Hausa Daily Post

Hausa Daily Post Hausa Daily Post is an independent newspaper that broadcasts online in Hausa Language.

Hausa Daily Post is an independent newspaper that broadcasts in Hausa Language.

Tawagar Malaman da s**a kai ziyara Nijar daga Najeriya ke nan a cikin hotuuna.Kuma za a iya cewa ziyarar ta yi kyau sojo...
13/08/2023

Tawagar Malaman da s**a kai ziyara Nijar daga Najeriya ke nan a cikin hotuuna.

Kuma za a iya cewa ziyarar ta yi kyau sojojin Nijar sun bayyana a shirye suke su hau teburin tattaunawa da Ecowas.

Bayan wani taronsu na jiya, Ecowas ta yanke shawarar amfani da sulhu don magance rikicin Nijar kuma za ta tura da tawagarta don fara tattaunawa.

Credit: HD PRESS

Mata 200 ne s**a ci gajiyar tallafin kayayyakin masarufi da kungiyar Farfesa Gwarzo ta raba a Magama-Jibia da ke Katsina...
13/08/2023

Mata 200 ne s**a ci gajiyar tallafin kayayyakin masarufi da kungiyar Farfesa Gwarzo ta raba a Magama-Jibia da ke Katsina

Sak**akon tsadar rayuwa da ta mamaye al'ummomi da dama biyo bayan tashin farashin kayayyakin amfani na yau da kullum a Najeriya, kungiyar matasan Farfesa Abubakar Gwarzo da ke da himma wajen yiwa bil'adama hidima ta raba kayan masarufi a garin Magama-Jibia, dake a iyakar Jamhuriyar Nijar a jihar Katsina.

Babban sakataren kungiyar Kwamared Saifuddeen Ishaq ya bayyana cewa, tallafin na yau na daya daga cikin muhimman manufofi da ayyukan kungiyar na kyautata alaka da tunkarar mabukata domin tallafa musu da rage radadin wasu matsalolin da suke fuskanta.

“A halin yanzu muna da wasu tsare-tsare na shiga kusurwoyin kauyuka da karkara, don ci gaba da aiwatar da irin wannan tallafi wanda daya ne daga cikin tsare-tsaren wannan kungiya. Abin da ke gaban Farfesa Gwarzo ke nan, shi ya sa muke kokarin bin sawunsa domin bayar da gudunmawarmu don samun babban rabo a ranar kiyama.” In ji shi.

Ishaq ya kuma bayyana cewa tallafawa yara a fannin ilimi na daya daga cikin manufofin kungiyar, inda ya ce suna da tsarin da ke kokarin tura yara makarantu domin neman ilimin addini da na boko.

A nasa jawabin sakataren kudi na kungiyar Kwamared Aliyu Adamu Lamama ya ce sun yi la’akari da irin mawuyacin halin da al’ummar yankin ke ciki sak**akon barazanar rashin tsaro da s**a hada da fatara da yunwa, shi ya sa s**a mayar da hankali wajen tallafawa gajiyayyu da mabukata da sauran yara kanana don rage radadin damuwarsu sak**akon rufe iyakokin kasar biyo bayan juyin mulkin da sojoji s**a yi a Nijar, shi ya sa kungiyar ta samar da kayayyakin abinci don tallafa wa mutane.

Aliyu Lamama, ya kuma bukaci kungiyoyin farar hula da masu hannu da shuni da su jajirce wajen samar da irin wannan shiri na tallafawa gajiyayyu da mabukata da ma sauran makwabta domin kawar da jama’a daga mawuyacin halin da suke ciki.

Wasu daga cikin matan da s**a ci gajiyar tallafin, Fadimatu Zahra’u da Hajiya Halima, sun bayyana jin dadinsu bisa namijin kokarin da kungiyar matasa ta Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ke yi na yi musu hidima a halin da suke cikin mummunan yanayi, sun kuma mika godiya ta musamman ga shugabannin kungiyar da suke jajircewa ba dare ba rana, musamman Farfesa Gwarzo wanda ke taka muhimmiyar rawa ta fuskar yi wa al’umma hidima.

Tsaron rayuka da dukiyoyin al'ummar jihar Katsina ne ke gabanmu - Malam Dikko RaddaGwamnan jihar Katsina Malam Dikko Uma...
11/08/2023

Tsaron rayuka da dukiyoyin al'ummar jihar Katsina ne ke gabanmu - Malam Dikko Radda

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD ya a ranar Juma'a 11 ga Agusta, 2023 ya ce babu abin da gwamnatinsa ta sa a gaba k**ar tsaron rayuka da dukiyoyin al'ummar jihar na lungu da sako domin su koma barci da idanunsu biyu a rufe k**ar yadda suke rayuwa a baya.

