Yusuf Assalafiy

  • Home
  • Yusuf Assalafiy

Yusuf Assalafiy personal blog preaching

04/12/2024

WANI JINKIRIN ALKHAIRI NE 'YAR UWA.

Sau da yawa za ka samu mace ta kai wani mataki wanda ya kamata a ce ta yi aure amma har yanzu ba ta yi ba, age-mates ďinta sun yi aure wasu ma har da 'yaƴa, ita kuma bata yi ba, qin yin auren ba daga gare ta bane, itama tana so, sai dai kuma har yanzu Allah bai kawo mata mijin aure ba. 'Yar uwa wannan ba komai bane illa jarabawa daga Allah Mabuwayi, mai yiyuwa ya jarrabe ki ne domin Ya ga yadda za ki yi, idan kika yi hakuri kuma kika mayar da Al'amuranki ga Allah, sai ki ga Ya kawo maki miji adali mai addini da kyawawan dabi'u da dukkan siffofin da mace za ta bukata a wajen namiji ta hanyar da ba ki yi tsammani ba 'yar uwa.
Allah Shi ne Ya yi alkawarin zai jarrabi muminai a duniya da jarabawa iri-iri, kuma Ya ce Lallai a yi bushara ga masu hakuri. 'Yar uwa wani irin babban rabo k**e tunani Allah Ya tanadar maki idan kika kasance cikin masu hakuri.
Hakurin shi ne a kowane lokaci ki dinga jin Allah Yana son ki, kuma Yana sane da halin da k**e ciki, kada ki kai kukan Sa wajen bayin Sa, kuma ki kasance mai kiyaye iyakokin Sa, ki Tsare ganinki, jinki daga haramun kuma ki kiyaye al'aurarki, ki kare mutuncin kanki kuma kada ki tozartar da tarbiyyar da su Abba da Umma s**a ba ki, kada ki aikata abin da za su yi da-na-sanin zuwanki duniya, Sannan kada ki aikata abin da zai zama abin gorantawa ga Qannenki, 'yaƴanki da dukkan wanda yake da alaqa ta jini da ke! Ki bar tarihi mai kyau ko don gaba, kuma ki ji tsoron Allah ki dinga dubin abin da k**e aikatawa don gobe.
Da yawa daga cikin 'Yan mata kamilallu sun rasa kimarsu, inda suke tunanin mai yiyuwa sanya wadataccen hijabi da Niqabi ne ya jawo masu jinkirin aure, sai s**a koma yin shiga irin ta tsiraici da bayyana adonsu wai da sunan samun mijin aure. 'Yar uwa Wallahi arhar ta yi yawa, meyasa sai kin tallata kanki za ki samu mai aure, kin ta6a ganin wani abu mai daraja ana tallata shi, duk wani abu mai daraja rufe shi ake kuma a adana shi a mafi dacewar guri, shin a tunaninki tsinuwar Allah da ta malā'iku su za su yi maki jagoranci wajen neman mijin aure, ki watsar da wannan tunanin 'yar uwa. Ki killace kanki, ki ďauki kanki kamar sarauniya, Allah Masani ne a kan halin da k**e ciki, kuma Shi zai turo maki miji ďan asali mumini, domin su mata masu tarbiyya na maza masu tarbiyya ne, su kuwa lalatattu sai lalatattu irinsu.
Mata nawane s**a yi auren amma har yanzu ba su shaida daďinsa ba? Nawa ne s**a rabu da iyayensu s**a je gidan wani amma ya dinga azabtar da su, wata ma sai ta gwammace dama ba a haife ta ba. Ashe kun ga kenan yin auren ba shi ke tabbatar da natsuwa ba, sai an bi hanyar da Allahu da ManzonSa s**a tsara.
Ku kuma masu tsangwamar irin waďannan matan da cewa sun qi yin aure, ku ji tsoron Allah ku daina, ku sani kowa akwai irin Qaddararsa a rayuwa. Sai ku ji kawai an zauna ana firar wance ga Qannenta sun yi aure har da yara, amma ita ta tsaya sai.... Wallahi ku sani! Tafi kowa son ta yi auren, kuma iyayenta ma sun kosa su rabu da ita. To amma ya za su yi tunda haka Allah Ya tsara mata?
Allah ka ɗora mu akan abinda kake so kuma ka yarda dashi

السلام عليكمJan hankali na garemu mu Musulmi musamman mu da muke kiran kan mu Ahlis-Sunnah yakamata mu dunga lura da was...
21/09/2024

