Rahma TV

Rahma TV RAHMA TELEVISION FARIN CIKIN AL'UMMA. RADIO AND TV STATIONS

Domin aiko da abubuwan dake faruwa a inda kuke- 08100335970 , 07017233284
Domin samun sahihan labarai da shirye shirye kasance da Rahma TV da Rahma Radio 97.3FM dake Facebook da YouTube ko website a www.Rahma Tv.com

Shugaba Trump ya ce daga ranar Laraba, kamfanonin samar da magunguna da ke shigar da su kasar za su fuskanci harajin kas...
26/09/2025

Shugaba Trump ya ce daga ranar Laraba, kamfanonin samar da magunguna da ke shigar da su kasar za su fuskanci harajin kashi 100 cikin 100 matsawar basu fara samar da masana'antunsu ba Amurka.

Manazarta sun yi imanin cewa harajin zai cutar da ƙasashe irin su Ireland, wacce ta fi kowace kasa fitar da magunguna zuwa Amurka.

Trump ya kuma ba da sanarwar ƙarin haraji kan kayayyaki daban- daban tun daga manyan manyan motoci zuwa kayan kicin da na daki da sauransu.

Hakan na kunshe ne, a cikin sanarwar da Hukumar ta fitar, inda sanarwar ta ce, ana kuma sa ran hako ganguna Man Fetur sa...
26/09/2025

Hakan na kunshe ne, a cikin sanarwar da Hukumar ta fitar, inda sanarwar ta ce, ana kuma sa ran hako ganguna Man Fetur sama biliyan 1 da kuma wasu ganguna biliyan 5 na Iskar Gas. Sanarwar ta kara da cewa, ana kuma sa ran hako ganguna 591,000 na Man a kullum da kuma wasu ganguna 2 na Iskar Gas.

Hakan zai kuma kara sanya burin da ake da shi, na samar da sarrafa ganguna miliyan uku na danyen Mai Komolafe wanda ya bayyana hakan a wani taro mako na Mai na Afrika da ya gudana a babban birnin Accara na kasar Ghana, ya kara nuna kokarin da gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu ke ci gaba da yi, na cimma kuurin da gwamnatinsa ta sanya a gaba.

Gwamna Abba kabir yusuf ya bada umarnin mika batun ga majalisar shura ta jihar kano domin nazarin korafe-korafen tare da...
26/09/2025

Gwamna Abba kabir yusuf ya bada umarnin mika batun ga majalisar shura ta jihar kano domin nazarin korafe-korafen tare da baiwa gwamnati shawara akai. Mai magagana da yawun ofishin sakataren gwamnatin kano Musa Tanko, ya bayyana cewa kungiyoyin da dama ne s**a shigar da koken daga bangarorin dariku daban-daban, yace gwamnati tariga ta mika batun ga kwamitin shura daya kunshi manyan malaman jihar kano.

Sakataren gwamnatin kano Umar Faruk Ibrahim yace suna da niyar tabbatar da zaman lafiya, hadin kai da mutunta juna tsakanin kungiyoyin addinai a jihar nan. Wakilinmu a fadar gwamnatin kano, Tukur S Tukur ya rawaito cewa lamarin ya samo asali ne tun a larabar data gabata biyo bayan zanga- zangar wasu matasa da s**a mikawa gwamnati korafin a rubuce.

Janye yajin aikin yazo ne sak**akon wani taron gaggawa tsakanin kungiyar da manayan jami'an kungiyar dake da jibi da lan...
26/09/2025

Janye yajin aikin yazo ne sak**akon wani taron gaggawa tsakanin kungiyar da manayan jami'an kungiyar dake da jibi da lantarki da kamfanonin samar da lantarki da kamfanin tattara wutar na kasa da ma'aikatar mak**ashi inda aka cimma yarjejeniya akan bukatun ma'aikatan.

Ministan dai ya samu wakilcin daraktan rarraba wuta na ma'aikatar, matsayar da aka cimma ita ce fara biyan bukatun ma'akatan daga watan oktoba mai k**awa.

