W.A.), Imamu Hussaini yana da hakki a kansa na kokawa kan zaluncin da aka yiwa gidan Manzon Allah. " Don haka nema, idan irin wannan lokacin yazo, muke gabatar da tarurruka, da zamammaki, da muzaharori domin tunatar da al'umma da kawukanmu, irin abin da ya faru ga gidan Manzon Allah (S.A.W.A.)"

Bugu da kari, Malam Ibrahim Abdu yace, "a filin hamadar Karbala, imamu Hussaini (AS) yayi kira, inda cewa, 'Hal Min Nasirin Yansurna'? ( Shin babu wani mai taimako da zai taimakeni?), yayin da makiya Allah ke yunkurin shahadantar dashi." Don haka sai Malam Ibrahim yace, " ko da ya kasance, mutum ba ya waccen lokacin da Imam yai waccen kiran, ballantana ya amsa masa, to idan a yanzu ya koka akan abin da ya samu Imamu Hussaini na musiba, tamkar ya amsa masa waccen kiran ne.

A karshe ya koka akan mulkin zalunci, da zubda jinin bayin Allah, dake faruwa babu gaira bare dalili, a kasar nan, inda yace, "mafita kawai shine al'umma tayi koyi da sadaukarwa irin wadda Imam Hussaini yayi, domin samun wanzuwar adalci a doron kasa.

Ya karkare da yin kira ga al'umma, dasu taimaki al'ummar kasar Falasdinu, da duk abin da zasu iya, domin tseratar dasu daga danniya, zalunci da keta, wanda kasar Israila da kawayenta ke aiwatarwa a kansu.

Hakan nan, shima ya fadakar da yan'uwa, kan hakkin shahidan harka a kanmu, inda yace, ya zama wajibi yan'uwa su dauki dawainiyar iyalansu da kuma biyan hakkin shuhada'u na tsarin wata wata ko kuma shekara shekara.

Yayin muzaharar an rarraba takardu ga al'ummar garin na Dawakin kudu, wadda ke dauke da hakikanin sakon Ashura.

Misalin karfe 7: 00 na Magariba, Malam Abdullahi Musa ya gabatar da adu'ar kammalawa, aka sallami jama'a.

26/07/2025

TUNA BAYA
A ranar mai kamar ta yau shekaru goma sha daya da s**a gabata, watau Asabat 26 ga watan Yuli 2014, aka yi wannan ganawa da manema labarai a Gyellesu, Zaria.

Darur Rahama Zaria Kaduna StateTare da Fatima Aliyu Usman, ZariaDa sanyin safiyar wannan rana ta Juma'a ƴan’uwa musulmi ...
26/07/2025

Darur Rahama Zaria Kaduna State

Tare da Fatima Aliyu Usman, Zaria

Da sanyin safiyar wannan rana ta Juma'a ƴan’uwa musulmi Almajiran Sheikh Ibraheem Yaƙoub Alzakzaky Hafizahullah sun fara tuɗaɗowa zuwa Darur Rahama dake Dambo Zariya domin gudanar da taron 25th July na shekarar 2025/1447.

Shekara 11 bayan kisan kiyashin da sojoji s**a ka yi wa 'yan'uwa 34 a ranar Qudus a Zariya. Cikin waɗanda s**a yi shahad...
25/07/2025

Shekara 11 bayan kisan kiyashin da sojoji s**a ka yi wa 'yan'uwa 34 a ranar Qudus a Zariya. Cikin waɗanda s**a yi shahada har da 'ya'yan Shaikh Ibraheem Zakzaky (h) uku.

A rana mai kamar ta yau ne Allah ya yi wa mahaifiya ga Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H), Hajiya Hari Jamo Giɗaɗo (Sali...
21/07/2025

A rana mai kamar ta yau ne Allah ya yi wa mahaifiya ga Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H), Hajiya Hari Jamo Giɗaɗo (Saliha Muhammad Al-Mustafa), rasuwa shekaru goma sha ɗaya da s**a wuce. Allah ya jiƙanta da rahamarsa. Amin.

Mu Karanta Fatiha da Salatin Annabi Allah ya kai ladan gareta da sauran shahidanmu maɗaukaka.

21/07/2025

An ce Trump na samun sauki

Address

Tudun Wada

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ALMIZAN TV Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ALMIZAN TV Hausa:

Share