السلام عليكم

Jan hankali na garemu mu Musulmi musamman mu da muke kiran kan mu Ahlis-Sunnah yakamata mu dunga lura da wasu abubuwa duk yadda kake so al'umma ta gyaru kai idan baka gyara kanka ba to aikin banza ne
Kada mu dunga tuya muna mantawa da albasa idan ya kasance babbanakamin mu shine abinda Annabi baiyi ba a addini muna kallon sa bidi'a kuma mun yarda dukkanin bidi'a ɓata ce to dole mu ƙauracewa duk abinda babu nassi akai.
Kamar zaman makoki babu wanda ya isa ya kawo maka inda Annabi S. A. W yayi ko ɗaya daga cikin sahabbai har ma an samu hadithin da sahabi ya tabbatar da haramcin sa to koda da saɓani akai barirshi shi yafi alkhairi don kuɓutar da addinin mu

Babu abinda zai zama addini a yanzu wanda lokaci Annabi da sahabbai bai zama addini ba mu mun yarda Annabi S. A. W kafin yabar duniya ya sanar da mu dukkan komai hatta shiga bayi

Ita Ta'aziyya anayin tane a duk inda aka haɗu da mutum sawa'un gidan sane ko wajen kasuwancin sa ne ko wajen aikinsa ko kan hanya ko a masallaci duk ya halatta kayiwa mutum ta'aziyya.
Muna zuwa gidan ne saboda kun tare a can da baku a ƙofar gidan zamu biku duk inda kuke mu yi maku saboda ta'aziyya ibada ce Manzan Allah S. A. W a hadithin da ibn maaja ya ruwaito yace "BABU WANI MUMINI DAZAI YIWA DAN UWANSA TA'AZIYYAR WATA MUSIBA FACE ALLAH YA TUFATAR DASHI DA KAYAN ADO NA ALJANNA"
A hadithin da tirmizi ya ruwaito kuma Annabi S. A. W yace "WANDA YAYI TA'AZIYYA GA WANDA WATA MUSIBA TA SAMESHI YANA DA KWATANKWACIN LADAR SA(ma'abocin musibar)
Mu muna amsar tawili ne a idan babu nassi

Allah ka ɗora mu akan abinda kake so kuma ka yarda dashi

      HUKUNCIN ZAMAN MAKOKI    Babban Malami ibn ƙayyumul jauziyya almajirin shaikhul Islam ibn Taymiyya wanda ya rasu r...
21/09/2024



HUKUNCIN ZAMAN MAKOKI

Babban Malami ibn ƙayyumul jauziyya almajirin shaikhul Islam ibn Taymiyya wanda ya rasu ranar Alhamis 13 ga watan Rajab Hijira nada shekara 751 yau shekarar sa 695 da mutuwa ya faɗa a cikin littafin sa (Zaadul Ma'aad fiy Hadyi khairil Ibaad) a juzu'i na farko shafi na 214 a fasalin daya ɗaura

حكم التعزية و عدم الإحتماع لها
Ma'ana: Hukuncin ta'aziyya da barin haɗuwa domin ta

Sai yace; ya kasance daga cikin shiriyar sa(Mazan Allah S. A. W) yin ta'aziyya ga iyalan mamaci, amma baya cikin shiriyar sa Haɗuwar zaman makoki ko karantawa mamaci Alƙur'ani akan ƙabarinsa ko a wani waje daban.

Sai yace DUKA WANNAN BIDI'A NE Wadda aka ƙirƙira bayansa(S..A.W) kuma abin ƙyama ne a cikin addini.
Ya kasance daga cikin shiyar sa natsuwa da yarda da ƙaddarar Allah da godiya ga Allah da mayar da Al'amari gareshi, kuma ya barranta(S.A.W) ga wanda yake yaga tufafi saboda musiba, Ɗaga sauti da kururuwa da bugun jiki ko matan dake aske gashin kai.

Yace; ya kasance daga shiriyar sa kada iyalan mamaci su dafa abinci don mutane amma ya umarci mutane su dafa abinci su kawo ma iyalan mamaci, yace wannan yana daga cikin manyan kyawawan dabi'u da tausayawa ga iyalin mamaci saboda abinda ya shgaltar dasu na rashi.

Yace ;yana daga cikin shiriyar sa barin yin shelar mutuwa hasalima yayi hani akai, yana cewa YANA DAGA CIKIN AIKIN JAHILIYYA(yin shelar mutuwa).