Kamfanin Dillancin Labaran Kasar nan ya bayar da rahoton cewa, fitar da kudaden wani shiri ne na Tallafin Kudi da nufin ...
26/09/2025

Kamfanin Dillancin Labaran Kasar nan ya bayar da rahoton cewa, fitar da kudaden wani shiri ne na Tallafin Kudi da nufin bunkasa ilimin yara mata a jihar Sokoto. An bukaci wadanda s**a ci gajiyar tallafin da iyalansu da su tabbatar da yin amfani da kudaden ta hanyar zuwa makaranta da kuma maida hankali kan karatu a nan gaba.

A nata jawabin, shugabar kungiyar ta AGILE ta kasa, Mr Fatima Buba- Haruna, ta ce shirin na CCT wani muhimmiyar dabara ce na AGILE don bunkasa riko, da mika yara mata a makarantun sakandire na gwamnati. Buba-Haruna ya bayyana fatan cewa shirin na CCT zai samar da fa'ida ta dogon lokaci da kuma kawo sauyi ga rayuwar mata a jihar .

Rahotanni sun bayyana cewa yaran, anyi garkuwa da su a ranar Talatar data gabata, daga baya aka tsinci gawarsu a cikin m...
26/09/2025

Rahotanni sun bayyana cewa yaran, anyi garkuwa da su a ranar Talatar data gabata, daga baya aka tsinci gawarsu a cikin motar mahaifinsu da daddare. Mahaifin yaran, Babagana Zanna Jaridama, wanda aka fi sani da bayyana ra’ayi a shafukan sada zumunta, inda ya ce kisan na da alaka da wani rubutu da ya yi a kwanakin baya, inda ya zargi wasu ‘yan siyasa da yin zagon ƙasa ga Gwamna Babagana Zulum.

Jaridama ya tabbatar da cewa ya kai lamarin ga ‘yan sanda, tare da bukatar a gudanar da bincike domin a tabbatar da adalci. Ya kuma ce an kai gawar yaran asibiti domin a gudanar da binciken
likita. Haka zalika kuma anyi Kokarin jin ta bakin mai magana da yawun ‘yan sanda na jihar Borno, ASP Nahum Kenneth Daso, amma hakan bai samu ba, domin bai amsa waya ko sakon da aka aike masa ba.

Rahotanni sun bayyana cewa jami'an tsaro ne tare da hadin gwiwar 'yan sa kai ne s**a gudanar da samame karkashin jagoran...
26/09/2025

Rahotanni sun bayyana cewa jami'an tsaro ne tare da hadin gwiwar 'yan sa kai ne s**a gudanar da samame karkashin jagorancin jami'ain offishin mai bawa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro tare da 'yan sanda. Jami’an tsaron sun kai samame maboyar ‘yan bindigar, inda aka yi musayar wuta mai tsanani,Wanda ya tilasta wa ‘yan ta’addan tserewa tare da barin mutanen da s**a sace.

A cewar rundunar ‘yan sanda, dan sa-kai da ya samu rauni a yayin arangamar amma yana samun sauki a asibiti. Kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Kwara, SP Adetoun Ejire-Adeyemi, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce an kwato babura guda uku da kuma harsashin bindiga kirar AK-47 guda tara daga hannun ‘yan bindigar.

Daraktan yada labarai na tsaro, Manjo Janar Markus Kangye, ne ya tabbatar da hakan yayin ganawa da manema labarai a birn...
26/09/2025

Daraktan yada labarai na tsaro, Manjo Janar Markus Kangye, ne ya tabbatar da hakan yayin ganawa da manema labarai a birnin Abuja,inda ya ce wannan aiki ya gudana ne tsakanin ranar 14 zuwa 22 ga watan Satumba a dukkan sassa na ƙasar. A Arewa maso Gabas, dakarun Operation Hadin Kai sun kubutar da mutane uku, sun kuma cafke abokan hulɗar ’yan ta’adda ashirin da shida tare da kashe mayakan Boko Haram da ISWAP a jihohin Borno, Yobe da Adamawa.

A Arewa maso Yamma, dakarun Operation Fansan Yamma sun kubutar da mutane goma sha huɗu, sun hallaka ’yan ta’adda a jihohi biyar tare da k**a fitaccen ɗan ta’adda Mallam Abubakar Ahmadu da wasu abokanansa guda shida. A Arewa ta Tsakiya kuwa, Operation Enduring Peace ta k**a mutum hamsin da biyu a Jihar Filato da Kaduna, tare da ceto mutane tara, yayin da Operation Whirl Stroke ta kubutar da wasu mutane takwas a jihohin Benue, Taraba, Kogi, Nasarawa da Abuja, inda aka cafke shahararren mai garkuwa da mutane, Saawuan Wuaiyolna.

