IDON AREWA 24

  • Home
  • IDON AREWA 24

IDON AREWA 24 INGANTATTUN LABARAI

DA ƊUMI-ƊUMI: Yan Jamhuriyyar Nijar sun fara kiranyen Shugaban Kasar Rasha Putin, da ya goyi bayansu, ya kuma tallafa ma...
21/08/2023

DA ƊUMI-ƊUMI:

Yan Jamhuriyyar Nijar sun fara kiranyen Shugaban Kasar Rasha Putin, da ya goyi bayansu, ya kuma tallafa masu a gumurzun da za su yi da ECOWAS.

PLATFORM (PONZI SCHEME)Abunda yake faruwa gameda abubuwan da s**a samu mutanenmu wanda akwai su daga ko wannen bangare n...
21/08/2023

PLATFORM (PONZI SCHEME)

Abunda yake faruwa gameda abubuwan da s**a samu mutanenmu wanda akwai su daga ko wannen bangare na kasar nan, saidai mafi yawan abun tausayi da zakaji shine daga arewa ne, kuma hakan ya samo asali ne daga wasu tsiraren mutanen da s**a san hadarin abun amma s**aki sanar da yan uwa da abokan arzikinsu da s**a gayyato acikin harkar, Sai kuma wa'yanda suma kansu gayyatar su akayi basu san hadarin dake cike da abinba, kuma aka dora su akan hanyar kawo wasu domin abunda suke samu ya ninku.

Banso nace komai ba akan wannan hali da yan uwa da abokan mu s**a tsinci kansu aciki, na rasa makudan kudade, dukda wasu kuma alhamdulillah sun samu alkhairi sosai, Ba zanyi wannan rubutu ne ba domin cin mutuncin wasu ba, hasali Nima Dinnan ina platform kuma alhamdulillah zan iya cewa kaso 80% cikin dari 100% na platform dinda nayi acikin riba nake suke guduwa, adan karamin tunani na platform mafi hatsari shine wanda ake ninka maka duk abunda ka saka acikin awa ashirin da hudu 24hrs (DOUBLER), masu yin platform munsan abunda ake nufi da DOUBLER, to ni Dinnan nayi DOUBLER.

Asarar da aka samu wannan karon yanada alaka da yanda wasu mutanen s**a dauki cewa platform Dinnan suma fah kaman bankunan mune na gargajiya wato First Bank ko UBA, wannan shine babban kuskuren da sababbi a harkar s**a aikata kuma yazama sillar wannan mummunar asarar, bana tunanin akwai wanda yasan platform irinsu, INSMI, UWORK, SUN POWER, ToLike, ON THE WAY, Sbot da Strx da sauransu, ko kuma yayi shekara daya yana platform amma ace wai baya cire abunda yake samu acikin wayanan platform din irinsu, MTFE, AlphaAGPT, Catly 🤔, shiyasa zamuji asarar tafi yawa ga wa'yanda Ba'a yi musu cikakken bayanin akan harkar ba.

Naji mamakin yanda wasu s**a dinga bayarda kwarin guiwa wa wasu mutane su siyarda abunda s**a mallaka su shiga harkar, wanda duk wani babba aharkar bazai baka wannan shawara ba, hasali ma nasan CEO MTFE wanda yace cewa basa don suji ance za'a siyar da wata kadara ashiga sunfison suji ance ancire daga ciki an siyi kadarorin.

Yau naji wani lost daga bakin mai ita wanda ya girgizani amma babu abinda na'iya fiyeda nace Allah ya mayar da alkairi, dan Allah ya kamata komai zamu saka wasu mudinga fada musu alkairi da kuma abunda ke iya faruwa idan aka samu matsala, nayi platform abaya wanda yanzun na fahimci kuskuren dake cikin hakan saboda abunda ya faru wannan lokacin, ina rokon Allah da ya yafe mana kuma ya bamu ikon gane gaskiya da yarda da ita komai Dacinta.

a karshe ina mai rokon Allah ya mayar da alkairi ga wyaanda wannan abu ya rutsa dasu.

