Tambari

Tambari Tambari News na maraba da ku a shafin Facebook. Domin bayyana Ra'ayi sai a kira mu da Wannan lamba
+234 815 592 8085.

Ko sako ta manhajarmu ta WhatsApp a lamba
+234 815 592 8085

RC:3250291

MUHIMMANCIN KARƁAR KATIN ZABE A ƙarƙashin jagorancin Arc. Shehu Ahmad Tukur Sarkin Fadar Keffi, ana kira ga al’ummar mu ...
28/08/2025

MUHIMMANCIN KARƁAR KATIN ZABE

A ƙarƙashin jagorancin Arc. Shehu Ahmad Tukur Sarkin Fadar Keffi, ana kira ga al’ummar mu da su tabbatar sun karɓi katin zabe domin kada kuri’unsu ya ƙara ƙima da tasiri a zabubbuka masu zuwa.

Katin zabe shi ne makamin da zai ba mu damar zabar shugabanni nagari da za su jagorance mu zuwa ci gaba. Idan ba mu da katin zabe, ba mu da murya a zabubbuka.

Arc. Shehu Ahmad Tukur ya jaddada cewa:
"Zabe hanya ce ta sauya al’amura cikin lumana, kuma karɓar katin zabe shi ne mataki na farko wajen tabbatar da cewa muryar mu ta yi tasiri."

Ku tashi tsaye, ku karɓi katin zabenku, ku zama ɓangare na canji mai kyau!

- Ka karɓi katin zabe
- Ka yi rijista idan baka yi ba
- Ka shirya don kada kuri’a

Sako daga Arc. Shehu Ahmad Tukur – Sarkin Fadar Keffi

DA DUMI-DUMI: Shugaban Sashen Hausa na BBC, Aliyu Tanko, Ya Ajiye AikiShugaban Sashen Hausa na BBC, Aliyu Tanko, ya ajiy...
28/08/2025

DA DUMI-DUMI: Shugaban Sashen Hausa na BBC, Aliyu Tanko, Ya Ajiye Aiki

Shugaban Sashen Hausa na BBC, Aliyu Tanko, ya ajiye aikinsa bayan shafe shekaru 17 yana aikin jarida a gidan.

Tanko, wanda ya zama babban editan BBC Hausa a shekarar 2019, ya tabbatar da murabus ɗinsa ga Jaridar Tambari a ranar Alhamis, inda ya ce ya mika takardar ajiye aiki tare da mika ragamar shugabanci ga wani jami’in BBC.

Sai dai wannan murabus ya zo ne a daidai lokacin da ake rade-radin cewa an dakatar da shi daga aiki tare da kaddamar da bincike kan zargin kuntata wa wasu ma’aikata.

Hukumomi na Ci Gaba da Binciken Musabbabin Haɗarin Jirgin Ƙasa a KadunaHukumomin tsaro da na sufuri a Najeriya na ci gab...
27/08/2025

Hukumomi na Ci Gaba da Binciken Musabbabin Haɗarin Jirgin Ƙasa a Kaduna

Hukumomin tsaro da na sufuri a Najeriya na ci gaba da gudanar da bincike kan musabbabin haɗarin jirgin ƙasa da ya afku a hanyar Kaduna.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne a yayin da jirgin ke kan tafiya, inda ya gamu da tangarda da ta janyo cikas ga zirga-zirgar sa. Duk da yake ba a bayar da cikakken bayani kan asarar rayuka ko raunuka ba, hukumomi sun tabbatar da cewa an ɗauki matakan gaggawa don binciko hakikanin abin da ya haifar da haɗarin.

Ƙalilan ne amma jajirtattu: Dalibai huɗu kacal ne s**a kammala karatu a Jami’ar Nasarawa (NSUK) a fannin Nazarin Harsuna...
26/08/2025

Ƙalilan ne amma jajirtattu: Dalibai huɗu kacal ne s**a kammala karatu a Jami’ar Nasarawa (NSUK) a fannin Nazarin Harsunan Najeriya, Tsangayar Hausa – Ajin 2025

A wani lamari da ya jawo hankalin jama’a, dalibai huɗu kacal ne s**a kammala karatu a Sashen Nazarin Harsunan Najeriya, Tsangayar Hausa, Jami’ar Nasarawa State University Keffi (NSUK) a shekarar 2025.