26/09/2025

KANUN LABARAI

Shugaba Tinubu Ya Jaddada Kudirin Gwamnatinsa Na Gyara Fannin
Lafiya Da Wutar Lantarki.

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rage Hayakin Da Filin Jirgin Sama Na
Abuja Ke Fitarwa.

A kalla yara goma ne s**a rasa rayukansu sak**akon bullar cutar
mashako a jihar Naija.

KETARE
Gwamnatin Kasar Indonesia ta sanar da mutuwar mutane goma
sak**akon mummunar ambaliyar ruwa da ta mamaye tsibiran Bali da
Flores.

LARABA
18 RABI’UL AWWAL
10 SEPTEMBER 2025

Tsohon gwamnan Kano kuma jagoran jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ya musanta rahotannin da ke yawo a shafukan sada ...
26/09/2025

Tsohon gwamnan Kano kuma jagoran jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ya musanta rahotannin da ke yawo a shafukan sada zumunta da ke cewa ya tura takardar neman shiga wata jam’iyyar siyasa a ƙasar.

Ya bayyana cewa labarin ba gaskiya ba ne, yana mai jaddada cewa ba su nemi shiga wata jam'iyya ba.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake yaɗa jita-jita cewa Kwankwaso da tawagarsa na shirin komawa jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na X, Kwankwaso ya ce: “Mun samu labarin wasu jita-jita a shafukan sada zumunta cewa mun gabatar da takardar niyyar shiga wata jam’iyyar siyasa a ƙasar. Muna so mu fayyace cewa ba mu gabatar da irin wannan bukata ga kowace jam’iyya ba.”

Sanarwar ta kara da cewa irin waɗannan rahotanni na bogi ba su da wata manufa face rikita jama’a da kuma yaɗa ƙarya..

“Jama’a su yi hattara da irin waɗannan labarai na bogi da ake yadawa don daukar hankalin mutane kawai,” in ji Kwankwaso.

Kwankwaso ya kuma shawarci jama’a da su ci gaba da bibiyar sahihan bayanai daga ofishinsa da hanyoyin sadarwa na hukuma.

Da aka tambaye shi ko bai gamsu da kamun ludayin gwamnatin Kano ta yanzu, sai Ganduje ya ce "ai ba ma su da ludayin ball...
26/09/2025

Da aka tambaye shi ko bai gamsu da kamun ludayin gwamnatin Kano ta yanzu, sai Ganduje ya ce "ai ba ma su da ludayin ballantana ma a k**a. Gwamnatin ƴan bandan-bandan ce. Gwamnatin masu kame-kame."

"To ita gwamnati tana da nasarori da rashin nasarori. To amma ita wannan gwamnatin ba ta da nasarori ne irin waɗanda ake kira cigaban mai haƙar rijiya saboda irin facaka da suke yi da irin yawan kuɗin da ake kashewa kan ayyukan da suke cewa suna yi.

Babu shakka idan an yi aiki misali k**ar an gina gada ai cigaba ne to amma idan ka duba irin kuɗin da suke kashewa to da talakawa za su iya cewa ma ba sa son gadar saboda yawan kuɗin da aka kashe."

A ranar Alhamis ne tsohon shugaban jam'iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje da sauran jiga-jigan jam'iyyar na Kano ...
26/09/2025

A ranar Alhamis ne tsohon shugaban jam'iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje da sauran jiga-jigan jam'iyyar na Kano s**a gudanar da wani taro irinsa a karon farko a tsawon lokaci.

Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibril da sauran shugabannin jam'iyya na ƙananan hukumomi.

Abdullahi Ganduje ya ce sun shirya taron ne domin ƙara ɗinke jam'iyyar da yin kandagarki dangane da rigingimu ka iya taso mata a nan gaba.

Sai dai kuma majiyoyi na cewa an shirya taron ne da manufar yin kandagarki dangane da raɗe-raɗin da ake yi na komawar tsohon gwamnan jihar, Rabi'u Musa Kwankwaso zuwa jam'iyyar ta APC

Address

Kano

Telephone

+2348023724111

Website

http://www.youtube.com/@rahmaTv1

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Rahma TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Rahma TV:

Share