One News Hausa

  • Home
  • One News Hausa

One News Hausa WhatsApp: 08064672794
(3)

ONE NEWS HAUSA Jarida ce dake kawo muku labarai da ɗumi-ɗumi gami da rahotannin gida da na waje a cikin harshen Hausa, daga Kamfanin 5STARS MEDIA PRODUCTION.

-Aikin mu domin al'umma ne.
-Burinmu kasancewa ji da ganin al'umma.

Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya ce gwamnatinsa ta aiwatar da kashi 85 cikin 100 na alkawuran da ta dauka wa al’...
18/07/2025

Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya ce gwamnatinsa ta aiwatar da kashi 85 cikin 100 na alkawuran da ta dauka wa al’ummar jihar, inda ya rage kashi 15 cikin 100 yayin da yake shiga shekara ta biyu na wa’adin mulkinsa na farko.

Daily Trust ta rawaito cewa gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da ya ke rantsar da sabon Shugaban Ma’aikata na Jihar, Dr Sulaiman Wali Sani; Darakta Janar na Hukumar Ayyuka na Musamman, Manjo Janar Sani Muhammad (mai ritaya), da kuma Masu Ba da Shawara na Musamman guda 11, a ranar Alhamis.

Ya bayyana cewa wannan nasara ta kasance sak**akon tantancewar da aka yi kan ayyukan gwamnatinsa a cikin shekaru biyu da s**a gabata.

“Na yi farin ciki cewa makon da ya gabata lokacin da na duba wuraren da muka samu kuri’a a zabe, duk alkawuran da muka yi wa jama’a, a cikin shekaru biyu mun aiwatar da kashi 85 cikin 100. Don haka, yanzu ya rage mana kashi 15% kawai da za mu aiwatar cikin shekaru biyu masu zuwa, insha Allah,” in ji shi.

“Mun gabatar da wannan batu a gaban Majalisar Zartaswa ta Jihar. Mun dubi yadda abubuwa ke gudana kuma muna da shekaru biyu a gaba. Don haka za mu duba hanyoyin da za mu tabbatar da cika wannan kashi 15%,” inji shi.

Gwamna Yusuf ya kara da cewa gwamnatinsa ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kawo sababbin tsare-tsare da shirye-shirye domin kara tasiri a rayuwar al’ummar jihar Kano.

“Muna kawo sababbin shirye-shirye da ayyuka wadanda, da yardar Allah (SWT), za su ci gaba da inganta rayuwar al’ummar jihar. Kuma ba za mu iya yin hakan mu kadai ba; dole ne mu hada kai da ku duka,” in ji shi.

Sanarwar da Gwamnatin Jihar Kano ta fitar wadda ke dauke da sa hannun mai magana da yawun Gwamna, Sunusi Bature ya fitar...
18/07/2025

Sanarwar da Gwamnatin Jihar Kano ta fitar wadda ke dauke da sa hannun mai magana da yawun Gwamna, Sunusi Bature ya fitar yace, shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai kawo ziyayarar ta'aziyya na Marigayi Alhaji Aminu Dantata wanda ya rasu a baya bayan nan.

Sanarwar ta kuma bukaci alu'mmar Jihar Kano da su kasance masu karamci k**ar yadda s**a saba wajen nuna dattaku ga karbar bakuncin shugaban kasar a yau Juma'a.

Amma a gefe guda an ruwaito tsohon Gwamnan Kano kuma tsohon shugaban Jam'iyyar APC ta Kasa, Umar Abdullahi Ganduje ya ce zuwan na shugaban kasa a Jarida s**a gani, domin ba a sanar da su ba.

Me zuku ce?

DA DUMI DUMI: Iyalan Marigayi Janar Buhari Za Su Rika Karban Albashi 300,000 Duk Wata.A yunkurin gwamnatin tarayya na ky...
17/07/2025

DA DUMI DUMI: Iyalan Marigayi Janar Buhari Za Su Rika Karban Albashi 300,000 Duk Wata.

A yunkurin gwamnatin tarayya na kyautata goben iyalan Marigayin tsohon Shugaban Ƙasa Janar Buhari, gwamnatin tarayya zata rika bawa iyalan nasa naira dubu dari uku duk wata tare da basu alawi-alawi naira dubu dari biyu da hamsin duk karshen shekara, za a gina masu gida daya a duk In da su ke so a fadin Najeriya gwamnati zakuma ta basu motoci uku.

