KTG News Hausa

KTG News Hausa Wannan Shafi an kirkire shine domin kawo muku sahihan Labarai da S**a shafi Nigeria, Arewa harma da kasashen ketare.

Kungiyoyi Dalibai A Jihar Bauchi Sun Mara Wa Hon Farouk Mustapha Baya Domin Takarar Gwamnan A Zaɓen 2027Kungiyoyin ɗalib...
08/08/2025

Kungiyoyi Dalibai A Jihar Bauchi Sun Mara Wa Hon Farouk Mustapha Baya Domin Takarar Gwamnan A Zaɓen 2027

Kungiyoyin ɗalibai na ƙananan hukumomi 20 na jihar, ƙarƙashin jagorancin Hon. Hamza Muhammad Maikudi — mai ba Gwamnan Bauchi shawara na musamman kan harkokin ɗalibai — sun kai ziyarar tabbatar da goyon baya ga Rt. Hon. Farouk Mustapha, kwamishinan ci gaban karkara da harkokin musamman.

Wannan matakin ya nuna ƙara samun ƙarfin gwiwar Farouk Mustapha a siyasar jihar, duba da irin tasirin da ƙungiyoyin ɗalibai ke da shi wajen tsara makomar jihar.

Bayan jerin tattaunawa da bukukuwan taya murna da aka gudanar a cikin da wajen al’ummar ɗalibai, ƙungiyoyin sun bayyana Farouk Mustapha a matsayin ɗan siyasa mai kishin al’umma, tare da nuna gamsuwa da rawar da ya takawa wajen inganta rayuwar matasa da tallafa musu.

Da yake mayar da martani kan wannan goyon baya, Rt. Hon. Farouk Mustapha ya bayyana godiya, yana mai cewa har yanzu yana shawara da iyali, abokai, da kuma Gwamnan Jihar kan makomar siyasar da zai dauka. Ya kuma jaddada cewa haɗin kan matasa da tallafin al’umma shi ne ginshiƙin nasara a kowace irin fafutuka ta siyasa.

Masu sharhi na ganin wannan matakin na iya zama babban abin da zai rinjayi manufar siyasar jihar Bauchi a 2027, duba da yadda matasa za su iya zama ginshiƙin goyon baya mai ƙarfi ga Farouk Mustapha a ko’ina cikin jihar.

KBC Hausa

Jami'an Tsaro Sun Kora Mutumin Da Ya Yi Tattaki Daga Jigawa Zuwa Kano Domin Ganin Gwamna Abba Kabir Bayan Yace Ko Zai Yi...
08/08/2025

Jami'an Tsaro Sun Kora Mutumin Da Ya Yi Tattaki Daga Jigawa Zuwa Kano Domin Ganin Gwamna Abba Kabir Bayan Yace Ko Zai Yi Shekara Guda Ba Zai Tafi Ba Har Sai Ya Ga Abba

A lokacin da yake hanyar tahowa dai, gwamnatin Kano ta bakin kakakin Gwamna Abba ya umarci mutumin da ya koma gida amma duk da haka ya bijire ya taho.

YANZU-YANZU: An bawa Yan jaridu damar ganawa Da Omoyele Sowore a Shelkwatar Yan sanda Najeriya dake Abuja.Cikakken bayan...
08/08/2025

YANZU-YANZU: An bawa Yan jaridu damar ganawa Da Omoyele Sowore a Shelkwatar Yan sanda Najeriya dake Abuja.
Cikakken bayani nan tafe.

YANZU-YANZU Peter Obi ya bada Gudummawar Naira miliyan 10 ga Makarantar Malikiyya dake nan Bauchi.
08/08/2025

YANZU-YANZU

Peter Obi ya bada Gudummawar Naira miliyan 10 ga Makarantar Malikiyya dake nan Bauchi.

🚨 𝐓𝐀 𝐓𝐀𝐁𝐁𝐀𝐓𝐀: Manchester United ta kammala daukar Benjamin Šeško daga RB Leipzig kan €85m kuma ya rattaba hannu zuwa she...
07/08/2025

🚨 𝐓𝐀 𝐓𝐀𝐁𝐁𝐀𝐓𝐀: Manchester United ta kammala daukar Benjamin Šeško daga RB Leipzig kan €85m kuma ya rattaba hannu zuwa shekarar 2030..

