Dandalin Masu Sauraron Radio

  • Home
  • Dandalin Masu Sauraron Radio

Dandalin Masu Sauraron Radio Muna kawo labaran da s**a shafi Aikin jarida cikin Harshen Hausa zalla. Muna maraba da shawarwarin ku
(3)

Tsohon fitaccen ma'aikacin BBC, Ibrahim Isa, ya buƙaci a kai zuciya nesaIbrahim Isa ya bayyana hakan ne ta cikin wani ru...
24/07/2025

Tsohon fitaccen ma'aikacin BBC, Ibrahim Isa, ya buƙaci a kai zuciya nesa

Ibrahim Isa ya bayyana hakan ne ta cikin wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook, bayan ce-ce-ku-cen da ya barke kan tsangwama da kyara da wasu tsoffin ma'aikatan BBC Hausa s**a ce sun fuskanta daga abokin aikinsu lokacin da suke aiki a gidan rediyon.

A cewar Ibrahim, BBC gida ne da ya gina zumunci da haɗin kai tsakanin ma’aikata, kuma da dama sun amfana da zaman su a can ta fannoni da dama, ciki har da ɗaukaka da samun masoya. Ya ce yana jin takaici matuƙa da yadda cece-ku-ce ke ci gaba da yawo kan al’amarin, yana mai jaddada cewa ya kamata a saurari ɓangarori biyu kafin a ɗora laifi.

Ya ƙara da cewa akwai bukatar tsoffin ma’aikata da ke jin bacin rai su daure, su rungumi yafiya da juriya, domin a cewarsa, fusata da bayyanar da ɓacin rai a fili ba shi ne mafita ba. Ya yi kira da a daina cin mutunci da ɓata suna, yana mai jan hankali kan muhimmancin ci gaba da sada zumunci da mutunta juna.

Ku bayyana ra'ayoyinku...

Tsohon ma’aikacin BBC Hausa, Jabir Mustapha Sambo, ya ce kalaman Halima Umar Saleh kan tsangwama da cin zarafi a wurin a...
24/07/2025

Tsohon ma’aikacin BBC Hausa, Jabir Mustapha Sambo, ya ce kalaman Halima Umar Saleh kan tsangwama da cin zarafi a wurin aiki gaskiya ce tsagwaronta, yana mai cewa shi ma ya fuskanci irin wannan daga wani ma’aikaci kafin ya yanke shawarar barin aiki da tashar.

Jabir ya bayyana hakan ne ta cikin wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook inda ya ce ya daɗe yana jurewa matsin lamba da rashin kwanciyar hankali da ya ke fuskanta daga wani mutumi a wurin aiki, wanda hakan ya haifar masa da ciwon damuwa da har ya kai shi yanke shawarar ajiye aiki.

Wannan martani na Jabir na zuwa ne bayan hirar da Halima Umar Saleh ta yi da Arewa24, inda ta bayyana cewa daga cikin dalilan barinta aikin BBC Hausa, akwai tsangwama daga wani abokin aikinta.

Lamarin ya ƙara jawo ce-ce-ku-ce daga jama’a da dama, ciki har da tsofaffin ma’aikatan tashar da s**a tofa albarkacin bakinsu kan irin ƙalubalen da s**a fuskanta a lokacin da s**a yi aiki da kafar.

Ku bayyana ra'ayoyinku...

AREWA24 ZA TA MAIMAITA HIRAR HALIMA UMAR SALEHTashar talabijin ta AREWA24  za ta maimaita fitacciyar hirar da ta yi da t...
23/07/2025

AREWA24 ZA TA MAIMAITA HIRAR HALIMA UMAR SALEH

Tashar talabijin ta AREWA24 za ta maimaita fitacciyar hirar da ta yi da tsohuwar ma’aikaciyar BBC Hausa, Halima Umar Saleh, wadda ke ɗauke da bayani mai zafi game da ƙalubalen da ta fuskanta a lokacin da take aiki da sashen Hausa na BBC da ƙarfe shida na yammacin yau.

A cikin hirar da aka haska da safiyar yau Laraba ta cikin fitaccen shirin nan na Gari Ya Waye, Halima ta bayyana yadda ta sha fama da tsangwama da barazana daga wani abokin aikinta, lamarin da ya taimaka wajen yanke shawarar barin aikinta a BBC.

Sai dai bayan haska hirar ne kuma, aka fara ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, har ma rahotannin cewa tashar ta Arewa24 ta goge bidiyon tallar hirar daga shafukanta na sada zumunta, abin da ya janyo fargaba da tambayoyi daga masu kallo.

Yanzu dai za a maimaita cikakken shirin, tare da bai wa masu kallo dama su sake kallon hirar da ke ɗauke da bayani mai muhimmanci da ya tada kura a kafafen sada zumunta.