Wannan adadi ƙalilan ya nuna irin ƙalubale da Hausa ke fuskanta a jami'o'in Najeriya ta fuskar koma baya wajen samun raguwar dalibai a wannan fanni.

Daga cikin waɗanda s**a samu wannan gagarumar nasara har da Umar El-faruk, wanda ya shahara a fagen aikin jarida da yada labarai.

Masana sun bayyana cewa wannan lamari ya tabbatar da cewa fannin Hausa ba fanni ne na wasa ba, domin sai mai haƙuri, jajircewa da ƙwazo ne zai iya kammalawa.

Tambari News na taya waɗannan jarumai murna tare da fatan Allah Ya buɗe musu manyan hanyoyin nasara a rayuwa, ya kuma sa wannan nasara ta zamo hanya ta alheri ga rayuwarsu da al’umma baki ɗaya.

26/08/2025

Babu wata Jam'iyar Haɗaka da za ta iya yin Nasara akan Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.
- A jihar Nasarawa idan za a yi Zoning a bawa wanda ya fi cancanta. Hon. Joseph Maiwada

Ex-Karu Council Chairman Dumps APC, Calls for Stronger Internal DemocracyThe former Executive Chairman of Karu Local Gov...
25/08/2025

Ex-Karu Council Chairman Dumps APC, Calls for Stronger Internal Democracy

The former Executive Chairman of Karu Local Government Council in Nasarawa State, Mr. Samuel Akala, has officially resigned from the ruling All Progressives Congress (APC), effective immediately.

In a resignation letter dated August 22, 2025, and addressed to the APC Chairman of his Panda/Kare ward, Akala expressed gratitude to the party for the platform it provided him to serve in various capacities.

He, however, urged the party leadership to strengthen its internal democratic processes in order to ensure inclusiveness and a sense of belonging for all members.

“May God continue to bless our collective efforts,” Akala stated in his letter.

24/08/2025

Shirye-shiryen fara Musabakar Alqur'ani Mai Girma Karo na 28 wanda za a fara ranar Talata 9 ga watan Satumba 2025 har zuwa ranar Asabar 13 ga watan Satumba a cikin garin keffi jihar Nasarawa.

JUSTICE TO 1000 DISENGAGED TEACHERSWe have come to realized that the government we love and respected are treating the O...
23/08/2025

JUSTICE TO 1000 DISENGAGED TEACHERS

We have come to realized that the government we love and respected are treating the One Thousand (1000) DISENGAGED TEACHERS with neither empathy nor sympathy, our patience and respect for our beloved government is neither considered nor regarded.

The process followed for our disengagement is totally UNFAIR and UNJUST as only One Exam (CBT) was administered to us and no result was out for our verification, while the Seven Hundred and Eighty One (781) were administered Three (3) Series of Assessment Exercise and we believe that should not be a yardstick to termed us as UNQUALIFIED TEACHERS as none among us paid a particular amount to secured the employment letter.

Most of the disengaged teachers left a Suitable Private Attachment (Work) to accept the employment offer given to them by the Teachers Service Commission (TSC) that was APPROVED by the Executive Governor of Nasarawa State, ENGR. ABDULLAHI A. SULE, that approval followed after due scrutiny and assessment exercises conducted by the Board, Chairman and Members of the Teachers Service Commission. But because of the interest of few, the governor without any consideration or onward assessment through Schools is now reversing the Earlier Approved 1000 Teachers as Unqualified and Disengaged with no compensation, and we are replaced in our previous place of Private Attachment that kept us in a state of dilema.

However, we the disengaged One Thousand Teachers are moving to PROTEST based on the above mentioned exercise conducted by the UNQUALIFIED FIRM that knows nothing about Nasarawa State Education system as such, the action taken by the Governor is unfair and unjust to we the 1000 teachers.