KUKAN-KURCIYA!Ya ku al'ummar jihar Zamfara da katsina.Kafin ku karbi takardar N2,000, spaghetti da omo don musanya kuri'...
07/03/2023

KUKAN-KURCIYA!
Ya ku al'ummar jihar Zamfara da katsina.

Kafin ku karbi takardar N2,000, spaghetti da omo don musanya kuri'unku, kuyi tunani a kan abubuwa masu zuwa:

1. Da yawa daga cikinku ba za su iya cin abinci sau biyu a rana ba saboda hauhawar farashin kayan masarufi. Magidanta da yawa suna kwanciya barci da wofi ba tare da wani taimako da ya zo daga masu kiran kansu ’yan siyasa ba.

2. ’Yan fashi sun mamaye al’ummarku da rana, sun mamaye kowane gida a kauyenku, sun yi wa matanku fyade, da ‘ya’yanku mata da maza, sun sace gwammai, uwaye maza da mata da danginku, sun tafi da shanunku, amfanin gonarki da sauran kayayyaki masu daraja. kunnemi miliyoyin kuɗi don 'yantar da dangin ku. A duk cikin wannan mawuyacin lokaci babu wani dan siyasa da ya kawo muku agaji.

3. Babu makaranta a unguwar ku. Yaranku sun yi tafiyar kilomita 15 daga gida kafin su halarci makaranta a garin. Babu tsarin kula da lafiya a cikin al'ummar ku. Matan ku da ke naƙuda sai an yi tafiyar kilomita 20 zuwa gari kafin ta haihu. Babu ruwa a yankinku. Yaranku sai sun yi tafiyar kilomita 10 ƙasa don samun ruwa daga rafin.

Shin N2,000 na takarda, spaghetti da omo zai magance duk waɗannan matsalolin da aka ambata?

Naira 2,000, spaghetti da omo za su taimaka wajen samar da tsaro a Arewa domin manoma su samu damar shiga gonakinsu?

Shin N2,000, spaghetti da omo za su iya ciyar da iyalinka na tsawon shekaru 4?

Ka yi tunani kafin ka jefa kuri'un ku akan N2,000 takarda, spaghetti da omo.
"kukan kurciya jawabine ga mai hankali"
CAN CANTA DAN CIGABAN JAHARMU DA AL UMMARMU.
posted Abdulazeez Mantu
repost: ibrahim dodo
Fassarawa: @gmail.com

08/11/2022
SHIRU KAKE JI, KAMAR BA ABIN ALKHAIRI YA YI BA.Ministan sadarwa na Nigeria Prof.  Isah Ali Ibrahim Pantami ya tsaya tsay...
06/09/2022

SHIRU KAKE JI, KAMAR BA ABIN ALKHAIRI YA YI BA.

Ministan sadarwa na Nigeria Prof. Isah Ali Ibrahim Pantami ya tsaya tsayin daka, ya aikawa shugaban kasa Muhammadu Buhari takardar korafi akan cewa ka da a kara haraji a harkar sadarwa.

Ministan ya nunawa shubaga Muhammadu Buhari cewa idan aka shigo da haraji, an kara jefa al’umma da tattalin arziki a cikin matsala.

Duk da Irin wanna abin Alkhairi da wannan Bawan Allah ya yi kowa yaja bakin sa yayi shiru. inda ace kuma wani abin sharri ne ba wannan ba, da yanzu kowa ya dauka har Wanda baya posting ma sai yayi saboda bakar kiyayya da hasada. kamar yadda kuke fitowa kuna tsine masa Albarka, tunda dai wannan abin Alkhairi yayi, kuma ya shafi kowa da kowa kamata yayi a cire hasada a fito a yaba masa. ana son idan ka fadi sharrin mutum, idan yayi Alkhairi ma ka fada. domin ko wani mutum a duniya yana da nashi Alkhairi sannan kuma yana da sharri.

wato su fa mutane, idan kace zaka faranta musu, zaka musu abin da suke so don su yabeka, to wallahi baka san rayiwa ba, kuma ka batawa kanka lokaci, mutane ba'a iya musu. wannan abu ya saka na Kara daukan darussa.