Tsohuwar ma’aikaciyar BBC Hausa, Halima Umar Saleh, ta bayyana cewa ta sha fama da tsangwama da kyara yayin da take aiki...
23/07/2025

Tsohuwar ma’aikaciyar BBC Hausa, Halima Umar Saleh, ta bayyana cewa ta sha fama da tsangwama da kyara yayin da take aiki a BBC Hausa.

Halima ta bayyana hakan ne ta cikin wata tattaunawa da ta yi da gidan talabijin na Arewa24.

A cewarta, wani abokin aiki ya taba yi mata barazana har da cewa zai sa a kore ta daga aiki, duk da cewa ya amince tana yin aikinta yadda ya kamata.

Halima ta ce irin waɗannan ƙalubalen da ta fuskanta ne s**a taimaka wajen yanke shawarar barin BBC.

A yayin da tattaunawar ta ci gaba da janyo martani a shafukan sada zumunta, wasu tsofaffin ma’aikatan BBC Hausa ma sun bayyana irin abubuwan da s**a fuskanta a lokacin da suke aiki da kafar.

Mohammed Sani Aliyu ya bayyana cewa shi ma ya bar aikin ne "saboda yadda wurin ya koma muhalli mai cike da matsin lamba da da rashin jin daɗi”, yana mai kira da a gudanar da bincike kan yadda ake tafiyar da ɓangaren gudanarwar sashen Hausa na BBC.

Ita kuwa Fauziyya Kabir Tukur ta ce lokaci ya yi da za a karkata hankali kan halin da ma’aikatan ke ciki, tana mai danganta sauke bidiyon da Arewa24 ta yi da yiwuwar akwai gaskiya a korafin Halima.

Tuni dai wasu daga cikin masu sauraron tashar ta BBC s**a rubutawa shalkwatar tashar dake birnin Landan ƙorafi dangane da batun, tare da neman a gudanar da bincike a kai.

📌 Shin a wurin aikinku kun taɓa fuskantar irin wannan matsin lamba ko tsangwama?

🕒 Ƙarfe 3:00 na rana agogon Najeriya 🇳🇬, Nijar 🇳🇪, Kamaru 🇨🇲 da Chadi 🇹🇩🕑 Ƙarfe 2:00 na rana agogon T.U da Ghana 🇬🇭🎙️ Sa...
20/07/2025

🕒 Ƙarfe 3:00 na rana agogon Najeriya 🇳🇬, Nijar 🇳🇪, Kamaru 🇨🇲 da Chadi 🇹🇩
🕑 Ƙarfe 2:00 na rana agogon T.U da Ghana 🇬🇭

🎙️ Sashin Hausa na DMS Radio ke magana...

Daga ina ku ke tare da mu?

Yadda Hauwa Halliru Gwangwazo Ta Ɗauki Hankalin Ƴan Arewa a Kafafen Sada ZumuntaA 'yan kwanakin nan, Hauwa Halliru Gwang...
19/07/2025

Yadda Hauwa Halliru Gwangwazo Ta Ɗauki Hankalin Ƴan Arewa a Kafafen Sada Zumunta

A 'yan kwanakin nan, Hauwa Halliru Gwangwazo, wadda ke gabatar da labarai a RFI Hausa, ta jawo hankalin masu amfani da kafafen sada zumunta.

Wannan na zuwa ne sakamakon yadda take karanta labarai cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, abin da ke daukar hankalin masu sauraro da kallo.

Yayin da wasu s**a maida batun abin raha, wasu kuma sun duƙufa wajen wallafa hotuna da bidiyoyinta domin samun ƙarin mabiya a shafukansu na Facebook.

Hauwa Gwangwazo dai na cikin yan jaridu masu nasibi da ta samu ɗaukaka cikin kankanin lokaci da fara aikinta.

Ku bayyana ra'ayoyinku...

Shafin Dandalin Masu Sauraron Radio ya samu mabiya dubu 103 a TikTokShafin Dandalin Masu Sauraron Radio da ke wallafa la...
18/07/2025

Shafin Dandalin Masu Sauraron Radio ya samu mabiya dubu 103 a TikTok

Shafin Dandalin Masu Sauraron Radio da ke wallafa labarai da bayanai kan gidajen rediyo da talabijin a Arewacin Najeriya, ya cika mabiya dubu 103 a dandalin TikTok.

Shafin ya zama ɗaya daga cikin manyan hanyoyin da matasa ke amfani da su wajen samun sahihan bayanai da abubuwan ban sha’awa da s**a shafi kafafen yaɗa labarai na yankin.

A cikin wata sanarwa da masu kula da shafin s**a fitar, sun nuna godiya ga masu bibiyar su bisa irin goyon bayan da suke samu, tare da alƙawarin ci gaba da kawo abubuwan da za su amfani jama’a.