Bilyaminu Yusuf Yashi

Chairman. 1000 Disengaged Teachers

Dakarun Sojin Najeriya Na Tabbatar da Cewa Manoma Na Gudanar da Noma Cikin Kwanciyar Hankali – Hedkwatar TsaroHedkwatar ...
22/08/2025

Dakarun Sojin Najeriya Na Tabbatar da Cewa Manoma Na Gudanar da Noma Cikin Kwanciyar Hankali – Hedkwatar Tsaro

Hedkwatar Tsaro ta tabbatar da cewa dakarun sojin Najeriya na ci gaba da gudanar da ayyukan tsaro a faɗin ƙasar domin kare manoma su yi ayyukansu cikin kwanciyar hankali.

Daraktan Yaɗa Labaran Tsaro, Manjo Janar Markus Kangye, ya bayyana haka a Abuja yayin fitar da rahoton makon nan. Ya ce dakarun tare da rundunonin haɗaka sun ƙara tsananta kai hare-hare ta ƙasa da sama kan ’yan ta’adda, ’yan bindiga, masu tayar da kayar baya da masu fasa bututun mai.

A cewar Kangye, wannan tsanantawa ta haifar da hallaka ’yan ta’adda da dama, cafke masu taimaka musu, da kuma ceto mutanen da aka yi garkuwa da su. A Arewa maso Gabas, an yi nasarar hallaka da k**a mambobin Boko Haram da ISWAP, tare da ceto fursunoni a jihohin Borno da Yobe.

A Arewa maso Yamma kuwa, dakarun Operation Fasan Yamma sun ceto mutum 60 da aka yi garkuwa da su tare da k**a wasu 14 da ake zargi da taimaka wa ’yan ta’adda. A Arewa ta Tsakiya, sojojin Operation Safe Haven da Whirl Stroke sun cafke fitaccen mai laifi Adamu Buba, wanda aka fi sani da “Mai Pankshin,” tare da wasu abokan harkarsa 13.

Haka kuma, a Kudancin Najeriya, dakarun Operation Delta Safe sun bankado satar mai da darajarta ta kai Naira miliyan 25 tare da rushe wuraren tace mai na bogi. A Kudu maso Gabas kuwa, sojoji sun yi nasarar k**a da kashe mambobin IPOB/ESN da kuma ceto mata masu juna biyu da yara daga gidan marayu na bogi a Jihar Imo.

Manjo Janar Kangye ya tabbatar da cewa dakarun tsaro za su ci gaba da wannan ƙoƙari har sai an tabbatar da cikakken zaman lafiya a ƙasar.

Sojojin Nijeriya Sun Yi Ajalin ‘Yan Bindiga 7, Sun Kwato Babura 4 a KatsinaDakarun sojin Nijeriya sun samu nasarar fatat...
22/08/2025

Sojojin Nijeriya Sun Yi Ajalin ‘Yan Bindiga 7, Sun Kwato Babura 4 a Katsina

Dakarun sojin Nijeriya sun samu nasarar fatattakar ‘yan bindiga a jihar Katsina, inda s**a kashe akalla mutum bakwai daga cikin su tare da kwato babura guda hudu da mak**an da ke hannunsu.

Rahotanni sun bayyana cewa samamen ya gudana ne a wani ɓangare na yaki da ta’addanci da hare-haren ‘yan fashi da ke addabar al’ummar jihar da makwabtan ta.

Wata majiyar tsaro ta tabbatar da cewa dakarun sun yi aiki bisa bayanan sirri da aka tattaro kafin kai farmakin, lamarin da ya taimaka wajen kawo cikas ga shirin ‘yan bindigar.

An kuma tabbatar da cewa babu wani asarar rai daga bangaren sojoji yayin wannan samame.

22/08/2025

Barka da safiyar Juma'a.

22/08/2025

Hi everyone! 🌟 You can support me by sending Stars – they help me earn money to keep making content that you love.

Whenever you see the Stars icon, you can send me Stars.

Address

Uke

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tambari posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Tambari:

Share