Gwamnan ya kuma kara jaddada shirin gwamnatinsa na hada hannu da hukumomin tsaro da ke jihar domin ganin tsaron al'ummar jihar ya kyautatu.

Malam Dikko Umaru Radda na magana ne a lokacin da ya karbi bakuncin mataimakin babban Sufeton 'yan sanda mai kula da shiyya ta 14 da ta hada Katsina/Kaduna AIG Ahmad AbdurRahman a lokacin da ya ziyarci Gwamnan a gidan gwamnatin jihar Katsina.

Gwamnan ya yi la'akarin cewa babu inda ke samun ci gaba muddin tsaron yankin na samun tazgaro. Ya sha alwashin cewa gwamnatinsa za ta hada hannu da 'yan sanda da sauran jami'an tsaro domin ganin Katsinawa sun koma harkokinsu yadda ya k**ata ba tare da wata barazanar tsaro ba.

Ya bukaci hadin kai da goyon bayan jami'an tsaron wajen tsare rayuka da dukiyoyin al'ummar jihar.

Mataimakin babban Sufeton 'yan sandan Nijeriya mai kula da shiyya ta 14 ya jinjina wa Gwamnan ganin yadda a kodayaushe yake tsaye wajen ganin an tsare rayuka da dukiyoyin al'ummar jihar Katsina tun lokacin da aka rantsar da shi a matsayin Gwamna a watan Mayun, 2023.

SSA Isah Miqdad,
11/08/2023.

Yadda wani ya dauki gwamnan Katsina a kan babur jim kaɗan bayan fitowa daga Sallar Juma'a Gwamna Malam Dikko Radda ya gu...
11/08/2023

Yadda wani ya dauki gwamnan Katsina a kan babur jim kaɗan bayan fitowa daga Sallar Juma'a

Gwamna Malam Dikko Radda ya gudanar da sallar Juma'a a babban masallacin Radda dake garin Radda a karamar hukumar Charanchi. Bayan kammala sallar, dimbin al'ummar musulmi sun nuna farin cikin su ga mai girma gwamna.

Labarin Sirri Game Da Kin Amincewa Malam El-Rufai Ya Zama Minista.Labarin da muke samu shi ne Janaral TY Danjuma na daya...
11/08/2023

Labarin Sirri Game Da Kin Amincewa Malam El-Rufai Ya Zama Minista.

Labarin da muke samu shi ne Janaral TY Danjuma na daya daga cikin wadanda suke kokarin hana a ba Malam Nasir El-Rufai minista, kuma yana amfani da Sanata Remi Tunubu, matar Shugaban Kasa ne wurin cinma burinsa. Laifin El-Rufai a wurin T.Y Danjume bai wuce maganar Muslim- Muslim Ticket da ya yi a Kaduna kuma wanda hakan ya taimaka aka yi a Kaduna. Abin da suke nuna wa Shugaban Kasa shi ne in aka ba El-Rufai minista hakan yana iya jefa Nijeriya cikin tashin hankali.

Sannan, Kungiyar Kiristoci ta CAN da na Shi’a na amfani da Shehu Sani wurin hada zanga zanga da kuma rubuta ‘petition’ din da aka kai Majalisar Dattawa. A labarin da muka samu, da farko tsohon sanatan ya so ya yi amfani da Mr La ne wurin mika takardar a majalisa amma Sanata Mr La ya ki amincewa shi ne ya yi amfani da na Kogi West.

Baya ga wadannan, akwai kuma wadanda ke yakin El-Rufai saboda suna tunanin in ya masto kusa da shugaban kasa zai hana su rawar gaban hantsi. Akwai masu son yin takarar Shugaban Kasa kuma suna son duk yadda za a yi su hana duk wani babba daga Arewa da zai iya shugaban kasa yin karfi a kusa da shugaban kasa Tinubu. Daya daga cikin masu yakin El-Rufai a boye shi ne Kashim Shettima, Mataimakin Shugaban Kasa. Duk wadannan masu yaki da El-Rufai a boye saboda hana shi yin karfi suna amfani da Nubu Ribado ne.

Sannan sanin kowa ne matsalar wutan lantarki a Nijeriya na daya daga cikin abin da ke mayar da kasar baya kuma yake kara jefa kasar cikin kangin talauci musamman Arewa. Kuma manyan kasar nan su suke siye da wadannan kamfanonin raba wutan lantarki. Saboda haka sun san El-Rufai in ya zama mininstan wutan lantarki sai ya karya su. Sai ya gwamnati ta kwace kaddarorrinsu k**ar yadda ya kudirta wurin tantance shi a majalisa. Saboda haka, su ma sun fito da karfinsu na ganin sun hana El-Rufai zama minista.