Allah ya taimaki Isah Ali, ya tsare shi daga sharrin munafukai da kuma ainahin mahasada Amin.

Na Gwamnace Auren Dan Pi_Netwok Da Auran Dan baro~ Murjanatu Diri Dana Auri Mai Tukin Baro Kara Na Auri Mai Mining Pi_Ne...
03/09/2022

Na Gwamnace Auren Dan Pi_Netwok
Da Auran Dan baro~ Murjanatu Diri

Dana Auri Mai Tukin Baro Kara Na Auri Mai Mining Pi_Network Ko Banza Siffofin Zama Zama Biloniya Sunfi Nunawa Tare da shi.

Matashiyar wacce tayi Kaurin Suna a Yanar gizo Murjanatu Diri ta tabbatarwa Wakilinmu cewa; Dan Pi_Network duk wasu Sufofin alamomin zamtowar Shi mai Arziki Sun bayyana daga gare shi.

Za Mu Taimaka Wajen Ganin PDP Ta Yi Rashi Nasara A Zaben Shugaban Kasa Na 2023, Cewar Gwamna WikeWike ya bayyana hakan n...
01/09/2022

Za Mu Taimaka Wajen Ganin PDP Ta Yi Rashi Nasara A Zaben Shugaban Kasa Na 2023, Cewar Gwamna Wike

Wike ya bayyana hakan ne a yayin kaddamar da wani t**i a yankin Omerelu dake karamar hukumar Ikwerre a jihar ta Ribas.

Sannan ya kara da cewa shugaban Jam'iyyar PDP, Iyochia Ayu da yake cewa su yara ne ya manta cewa sune s**a kawo shi kan kujerar da yake kai.

DA ƊUMI ƊUMI: Za'a  Rubuta Sunan Ganduje A Cikin Kundin Sunayen Mutanen Da S**a Ba Wa Musulunci Gagarumar Gudunmawa A Ƙa...
01/09/2022

DA ƊUMI ƊUMI: Za'a Rubuta Sunan Ganduje A Cikin Kundin Sunayen Mutanen Da S**a Ba Wa Musulunci Gagarumar Gudunmawa A Ƙarni Na 21 A Cikin Kundin Tarihin Musulunci

Ƙasar Saudiyya ta duƙufa wajen tsara biki na musamman domin karrama mai girma gwamnan Jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje a dalilin namijin ƙoƙarinsa wajen musuluntar da maguzawa sama da mutum dubu goma batare da zubar da jini ba.

A cewar mahukuntar ƙasar, abin da gwamna Gandujen ya yi wata babbar gudunmawa ce ga addinin musulunci wacce babu wani ɗan siyasa da ya taɓa ba da irinta a Afrika ta yamma gaba ɗaya a wannan ƙarni na 21 tayadda hakan ke nuni da yadda gwamnan ya cancanci yabo.

Ƙasar ta Saudiyya ta kuma ƙara da cewa a dalilin wannan ƙoƙari da gwamna Ganduje ya yi, za ta rubuta sunansa a cikin kundin tarihinta wanda ta samar domin rubuta sunayen mutanen da ke ba wa musulunci gudunmawa mai girma a Nahiyar Afrika.

Wannan dai ba shi ne karo na farko da ƙasar ta Saudiyya ta ke yabawa gwamna Ganduje a kan ƙoƙarinsa na hidimtawa addinin musulunci ba, ko da a baya ta taɓa karrama shi da lambar yabo mai ɗauke da ƙyallen ɗakin Ka'aba.

