Tambari

Tambari Tambari News na maraba da ku a shafin Facebook. Domin bayyana Ra'ayi sai a kira mu da Wannan lamba
+234 815 592 8085.

Ko sako ta manhajarmu ta WhatsApp a lamba
+234 815 592 8085

RC:3250291

CIKIN HOTUNA: Fuskokin Wasu Daga Cikin Dattawan Ƙungiyar Tripple R Kannywood Wacce Rarara Yake Jagoranta A Wajen Taronsu...
10/09/2026

CIKIN HOTUNA: Fuskokin Wasu Daga Cikin Dattawan Ƙungiyar Tripple R Kannywood Wacce Rarara Yake Jagoranta A Wajen Taronsu Na Yau A Garin Kahutu Dake Jihar Katsina

GANI GA WANE: ƳAN SANDA SUN K**A HĀFSAT ABUBAKAR KAN LABARIN OPAYRundunar ’yan sanda ta k**a Hafsat Abubakar, wadda ake...
10/09/2026

GANI GA WANE: ƳAN SANDA SUN K**A HĀFSAT ABUBAKAR KAN LABARIN OPAY

Rundunar ’yan sanda ta k**a Hafsat Abubakar, wadda ake zargi da fara yaɗa wani labari cewa Opay za ta daina aiki a Najeriya.

Rahoton ya ce k**a Hafsat na da alaƙa da yaɗa wannan saƙo, wanda ya janyo hankalin jama’a a kafafen sada zumunta.

09/09/2026

Ya k**ata yan Najeriya su yiwa Ministan Tsaro Christopher Musa Adalci, kada a duba kalamansa akan Nasir El-Rufai.

-Alhaji Abdullahi Ibrahim Mai Sharhi kan harkokin tsaro

08/09/2026

Zazzafan Martanin Martanin Murtala Gamji ga Ministan Tsaron Najeriya, Christopher Musa

Shugaban Ƙungiyar Dattawan Matasan Arewacin Najeriya, Kwamared Murtala Gamji, yayi martanin ne a wani Sakon Murya da aikawa manema labarai ta Whatsapp, biyo bayan kalaman da Ministan tsaron, yayi akan toshon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru El-rufa'i.

NSUK: VC TA SHIRYA TATTAUNAWA DA ASUU DOMIN ƘARE YAJIN AIKITambari News  Mataimakiyar Shugabar Jami’ar Jihar Nasarawa, K...
08/09/2026

NSUK: VC TA SHIRYA TATTAUNAWA DA ASUU DOMIN ƘARE YAJIN AIKI

Tambari News

Mataimakiyar Shugabar Jami’ar Jihar Nasarawa, Keffi (NSUK), Farfesa Sa’adatu Hassan Liman, ta jagoranci wani babban taron masu ruwa da tsaki da shugabannin ASUU, domin tattaunawa kan yadda za a kawo ƙarshen yajin aikin da ya shafe wata guda yana gudana. Taron da aka gudanar ranar 7 ga Satumba, 2026, ya mayar da hankali kan samo mafita mai ɗorewa da dawo da harkokin karatu cikin gaggawa.

A yayin taron, mahalarta sun tattauna kan matsalolin da s**a haifar da yajin aikin, inda s**a nuna aniyar ci gaba da tattaunawa domin samun maslaha. Mataimakiyar Shugabar Jami’ar ta jaddada muhimmancin warware rikicin cikin lumana, musamman saboda ɗaliban da karatunsu ya samu tsaiko, tare da tabbatar da cewa mahukuntan jami’ar za su ci gaba da ƙoƙarin ganin an dawo da harkokin karatu cikin kankanin lokaci.

ZARGIN ƁATA SUNA: JNI DA CAN SUN NEMI A HANA MINISTAN TSARO CI GABA DA MAGANA KAN EL-RUFA’ITsohon Gwamnan Jihar Kaduna, ...
08/09/2026

ZARGIN ƁATA SUNA: JNI DA CAN SUN NEMI A HANA MINISTAN TSARO CI GABA DA MAGANA KAN EL-RUFA’I

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya buƙaci Ministan Tsaro, Christopher Musa, ya biya shi Naira biliyan 10 tare da neman afuwa, bisa zargin yin kalaman da s**a ɓata masa suna a gidan talabijin.

Rahotanni sun ce ƙungiyoyin Jama’atu Nasril Islam (JNI) da Ƙungiyar Kiristocin Najeriya (CAN) sun kuma nemi a ɗauki matakin hana Ministan ci gaba da yin wasu kalamai kan El-Rufai, yayin da takaddamar da ke tsakanin ɓangarorin ke ci gaba da ɗaukar hankali.

ANGWAN RIMI YOUTH TA FUSATA KAN RASHIN DAMAR GANIN SANATA WADADA, TA KARƁI ƊANSA MODIBBOTambari News  Shugabanni da mamb...
08/09/2026

ANGWAN RIMI YOUTH TA FUSATA KAN RASHIN DAMAR GANIN SANATA WADADA, TA KARƁI ƊANSA MODIBBO

Tambari News

Shugabanni da mambobin Angwan Rimi Youth Intellectual Association, Keffi, sun bayyana fushinsu kan rashin samun damar ganawa kai tsaye da Sanata Ahmad Aliyu Wadada, ɗan takarar Gwamnan Jihar Nasarawa na jam’iyyar APC. Ƙungiyar ta karɓi ɗansa, Modibbo, inda ta miƙa masa littattafan rubutu guda 500 da littattafan koyon karatun Islamiyya guda 500 a matsayin nuna goyon baya ga burin siyasar mahaifinsa.

Ƙungiyar ta ce goyon bayanta bai tsaya kan gudummawar kayan aiki ba, inda ta bayyana cewa mambobinta sun gudanar da karatun Hizb 60 na Alƙur’ani a kowace rana tsawon kwanaki 30 na Ramadan, tare da yin addu’ar samun nasarar Sanata Wadada. Sai dai sun nuna takaicinsu kan yadda s**a kasa samun damar ganawa da shi, suna zargin cewa wasu daga cikin mutanen da ke kewaye da shi na iya zama shinge tsakanin sa da masu goyon bayansa. A nasa ɓangaren, Modibbo ya ba su haƙuri, ya gode musu kan gudummawar da addu’o’in da suke yi, tare da yin alƙawarin isar da saƙonsu ga mahaifinsa da kuma ƙoƙarin haɗa su domin su gana da Sanatan.

TINUBU HOUSE TO HOUSE NETWORK TA KARRAMA BARADEN KEFFITambari News  Reshen Jihar Nasarawa na ƙungiyar Tinubu House to Ho...
08/09/2026

TINUBU HOUSE TO HOUSE NETWORK TA KARRAMA BARADEN KEFFI

Tambari News

Reshen Jihar Nasarawa na ƙungiyar Tinubu House to House Network ya karrama Prince Abdullahi Attajiri (Baraden Keffi) da lambar yabo ta Award of Excellence bisa gudunmawarsa da jajircewarsa wajen tallata manufofin Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi A. Sule.

An gabatar da lambar yabon ne a ranar 7 ga Satumba, 2026, a gidansa da ke Keffi, inda ƙungiyar ta bayyana karramawar a matsayin nuna godiya da yabawa bisa irin gudunmawar da yake bayarwa wajen ci gaban al’umma da ayyukan ƙungiyar.

07/09/2026

Hon. Daniel Oga Ogazi ya yi zazzafan Martani ga masu yada siyasar Addini da Kabilanci a jihar Nasarawa.

Address

Uke

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tambari posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Tambari:

Shortcuts

Share