In kun lura duk cikin sunayen da aka tura na ministoci daga Arewa babu jajirtacce irin El-Rufai saboda asara

An k**a jami'an 'yan sandan Najeriya da ke tilasta wa matasa tura musu kudi ta asusunsu na banki a jihar Osun.Shin kun t...
11/08/2023

An k**a jami'an 'yan sandan Najeriya da ke tilasta wa matasa tura musu kudi ta asusunsu na banki a jihar Osun.

Shin kun taba fuskantar irin wannan daga wani jami'in dan sanda a Najeriya?
📷 Daily Trust

Bai dace Tinubu ya shugabanci ECOWAS ba – Sheikh Lawal JibiaBayan juyin mulkin da sojojin Nijar s**a yi wa gwamnatin Moh...
11/08/2023

Bai dace Tinubu ya shugabanci ECOWAS ba – Sheikh Lawal Jibia

Bayan juyin mulkin da sojojin Nijar s**a yi wa gwamnatin Mohammed Bazoum a watan Yuli, malaman addinin Islama a Najeriya da wasu kasashen yammacin Afirka na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu dangane da shirin kungiyar ECOWAS na aikewa da dakarun soji domin dawowa da mulkin dimokradiyya jamhuriyar.

Alkali Sheikh Lawal Musa Jibia daga jihar Katsina a Najeriya, ya ce yakin ba zai zama mafita ga jama'a ba, musamman al'ummar jihohin arewacin kasar da ke makwabtaka da Nijar.

Malamin ya ci gaba da cewa, “Rashin sanin shugabanci ne zai sa shugaban ECOWAS Tinubu ya amince da shirin kai wa Nijar hari, alhali al’umma na cikin wani mawuyacin hali da ka iya jefa ‘yan kasar cikin matsaloli da dama.

“Duk kasar da ke fama da matsalolin tsaro irin wannan, bai dace a gina irin wannan yaki da ke kokarin jefa al’ummarta cikin rudani da tashin hankali da tsadar rayuwa ba, wanda ka iya zama sanadin durkushewar kasar." Yace.

Sheikh Jibia, ya bayyana Nijar a matsayin babbar kawar Najeriya, sannan ya bukaci ECOWAS da ta janye aniyar ta na fara yaki a tsakaninsu domin kaucewa matsalolin da yaki ke haifarwa da s**a hada da fatara, yunwa, da yawaitar ayyukan lalata da tabarbarewar tattalin arzikin masana'antu da kasa baki daya.

Ivory Coast za ta tura sojoji NijarShugaban Ivory Coast ya ce ƙasarsa za ta tura sojoji kimanin 1,000 waɗanda za su bi s...
11/08/2023

Ivory Coast za ta tura sojoji Nijar

Shugaban Ivory Coast ya ce ƙasarsa za ta tura sojoji kimanin 1,000 waɗanda za su bi sahun sauran dakarun ko-ta-kwana da za su zauna cikin shirin ko-ta-kwana don tura wa Nijar.

Alassane Ouattara na jawabi ne bayan kammala taron gaggawa na ECOWAS a Abuja, inda ƙungiyar ta ba da umarnin tanadar dakarun ko-ta-kwana don tura su Nijar a ƙoƙarin dawo da aiki da tsarin mulki.

Ya ce ƙungiyar na son a dawo da shugaban ƙasar da sojoji s**a hambarar da gwamnatinsa, Mohammed Bazoum a kan mulki.

Mr Outtara, ya ce sojoji daga Najeriya da Benin da sauran ƙasashe za su haɗu da na Ivory Coast don zama cikin wannan shiri.

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Daruruwan Gonaki Da Amfanin Gona A NejaTun kafin isowar damunar, hukumar hasashen yanayi ta Naj...
10/08/2023

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Daruruwan Gonaki Da Amfanin Gona A Neja

Tun kafin isowar damunar, hukumar hasashen yanayi ta Najeriya ta yi gargadin samun ambaliyar ruwa a kananan hukumomi da dama na kasar a ciki har da na jihohin Nejan.

VOA Hausa ta ruwaito cewa, daruruwan gonaki ne hade da amfani gona mai dumbin yawa s**a salwanta a jihar Nejar Najeriya sanadiyyar ambaliyar da ta aukawa wasu kananan hukumomi.

Wannan al’amari dai ya jefa dubban manoma cikin yanayi na tashin hankali tare da fargabar kara samun karancin abinci a wannan shekara.

Tun kafin isowar damunar, hukumar hasashen yanayi ta Najeriya ta yi gargadin samun ambaliyar ruwa a kananan hukumomi da dama na kasar ciki har da Jihar Nejan.