Sun ce wannan ci gaba da aka samu ba nasu kaɗai ba ne, nasara ce ta hadin kan al’umma da ke ganin muhimmancin irin wannan dandalin da ke haskaka ayyukan kafafen rediyo da talabijin, da ma ma’aikatansu.

Dandalin, wanda ya shahara wajen kawo bayanai na cikin gida da kuma labarai masu ɗaukar hankali, ya fara ne da niyyar kawo sauyi a fahimtar al’umma game da aikin kafafen yaɗa labarai a yankin na Arewacin Najeriya.

Ku bayyana ra'ayoyinku...

An naɗa Nasiru Abbas Babi a matsayin mai riƙon shugabancin sabuwar tashar Iconic FM Sokoto.Hukumar gudanarwar sabon gida...
16/07/2025

An naɗa Nasiru Abbas Babi a matsayin mai riƙon shugabancin sabuwar tashar Iconic FM Sokoto.

Hukumar gudanarwar sabon gidan rediyo na Iconic FM 104.5 da ke Sakkwato ta naɗa Nasiru Abbas Babi a matsayin mai riƙon shugabancin tashar a matakin gwaji.

Nasiru Abbas, wanda ya taɓa zama shugaban sashin shirye-shirye na Garkuwa FM Sokoto, ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook a yau Laraba. Ya ce an damƙa masa kula da gwajin shirye-shiryen tashar, wanda zai gudana na tsawon watanni biyu zuwa uku.

Iconic FM na daga cikin sabbin kafafen yaɗa labarai da jami'ar Iconic ke shirin ƙaddamarwa a Sokoto domin tallafa wa wajen horas da ɗalibai a fannin sadarwa, da kuma inganta hulɗa da al’umma. Duk da cewa tasha ce mai zaman kanta, za ta rika aiki kafada da kafada da jami’ar.

Baya ga tashar rediyo, akwai kuma shirin ƙaddamar da jaridar Iconic Times da kuma Iconic Digital Media Services, domin cusa fasahar zamani cikin harkokin yaɗa labarai a Najeriya da ma wajen ta.

Ku bayyana ra'ayoyinku...

Amiru Inuwa Kachako mai gabatar da shirye-shiryen siyasa a tashoshin Express Radio da Kanawa Radio Kano, ya ajiye aiki d...
15/07/2025

Amiru Inuwa Kachako mai gabatar da shirye-shiryen siyasa a tashoshin Express Radio da Kanawa Radio Kano, ya ajiye aiki da tashoshin a jiya Litinin.

Amiru ya bayyana ajiye aikin ne ta cikin wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook inda ya godewa shugaban tashar da abokan aikinsa.

Ku bayyana ra'ayoyinku...

Khadija Bello Waziri ce ke farin cikin kasancewa da ku a zango na farko na yaɗa shirye-shiryen tashar Himma Radio 91.1 F...
15/07/2025

Khadija Bello Waziri ce ke farin cikin kasancewa da ku a zango na farko na yaɗa shirye-shiryen tashar Himma Radio 91.1 FM Kano.

Ku bayyana ra'ayoyinku...

📸 Khadija Waziri / Facebook

14/07/2025

Yakubu Musa Fagge kenan yayin da yake gabatar da shirin Rigar Ƙaya na Lumana Radio International a yau Litinin.

Ku bayyana ra'ayoyinku..

Za ku iya samun shirin idan kuka lalubi "Lumana radio International" a Facebook, YouTube da Tiktok.

📸 Lumana Radio International

Kungiyar Aminan Juna ta Kano za ta gudanar da taron cika shekara 10 da kafuwartaKungiyar Aminan Juna ta Jihar Kano, wadd...
12/07/2025

Kungiyar Aminan Juna ta Kano za ta gudanar da taron cika shekara 10 da kafuwarta

Kungiyar Aminan Juna ta Jihar Kano, wadda ta ƙunshi masu kira da tura saƙonni a kafafen yaɗa labarai, za ta gudanar da taron cika shekaru goma da kafuwarta.

Za a gudanar da taron ne a gobe Lahadi, 13 ga watan Yuli, 2025 da misalin karfe 1:00 na rana, a makarantar S.A.S da ke Kofar Kudu, cikin birnin Kano.

Kungiyar, wadda ke da hedikwata a karamar hukumar Nasarawa ta Jihar Kano, na da manufar wayar da kan al’umma da kuma taimakawa gajiyayyu ta hanyar ayyukan jin kai da ta ke gudanarwa a cikin al’umma.

A yayin taron, za a kuma karrama wasu daga cikin fitattun ’yan jarida a jihar Kano.

Taron dai na da nufin ƙara haɗin kai a tsakanin mambobin ƙungiyar, da kuma duba irin ci gaban da aka samu tun kafuwarta shekaru goma da s**a gabata.

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dandalin Masu Sauraron Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share