Bugu da kari gwamnatin tarayya zata bawa Iyalan tsohon Shugaban Ƙasar jami'an tsaro guda hudu, biyu 'yan sanda biyu na farar kaya, sannan za a rika fita dasu yawon bude ido duk shekara, bihasali tare da duba lafiyar su kyauta tun daga gida Najeriya har wajen kasar.

Shin ko menene ra'ayoyin ku game da matakan da gwamnatin tarayya ta dauka kan iyalan Marigayin?

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da sauya sunan Jami’ar Maiduguri zuwa Jami’ar Muhammadu Buhari (Muhammadu Buhar...
17/07/2025

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da sauya sunan Jami’ar Maiduguri zuwa Jami’ar Muhammadu Buhari (Muhammadu Buhari University) domin girmama tsohon Shugaban Ƙasa, marigayi Janar Muhammadu Buhari (rtd), GCFR.

Shugaban Ƙasa ya bayyana wannan mataki ne a yau, yayin wani zaman musamman na Majalisar Zartarwa ta Tarayya, wanda aka shirya domin marigayin, wanda ya rasu a birnin London, Birtaniya.

Shugaba Tinubu ya ce wannan girmamawa ce ta musamman domin tunawa da gudummawar da marigayin ya bayar wajen ci gaban ilimi, tsaro da zaman lafiya a Najeriya, musamman a Arewa maso Gabas inda matsalar tsaro ta daɗe tana addabar al’umma.

Ya ce Jami’ar Maiduguri ta taka rawar gani wajen ilimantar da dubban ɗalibai daga sassa daban-daban na ƙasa, kuma sauya sunan ta zuwa Jami’ar Muhammadu Buhari zai kasance tarihi da tunatarwa ga sabbin ƙarni na dalibai da malamai game da sadaukarwa da kishin ƙasa da marigayin ya nuna.

Zaman majalisar ya gudana cikin yanayi na tausayi da alhini, inda mambobin majalisar s**a bayyana irin kyawawan halayensa da saukin kai, da kuma jajircewar sa wajen hidimar ƙasa.

Yadda farashin buhun masara, dawa shinkafa, ke ci gaba da zaftarowa kasa a kasuwar hatsi ta DamdumeGa Yadda Sabon Farash...
17/07/2025

Yadda farashin buhun masara, dawa shinkafa, ke ci gaba da zaftarowa kasa a kasuwar hatsi ta Damdume

Ga Yadda Sabon Farashin Kayan Amfanin Gona A Kasuwar Hatsi Dake Karamar Hukumar Dandume Jihar Katsina Ranar Laraba 16/07/2025

1. Farar Masara Buhu 100kg ₦38,000 zuwa ₦48,000

2. Jar Masara Buhu 100kg ₦42,000 zuwa ₦48,000

3. Jar Dawa Buhu 100kg ₦40,000 zuwa ₦44,000

4. Farar Dawa Buhu 100kg ₦44,000 zuwa ₦46,000

5. Dauro/Gero Buhu 100kg ₦60,000 zuwa ₦63,000

6. Waken Hausa Buhu ₦95,000 zuwa ₦105,000.

7. Oloyin/iron/Dan amarya/Iron 100kg
₦105,000 zuwa ₦110,000.

8. Waken Soya Buhu 100kg ₦76,000 zuwa ₦82,000

9. Tsabar Shinkafa Buhu 110kg ₦100,000 zuwa ₦120,000

10. Gyaɗa buhu 100kg ₦150,000 zuwa ₦180,000

11. Barkono danminci Buhu 100kg ₦260,000 zuwa ₦300,000

12. Barkono Zamfara 100kg ₦120,000 zuwa ₦160,000

13. Barkono danmiyare 100kg ₦70,000 zuwa ₦90,000

14. Samfarerar Shinkafa Buhu ₦35,000 zuwa ₦45,000

15. Kalwa Buhu 100kg ₦130,000 zuwa ₦140,000

16. Kashin Rogo (Dry Cassava) Buhu 100kg ₦40,000 zuwa ₦50,000

17. Alk**a Buhu 100kg ₦50,000 zuwa ₦70,000

18. Kubewa busassa 100kg ₦??? zuwa ₦???

19. Busasshen Tumatur ₦??? zuwa ₦???

Rahoto Daga: Bashir Muhammad Bugash
Katsina Daily News

Babban limamin cocin Roman Katolika na Katsina Rev. Gerald Mamman Musa ya roka ma Buhari neman afuwa, a lokacin da ya ha...
17/07/2025

Babban limamin cocin Roman Katolika na Katsina Rev. Gerald Mamman Musa ya roka ma Buhari neman afuwa, a lokacin da ya halarci gidan tsohon shugaban kasar dake Daura, inda Sheikh Pantami da Yusuf Buhari s**a tarbe shi.