Alh. Shehu Yusuf Galadima Shugaban Hadaddiyar Kungiyar Manoma ta jihar Neja ya ce sun tabka asara ta miliyoyin Naira a sak**akon yadda ambaliyar ta yi awon gaba da gonakin masara da na shinkafa.

Ita ma dai Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta jihar Neja ta ce ba ta gama tantance yawan gonakin da ambaliyar ta mamaye ba a cewar mukaddashin Darakta na hukumar a jihar Neja Malam Garba Salihu.

Har ila yau dai Hukumar Bada Agajin ta ce akwai yiwuwar kara samun ambaliyar a nan gaba saboda haka jama’a su kula inji Malam Garba Salihu.

Yayin da aka tabka asara gonaki a sak**akon ambaliyar a jihar Nejan, a gefe guda kuma ‘yan bindiga ne s**a hana manoma zuwa gonakin al’amarin da masu sharhi ke ganin matsalar babbace saboda haka akwai bukatar daukar kwakkwarar mataki.

Sojojin Nijar sun nada matashiya mai shekaru 28 a mukamin ministar yawon bude ido da shakatawa.Mme Guichen Aghaichata AT...
10/08/2023

Sojojin Nijar sun nada matashiya mai shekaru 28 a mukamin ministar yawon bude ido da shakatawa.

Mme Guichen Aghaichata ATTA na daya daga cikin matasan Nijar da s**a yi wannan nasara a karon farko.

Me za ku ce da ita?

Wata kotu a Kano ta ƙwace kujerar ɗan majalisar tarayya na NNPP na TarauniKotun sauraren kararrakin zabe ta Majalisar Do...
10/08/2023

Wata kotu a Kano ta ƙwace kujerar ɗan majalisar tarayya na NNPP na Tarauni

Kotun sauraren kararrakin zabe ta Majalisar Dokoki ta kasa da ta Jiha da ke zamanta a Kano ta soke zaben dan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazabar Tarauni, Mukhtar Yarima, na jam’iyyar NNPP, a kan amfani da jabun shaidar karatu.

Mai shigar da kara, Hafizu Kawu na jam’iyyar APC ne ya kalubalanci nasarar zaben Muktar Yerima, wanda kotun ta soke a yau Alhamis.

Kotun mai kwamitin alkalai guda uku ta yanke hukuncin cewa takardar shaidar kammala makarantar firamare da wanda ake kara, Muktar Yerima ya bayar ta jabu ce.

Kotun ta yi bayanin da cewa makarantar firamare ta Hausawa ta ce ba satifiket din ta ne Yarima yayi amfani da shi ba kuma baya cikin jerin sunayen ɗaliban ta.

Bisa dukkan alamu ECOWAS ta janye barazanar da ta yi wa NijarKungiyar Kasashen Afrika ta Yamma, wato ECOWAS, ta ce za ta...
10/08/2023

Bisa dukkan alamu ECOWAS ta janye barazanar da ta yi wa Nijar

Kungiyar Kasashen Afrika ta Yamma, wato ECOWAS, ta ce za ta ci gaba tintibar sojojin da s**a yi juyin mulki a Jamhuriyar Nijar a yunkurin da take na warware matsalar, a wani yanayi da ke nuna alamun janye barazanar amfani da karfin soji domin mayar da zababiyar gwamnatin kasar.

Yayin bude taro na musammman da shugabannin kungiyar a Abuja, shugaban ECOWAS Bola Ahmed Tinubu da ke jagorancin taron ya bayyana taron na yau a matsayin mai matukar muhimmanci wajen ci gaba da dorewar yankin a matsayin dunkulalliya wadda za ta taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da kuma ci gaban jama’arta.

Shugaban ya ce taronsu na yau zai bada damar cikakken nazari kan ci gaban da aka samu da kuma matsalolin da aka fuskanta tun bayan taron farko da s**a yi kan Nijar, domin duba gyaran da ya k**ata a yi ko kuma gibin da ya k**ata a cike domin gyara lamarin.

Tinubu ya ce a matsayinsu na masu kare demokiradiya, ya zama wajibi su tintibe kowanne bangare, cikinsu har da da sojojin da s**a yi juyin mulki domin ganin sun amince da bukatar mayar da zababben shugaban kasa Bazoum Mohammed karagar mulki.

Shugaban na ECOWAS ya ce ya zama wajibi a gare su a matsayin shugabanni su fahimci cewar halin da ake ciki a Nijar na zama barazana a gare su, kuma abin da ke iya biyo baya zai shafi yankin baki daya.

Tinubu ya bayyana fatar cewar wannan taro na biyu kan Nijar zai bada damar daukar matakin da ya dace wanda zai taimaka wa yankin baki daya.

Address

Wuse Ii

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Daily Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa Daily Post:

Share

Category