— FabrizioRomano

Yadda Tsoffin Kansiloli A Jihar Kano S**a Yi Wa Shugaban Jam'iyyar APC Na Kano, Abdullahi Abbas Shagube Kan Kalaman Da Y...
07/08/2025

Yadda Tsoffin Kansiloli A Jihar Kano S**a Yi Wa Shugaban Jam'iyyar APC Na Kano, Abdullahi Abbas Shagube Kan Kalaman Da Ya Yi Game Da Biyansu Hakkokinsu Da Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Yi

Daga Mujaheed Aminu Shehu Tsakuwa Dawakin Kudu

Innalillahi wa inna IlaiHi Rajiun. Allah ya yiwa Mahaifin Dr Bello Galadanchi (Dan Bello) rasuwa yanzun nan~ Abba Hikima...
07/08/2025

Innalillahi wa inna IlaiHi Rajiun.
Allah ya yiwa Mahaifin Dr Bello Galadanchi (Dan Bello) rasuwa yanzun nan~ Abba Hikima

Allah ya gafarta masa. Ameen.

KAMAR JAMB, AN SAMU MATSALA A SAKAMAKON WAEC NA 2025.Hukumar Shirya Jarabawar Yammacin Afirka (WAEC) ta sanar da jama'a ...
07/08/2025

KAMAR JAMB, AN SAMU MATSALA A SAKAMAKON WAEC NA 2025.

Hukumar Shirya Jarabawar Yammacin Afirka (WAEC) ta sanar da jama'a game da matsalolin fasaha da s**a shafi sak**akon jarabawar WASSCE ta shekarar 2025. WAEC ta bayyana cewa an gano wadannan matsaloli ne yayin da suke duba sak**akon da aka saki kwanan nan.

Hukumar ta bada hakuri ga ɗaliban da abin ya shafa tare da ba da shawarar cewa wadanda s**a duba sak**akon nasu a baya su sake dubawa cikin sa’o’i 24 masu zuwa.

An samu irin wannan Matsalar a lokacin rubuta jarabawar JAMB na wannan shekara wanda hakan ya jawo dalibai da yawa basu samu damar rubuta jarabawa ba.

A Hukumance: An fitar da jerin ƴan takarar 2025 Balland'Or mutum 30 na maza!!! ✅• Fagen Wasanni
07/08/2025

A Hukumance: An fitar da jerin ƴan takarar 2025 Balland'Or mutum 30 na maza!!! ✅

• Fagen Wasanni

Alhamdulillah, Masu garkuwa da Mutane sun saki Murtala Abdulkadir, dan uwansa na jini ya tabbar mana da hakan.A halin ya...
07/08/2025

Alhamdulillah, Masu garkuwa da Mutane sun saki Murtala Abdulkadir, dan uwansa na jini ya tabbar mana da hakan.

A halin yanzu suna hanyar da wowa gida.

Allah ya kara kiyayewa na gaba.

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAAJI'UN

Mun samu rahoto mai tayar da hankali daga wani Mazaunin garin Azare yana neman taimakon addu’o’in jama’a bayan da masu garkuwa da Mutane s**ayi garkuwa da Kaninsa (Murtala Abdulqadir)

Ƙaninsa ya shiga hannun masu garkuwa da mutane ranar Lahadi, a hanyarsa ta dawowa gida daga Enugu zuwa Azare.

Masu garkuwar sun tuntubi iyalansa suna neman kuɗi masu yawa kafin su sake shi.

Da wannan yake neman Don Allah ‘yan uwa mu tayashi da addu’a Allah Ya kubutar da shi lafiya, Ya ƙarfafi iyalansa, Ya tona asirin masu wannan mummunan aiki.

DA DUMI-DUMI: Sultan ya shaƙi iskar ƴanci bayan tsawon kwanaki a kame, yanzu haka an bada belinsa.An Saki Ɗan TikTok Sul...
07/08/2025

DA DUMI-DUMI: Sultan ya shaƙi iskar ƴanci bayan tsawon kwanaki a kame, yanzu haka an bada belinsa.

An Saki Ɗan TikTok Sultan Bayan Zargin Wallafa Bidiyon Rashin Lafiyar Shugaban Ƙasa Tinubu.

Matashin ɗan TikTok mai suna Sultan da aka k**a kwanakin baya bisa zargin wallafa wani bidiyo da ke nuni da cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na fama da rashin lafiya, yanzu haka ya samu 'yanci bayan an sake shi daga hannun DSS.

An ce an wallafa bidiyon ne a dandalin TikTok na bogi da ke amfani da Sunan Sultan wanda ya janyo cece-kuce a tsakanin jama'a.

HOTUNA: Gwamnan jihar Bauchi Sen. Bala Mohammed Abdulkadir ya ziyarci asibitin garin Bagel a karamar hukumar Dass dan du...
07/08/2025

HOTUNA: Gwamnan jihar Bauchi Sen. Bala Mohammed Abdulkadir ya ziyarci asibitin garin Bagel a karamar hukumar Dass dan duba yanda aiki ke tafia a asibitin.

Address

Masallacin Idi Street Azare
Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KTG News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to KTG News Hausa:

Share