—Katsina Daily

YANZU-YANZU: Daga ƙarshe, Barista Abba Hikima, da Dan Bello sun maka gwamnatin Tarayya kotu kan zargin kin biyan ma'aika...
17/07/2025

YANZU-YANZU: Daga ƙarshe, Barista Abba Hikima, da Dan Bello sun maka gwamnatin Tarayya kotu kan zargin kin biyan ma'aikatan N-power haƙƙoƙansu da suke bi na sama da watanni takwas

Wane bangare za su so ya yi nasara a wannan shari'ar bangare su Dan Bello, ko bangare gwamnati da ake zarginsu da rike kudaden?

Shugaban Izala ɓangaren Jos, Shaikh Sani Yahya Jingir ya jagoranci tawagar da ta ziyarci ƙabarin tsohon shugaban ƙasa Mu...
17/07/2025

Shugaban Izala ɓangaren Jos, Shaikh Sani Yahya Jingir ya jagoranci tawagar da ta ziyarci ƙabarin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, tare yi masa addu'a da kuma yi wa iyalansa ta'aziyya da jaje a garin Daura da ke jihar Katsina.

Kenan ziyarar Kabari ba shirka ba ne, haka gini akan kabarin ma?

JIGA–JIGAN ƘUNGIYAR IZALA ZUN ZIYARCI ƘABARIN MARIGAYI BUHARIMalaman Ƙungiyar Izala ta ƙasa baki ɗaya, karkashin jagoran...
17/07/2025

JIGA–JIGAN ƘUNGIYAR IZALA ZUN ZIYARCI ƘABARIN MARIGAYI BUHARI

Malaman Ƙungiyar Izala ta ƙasa baki ɗaya, karkashin jagorancin Sheikh Bala Lau, sun ziyarci gidan Buhari dake Daura inda s**a je har inda ƙabarinsa yake don yi masa addu'a.

A baya dai Ƙungiyar Izala sun kasance masu adawa da Ziyarar Maƙabarta ko Ƙabari, su kan ƙira masu yi da "Mushrikai", amma sai gashi a yau zun ziyarci Ƙabari tare da yin addu’o'i.

Me zaku ce?

DA ƊUMI-ƊUMI: Sojoji sun kashe wasu ’yan bindiga a FilatoRundunar sojoji ta 3 Division/Operation Safe Haven sun kashe wa...
17/07/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Sojoji sun kashe wasu ’yan bindiga a Filato

Rundunar sojoji ta 3 Division/Operation Safe Haven sun kashe wasu ’yan bindiga biyu tare da ƙwato mak**ai da alburusai a Jihar Filato.

—Jaridar Aminiya

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kano ta tabbatar da cafke ɗalibai 11 na makarantar Government Boarding Secondary School, Bich...
17/07/2025

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kano ta tabbatar da cafke ɗalibai 11 na makarantar Government Boarding Secondary School, Bichi, bisa zargin hannu a kisan wasu ɗalibai biyu a cikin makarantar.

Mai magana da yawun rundunar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da hakan a wata saƙo da ya aike wa jaridar Punch a yau Alhamis.

Ya bayyana cewa an k**a ɗaliban ne domin tambayoyi da bincike kan yadda lamarin ya faru da kuma matsayin kowanne daga cikinsu a cikin wannan aika-aika.

Rahotanni sun nuna cewa waɗanda aka kashe, Hamza Idris Tofawa da Umar Yusuf Dungurawa, sun rasu ne sak**akon harin da wasu ɗalibai s**a kai musu da wasu ƙarafa da ake kira “Gwale-Gwale”.

A baya, Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Dr. Ali Haruna Makoda, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan kisan ɗaliban.

—Daily Nigerian Hausa


Shugaba Bola Tinubu zai jagoranci taron addu'a ga marigayi tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a fadarsa ta A*o Rock d...
17/07/2025

Shugaba Bola Tinubu zai jagoranci taron addu'a ga marigayi tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a fadarsa ta A*o Rock da ke Abuja a ranar Alhamis.

Shugaban ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da Ma'aikatar Yaɗa Labarai ta fitar, in da ya ce za a gudanar da taron ne da ƙarfe 5:00 na yamma.

Kazalika ya ce zai gudanar da addu'o'in ne tare da kafatanin ministocinsa da shugabannin Majalisar Dokoki ta Kasa da wakilai daga ɓangaren shari'ar ƙasar.

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when One News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to One News Hausa:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share