Tambari

Tambari Tambari News na maraba da ku a shafin Facebook. Domin bayyana Ra'ayi sai a kira mu da Wannan lamba
+234 815 592 8085.

Ko sako ta manhajarmu ta WhatsApp a lamba
+234 815 592 8085

RC:3250291

07/06/2026

Abba Laba daga Gundumar Yara, ya ce Hon. Baba Ali ya cancanci karo na uku, duk wanda ya ce ba a yi zaben fidda gwani na APC a garin Keffi ba to bai yiwa kansa Adalci ba.

07/06/2026

An taba yi mana kazafin kona kasuwar Keffi, amma duk abin da mutum zai yi ya tuna da ranar lahira.

- Alhaji Usman SalisuMaiyadi
Shugaban kungiyar Yan Kasuwa na Karamar Hukumar Keffi.

06/06/2026

Alhaji Mudi A*o daga Gundumar Iya ll Yelwan Barau Keffi ya yi godiya ga jama'a da s**a fito zaben fidda gwani tare da bayyana dalilin sake zaɓen Hon. Ibrahim Aliyu Nana Baba Ali a karo na Uku don wakiltatar Keffi ta yamma a zauren majalisar dokokin jihar Nasarawa.

06/06/2026

Wasu shaidu daga kowanne bangare sun sake bayyana kan zarge-zargen taƙaddamar da ta Kunno Kai a kasuwar Keffi ga jawabin Ibrahim Abdullahi sakataren kungiyar yan kasuwa da Yusuf Abdullahi tsohon jami'in kula da kasuwa.

•Nan gaba akwai jawabin Bulaman Keffi da Shugaban kungiyar yan kasuwa.

06/06/2026

Rahotanni sun nuna cewa Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Taraba, tare da Shugaban Ƙaramar Hukumar Karim Lamido da ‘yan majalisar dokokin jihar masu wakiltar mazaɓun Karim I da Karim II, sun maƙale a cikin laka yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa wani taron tsaro a Karim Lamido ranar Alhamis.

Alhamdulilah Sheikh Muhammad Nuru Khalid ya samu sauki a asibitin da aka kwantar da shi jiya a kasar Saudiyya.Muna Godiy...
06/06/2026

Alhamdulilah Sheikh Muhammad Nuru Khalid ya samu sauki a asibitin da aka kwantar da shi jiya a kasar Saudiyya.

Muna Godiya da addu'oin ku baki daya da fatan Allah ya ba saura marasa lafiya dake gida da Asibiti sauƙi.

06/06/2026

Manajan Kasuwar Keffi Kasim Abdullahi ya ce Gwamnati na da ikon karban duk wani waje (Revoking)da aka samu rikici a kasuwa har zuwa lokacin da za a kammala bincike.

Yusuf Abdullahi ya ce yana daya daga cikin wanda ya kai yaran Alhaji Musa Asibiti lokacin da s**a samu rauni.

05/06/2026

Babban Malami a Najeriya Sheikh Muhammad Nuru Khalid ya na fama da rashin lafiya a kasar Saudiyya bayan kammala aikin hajjin bana na 2026.

Allah ya karawa malam lafiya.

Ruwan Sama Mai Ƙarfi Ya Rushe Gadar Da Ke Haɗa Jalingo da YorroWata gada mai muhimmanci da ke haɗa wasu yankuna na ƙanan...
05/06/2026

Ruwan Sama Mai Ƙarfi Ya Rushe Gadar Da Ke Haɗa Jalingo da Yorro

Wata gada mai muhimmanci da ke haɗa wasu yankuna na ƙananan hukumomin Jalingo da Yorro ta rushe sakamakon mamakon ruwan sama da aka yi.

Rahoton Tambari News ya nuna cewa gadar, wadda ke kan hanyar Muslim Council a Jalingo, ta karye ne bayan ruwan saman mai ƙarfi, lamarin da ya katse zirga-zirga tare da kawo cikas ga harkokin kasuwanci da rayuwar al’umma a yankunan da abin ya shafa.

Mazauna yankin sun yi kira ga gwamnati da hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta ɗaukar matakan gyaran gadar domin sauƙaƙa wa jama'a wahalhalun da suke fuskanta.

Sarkin Matasan Keffi Ya Fice Daga APCRahotanni sun tabbatar da cewa Abdulaziz SK Danladi, wanda aka fi sani da Sarkin Ma...
04/06/2026

Sarkin Matasan Keffi Ya Fice Daga APC

Rahotanni sun tabbatar da cewa Abdulaziz SK Danladi, wanda aka fi sani da Sarkin Matasan Keffi, ya yi murabus daga jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Danladi, tsohon ɗan majalisar dokokin Jihar Nasarawa kuma jigo a siyasar Keffi, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar bayan faduwa zaben fidda gwani da jam'iyyar da gudanar kwanakin baya, ficewr na zuwa ne a wani mataki da ke ƙara sauya yanayin siyasa a jihar gabanin zaɓen 2027.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, bai bayyana jam’iyyar da zai koma ba ko kuma cikakken dalilin ficewarsa daga APC.

Address

Uke

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tambari posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Tambari:

Share