Akwai wani Malami Sa'ad Yusuf Mahmud Abu Aziz mawallafin littafin (Alfiƙhul Miyassar wa adillatihi minan Ƙur'ani was sunna) yayi maganganu masu kyau akan zaman makoki, abinda yasa ban kawo su ba bani da tabbacin ko ya rasu ko yana raye saboda ina kawo maganganun salaf ne.

SAI KUMA TAMBIHI DA ZAN YI A ZAMA NA GABA IN ALLAH YASO.

YA ALLAH KA ƊORAMU AKAN ABINDA KAKE SO KUMA KA YARDA DASHI

HUKUNCIN ZAMAN MAKOKI A SHARI'A, A MAHANGAR SALAF        MENENE ZAMAN MAKOKI?; Shine zaman ds mutane suke a ƙofar gidan ...
20/09/2024

HUKUNCIN ZAMAN MAKOKI A SHARI'A, A MAHANGAR SALAF

MENENE ZAMAN MAKOKI?; Shine zaman ds mutane suke a ƙofar gidan mamaci ko wani waje daban, da niyyar duk wanda zai yi masu ta'aziyya ya riskesu anan.

Wsnnan abin ƙi ne kuma bidi'a ne baya da asali cikin addini, kamar yadda da yawa daga cikin magabata na ƙwarai s**a tafi akan haka.

Daga cikinsu akwai imamu zahabiy almajirin Ibn al-Qayyim wanda ya rusa hijira tana da shekara 748, yau shekararsa 708 da barin duniya, ya fada acikin littafin sa kitabul kabaa'ir shafi na 134 bayan ya kawo maganganun imamu nawawiy sai yace "an ƙyamaci zaman makoki, kamar mun tambaya menene zaman makoki? Sai yace shine iyalan mamaci su haɗu a wani gida ko wani wuri da nufin duk mai son yi masu ta'aziyya ya same su anan.

Sai kuma Imamu nasiruddinil Albaniy wanda ya rasu hijira na da shekara 1420 yau shekarar sa 26 da barin duniya ya faɗa a cikin littafin sa ahkamul janaa'iz a shafi na 167 (ga wanda yake da irin bugu na) yace "ya kamata mu ƙauracewa abubuwa guda wanda mutane suke bibiyar su
1. Haɗuwar zaman makoki a wani waje kamar gida ko maƙabarta ko masallaci
2.Dafa abinci daga gidan mutuwa ana fito dashi ga ƴan zaman makoki.
Sai ya kawo hadithin jareer bn Abdullah wanda Ahmad da Ibn Majah s**a ruwaito da isnadi ingantacce. Jareer bn Abdullah R. A yace "mu sahabbai mun kasance muna lissafa zaman makoki da kuma yin abinci a fito dashi a matsayin kukan mutuwa". Kuma mun sani Annabi S. A. W yace " MAI KUKAN MUTUWA BATA SHIGA ALJANNA"

SABODA LOKACI ZAN CI GABA A RUBUTU NA 2 MU ƘARO KODA MALAMAI 2 NE.

19/09/2024

Wani kam mu Salafawa Ahlis sunna ina muka samo zaman makoki idan anyi mana mutuwa,? Do Allah ayi mana bayanin yadda zaman makokin gidan Annabi ya kasance, yaya yayi zaman makokin ƴaƴansa da ƴan'uwasa? . Do Allah ina neman sani don naga har gidajen manyanmu anayi.

25/11/2023

HIRAR MUSAMMAN: Miji na yana kwashe watanni 9 zuwa 11 yana bacci bai farka ba, wani lokacin kuma idan Allah yasa ya farka, zai iya daukar wata daya, biyu zuwa uku yana yawace-yawacen sa a gari, kafin ya sake komawa bacci.

Shekaru 15 kenan muna fama da wannan lalurar.

23/11/2023

Da Guiwa za'a tafi Sujjada ko da Hannu?

Prof. Muhd Sani Umar R/Lemo

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIUN!Allah Yayiwa Sheikh Giro Argungu Rasuwa, Bayan Jinya Da Ya Samu A Daren Jiya, Bayan Ka...
06/09/2023

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIUN!

Allah Yayiwa Sheikh Giro Argungu Rasuwa, Bayan Jinya Da Ya Samu A Daren Jiya, Bayan Kammala Tafsir Magriba Zuwa Ishaa, Allah Yayi Maka Gafara Sheikh Amin..

Wednesday!
6th September, 2023.

15/08/2023

Address


Telephone

+2348161716529

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Yusuf Assalafiy posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Yusuf Assalafiy:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share