Sai dai a wannan karon a na tunanin salon karramawar zai sha bamban da duk wanda aka taɓa yi masa a baya girma domin kuwa gagarumin biki ne na musamman wanda ake za ra halartar manyan shugabanni na duniya.

Wane fata zaku yi masa?

Tarihin MARIGAYI SHEIKH MUHAMMAD GONI AISAMIGWAGWARMAYAR YADA ADDININ MUSLUNCI DA:Marigayi Sheikh Muhammad Goni Aisami {...
21/08/2022

Tarihin MARIGAYI SHEIKH MUHAMMAD GONI AISAMI

GWAGWARMAYAR YADA ADDININ MUSLUNCI DA:

Marigayi Sheikh Muhammad Goni Aisami {Ya Sheikh} Gashua

A fagen Wa'azi da karantarwar Addinin muslunci akan doron Qur'ani da Sunnah.

✍️ Daga: Shehu A. A. Gashua

Shahidi Sheikh Muhammad Goni Aisami ya fara yin fice ne sosai a fagen Wa'azi da kungiyar Izalah take gudanarwa a mako-mako a Cikin unguwanni dake cikin Garin Gashua a shekarar 1992. Shehin malamin ya iya jawo hankalin Matasa da Dattawa a lokacin da yake wa'azi Kuma cikin shikima da Girmamawa.

Sheikh Goni ya Fara gabatar da Tafsirin Al-Qur'ani Mai Girma a watan Ramadan a Masallacin Juma'ah na kungiyar Jibwis dake unguwar Kofar Halliru Gashua a shekarar 1995 inda Alaramma Idriss Abdurrahman Gashua yake ja Masa Baki.

Ya sheikh ya Zama shugaban Majalisar Malamai na kungiyar Jibwis na Bade Local Government (Gashua) a shekarar 1996 har zuwa 2002. Inda malamin ya rike Sakataren Majalisar Malamai na Jihar Yobe na riko na tsawon wata shida.

Bayan Tafsirin Al-Qur'ani Mai Girma da yake yi a Kofar Halliru, sheikh ya dauki shekaru Goma Sha uku Yana Tafsirin Al-Qur'ani Mai Girma a Masallacin Juma'ah dake kofar Mai martaba sarkin Bade da yamma kafin bisani ya farayin na Dare a Babban Masallacin na fada shine tsawon shekaru.

Ya Sheikh, ya dawo da makarantar sa zuwa kofar Gidan sa a inda yacigaba da yin Tafsirin Al-Qur'ani Mai Girma tin a shekarar 2011 har izu a bana ta 2022.

Sheikh Goni Aisami Shine Wanda ya Assasa wa'azin karkara da a keyi a duk karshen wata a kauyikan Gashua, Jakusko, karasuwa, Nguru da Guri a Jihar Jigawa a shekarar 1996 inda muke shiga Kauyika domin karantar da Al'umma sunnar Annabi muhammad (sallallahu Alaihi Wasallam)

Sheikh Goni munkoyi jajircewa ne akan Aikin Addinin muslunci daga gareshi wajen nuna kauna, kyauta, sakin fuska, Ziyara da jawo mu a Jikin sa sosai domin mu tsaya akan hidimar Addinin muslunci.

A duk shekara idan shehin malamin zai tafi Aikin Hajj to a inda Yan Agaji suke anan yake sauka Haka ma dawowar sa. Ko a wannan shekara ma ya sheikh a wajen mu ya sauka.

Sheikh mutun ne Mai son mutane sosai da Gaske Wanda a zahira duk Garin Gashua babu mutum Mai yawan yiwa Al'umma sallama, a duk inda yaga mutum zai daga hannu yayi Masa sallama cikin fara'ah da Annashawa a fuskar sa a koyaushe.

Sheikh Goni Aisami, mutum ne son a ziyarce shi a Gidan sa domin bayason rabuwa da mutane a kusa da shi. Sheikh Goni malami ne Mai fadin gaskiya akan kowaye komin mulkin sa Kuma komin kudin sa.

Akwai wani Lokaci da barayi S**a tare mu mundawo daga wajen wa'azi a Garin Dagona, s**ayi Mana kaca kaca har sai da muka kwanta a Asibiti Ni da malam.

Sheikh Goni malami Mai so da kaunar 'yan Agaji sosai da Gaske a inda duk inda yaga Dan Agaji Yana girmamashi kwarai da Gaske.

A Ranar rufe Tafsirin sheikh na bana Ina zaune a wajen, sheikh yace Ina kaunar Shehu Abdurrahman Agaji Kamar yadda nake kaunar yayana.

Shekaran jiya Juma'ah da Daddare wani sojan Nigeria katon Arne ya halaka shi. Ya Allah ka saka Mana.

Ya Allah ka Karɓi shahadar Sheikh Muhammad Goni Aisami.

Daga
Shehu A. Abdurrahman Gashua

21/08/2022
WASU SOJOJI 'YAN FASHI SUN HARBE BABBAN MALAMIN MUSULUNCIWannan da ake gani a hoto Malamin addinin Musulunci ne, sunansa...
21/08/2022

WASU SOJOJI 'YAN FASHI SUN HARBE BABBAN MALAMIN MUSULUNCI

Wannan da ake gani a hoto Malamin addinin Musulunci ne, sunansa Sheikh Muhammad Goni Aisami

Ranar juma'a da ta gabata, Malamin yana kan hanya daga jihar Kano zuwa Gashuwa a jihar Yobe cikin motarsa kirar Honda 2006 model, ya iso kusa da barikin Sojoji na Nguru, sai wani Soja mai mukamin Lance Corporal sunansa JOHN GABREIL ya tareshi, ya roki ya rage masa hanya zuwa Jaji-Maji

Malamin sai ya daukeshi a mota s**a tafi, suna cikin tafiya sun iso wani kauye da ake kira Chakama, sai Sojan ya fitar da bindiga kirar AK47 ya harbi Malamin harbi uku ya kashe shi nan take, sai Sojan ya kira wani abokinsa Soja mai suna ADAMU GIDEON yana aiki a rundiar Recca Battalion 241 akan yazo ya tayashi tafiya da motar Malamin, cikin ikon Allah sai motar taki tashi, a haka akazo aka kamasu

Sojojin da s**a aikata wannan mummunan ta'addanci yanzu haka suna hannun hukumar Soji a garin Damaturu ana bincikarsu, sun tabbatar da cewa sun kashe Malamin ne kawai don su gudu da motarsa, abinda bincike kenan ya tabbatar ba barayi bane ko 'yan Boko Haram s**a kashe Malamin, sojoji ne kuma ba Musulmai ba إنا لله وإنا اليه راجعون

Yau inda wasu sojoji ne Musulmai barayi s**a hallaka wani Malamin addinin da ba na Musulunci ba, da yanzu labarin nan sai ya isa majalisar dinkin duniya

Muna kira ga Maigirma Gwamman jihar Yobe, kayi amfani da karfin ikonka kabi kadin jinin wannan Malami da wasu 'yan ta'addan sojoji s**a zubar, ba mu yarda a bar binciken sojojin a hannun rundinar soji ba

Anyi jana'izar Malamin jiya asabar, ya samu dunbin jama'ar Musulmi da s**a masa jana'iza tare da rakashi makwancinsa

Darasi anan shine, idan kana tafiya da mota ka kiyaye rage wa wanda baka sanshi ba hanya, musamman idan yana rike da jaka babba ko wani kaya, idan shi kadai ne zaka iya rage masa hanya, amma ka dubeshi da kyau, ka tabbatar a doke ba zai iya murdeka ba, sannan kar ka tsaya a wajen gari kace zaka saukar dashi

Muna rokon Allah Ya gafarta wa Malan.

Address


Telephone

+2348063084583

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when IDON AREWA 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to IDON AREWA 24:

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share