WAT News Hausa

WAT News Hausa Tsantsar gaskiya da cikakken bayani

Saudiyya ta bayyana matakin da Faransa ta dauka na amincewa da kasar Palastinu a matsayin wani muhimmin mataki na tarihi...
25/07/2025

Saudiyya ta bayyana matakin da Faransa ta dauka na amincewa da kasar Palastinu a matsayin wani muhimmin mataki na tarihi da ke kara tabbatar da matsayar da al’ummar duniya s**a cimma game da ’yancin Palasdinawa na kafa ’yantacciyar kasa bisa iyakokin da aka tsara tun shekarar 1967, tare da Gabashin birnin Kudus a matsayin babban birninta.

Ma’aikatar Harkokin Wajen Saudiyya ta ce wannan mataki yana da matukar muhimmanci wajen ci gaba da kokarin tabbatar da doka da oda na kasa da kasa da kuma aiwatar da kudurorin da s**a dace. Haka kuma, Saudiyya ta bukaci sauran kasashen da har yanzu ba su amince da kasar Palasdinu ba da su dauki irin wannan mataki mai kyau domin tallafa wa zaman lafiya da kare hakkokin Palasdinawa.

Yayin da yake kaddamar da cibiyar kula da cutar daji a Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Katsina ranar Alhamis, ministan...
25/07/2025

Yayin da yake kaddamar da cibiyar kula da cutar daji a Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Katsina ranar Alhamis, ministan lafiya Farfesa Muhammed Ali Pate ya ce Najeriya na fuskantar kimanin sabbin kamuwa dubu 127,000 na cutar daji a kowace shekara.

Ya kara da cewa cututtukan da ba sa yaduwa na kara yawan tasirinsu a Najeriya, kuma ana hasashen adadin masu kamuwa da cutar zai karu nan gaba.

A ganin ku, me ya kamata gwamnati da al'umma su mayar da hankali a kai don rage yawan mace-macen da cutar daji ke haddasawa a Najeriya?

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana a yau Alhamis cewa Faransa za ta amince da ƙasar Palastinu a watan Satumba m...
24/07/2025

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana a yau Alhamis cewa Faransa za ta amince da ƙasar Palastinu a watan Satumba mai zuwa.

A gefe guda kuma Firayim Ministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya ce wannan mataki “sakamako ne ga ta’addanci,” yayin da Ministan Tsaronsa ya bayyana shi da cewa “abin kunya ne, da miƙa wuya ga ta’addanci.”

Shin menene ra'ayinku game da wannan?

A wani yunƙuri na ƙarfafa tsaron ƙasa da fuskantar ƙalubalen tsaro na duniya, Jamus na shirin daukar matasa ‘yan shekara...
24/07/2025

A wani yunƙuri na ƙarfafa tsaron ƙasa da fuskantar ƙalubalen tsaro na duniya, Jamus na shirin daukar matasa ‘yan shekara 18 har 40,000 a kowace shekara domin aikin soja na sa kai daga yanzu har zuwa shekarar 2031.

- Babbar Manufa:

Faɗaɗa rundunar sojoji zuwa dubu 260,000 kafin 2035

Ƙara yawan ajiyar sojoji (reserves) zuwa dubu 200,000

Tallafa wa ƙoƙarin NATO wajen hana cin karen da ba bu babbaka daga Rasha

Abubuwan da za su jawo hankalin matasa sun haɗa da:

Dama mai sassauci ta yin aiki, kyakkyawan albashi, da hanyoyin samun ci gaba a aikin soja

Wannan na nuna yadda Jamus ke mayar da hankali sosai wajen tsare-tsarenta na tsaro, abu da ba a saba gani ba tun bayan yaƙin duniya na biyu.

Sojojin Operation Hadin Kai tare da hadin gwiwar rundunar sojojin sama, CJTF da masu farauta, sun cafke wasu da ake zarg...
24/07/2025

Sojojin Operation Hadin Kai tare da hadin gwiwar rundunar sojojin sama, CJTF da masu farauta, sun cafke wasu da ake zargi da bai wa 'yan ta’adda kayan sadarwa, muggan kwayoyi, kayan hada bama-bamai da makamai a Arewa maso Gabas.

Babban Daraktan Yada Labarai na Tsaro, Manjo Janar Markus Kangye, ya ce an kuma kashe ‘yan ta’adda da dama yayin sumame da kwantan bauna daga 15 zuwa 22 ga Yuli, 2025.

A ganinku, me ya kamata a kara yi don hana wadannan kayan su kai hannun ‘yan ta’adda?

Fatma Wahid ta saba da jin yunwa a cikinta, amma abin da ke ci mata tuwo a ƙwarya shi ne jin kukan 'ya'yanta uku ƙanana ...
23/07/2025

Fatma Wahid ta saba da jin yunwa a cikinta, amma abin da ke ci mata tuwo a ƙwarya shi ne jin kukan 'ya'yanta uku ƙanana suna neman abinci.

"Zuciyata na karyewa," in ji Wahid, mai shekara 39, daga birnin Deir al-Balah a tsakiyar Gaza. "Yaran ba sa samun cikakken ƙoshi."

A faɗin zirin Gaza, iyalai da dama na fuskantar ƙalubale na yau da kullum wajen samun abinci. Yunwar yara, alamar rashin abinci da ke shafar al’umma baki ɗaya, na yaɗuwa da sauri. ’Yan Falasɗinu da ƙungiyoyin agaji na cewa ƙarancin abinci da a baya ke shafar sassa daban-daban yanzu ya mamaye gaba ɗaya yankin.

Shin me kuke tunani shugabannin ƙasashe za su iya yi don kawo ƙarshen wannan yunwa a Gaza?

An shirya gudanar da zagaye na uku na tattaunawar zaman lafiya tsakanin jami’an Ukraine da na Rasha a birnin Istanbul, ƙ...
23/07/2025

An shirya gudanar da zagaye na uku na tattaunawar zaman lafiya tsakanin jami’an Ukraine da na Rasha a birnin Istanbul, ƙasar Turkiyya, a ranar Laraba, wanda zai zama karo na farko da za su gana cikin sama da makonni bakwai, yayin da Amurka ke matsin lamba don cimma yarjejeniyar tsagaita wuta.

Sai dai ana ganin yiwuwar samun ci gaba a wannan ganawa ba shi da yawa.

Ɓangarorin biyu sun taɓa ganawa a watan Mayu da Yuni, amma sun kasa cimma matsaya kan kawo ƙarshen yaƙin da ke tafiya tsawon shekaru uku da rabi.

Fadar Kremlin ba ta tabbatar da halartar ganawar ba, amma ta gargaɗi jama’a da kada su sa ran wani “mu’ujiza” idan ma ta halarta.

Ɓangarorin biyu na da saɓanin matsayi sosai dangane da yadda za a kawo ƙarshen rikicin.

Rasha na buƙatar Ukraine ta janye daga yankuna huɗu da ta bayyana cewa ta mamaye a watan Satumban 2022, buƙatar da Ukraine ta ce ba za ta yarda da ita ba.

Ukraine ta ce ba za ta shiga kowace tattaunawa kan yankuna ba sai bayan an samu tsagaita wuta, kuma ba za ta taba amincewa da ikon Rasha a kan kowanne yanki da ta mamaye ba, ciki har da Crimea, wadda Rasha ta karɓe ta tun shekarar 2014.

Shin kuna ganin tattaunawa tsakanin Ukraine da Rasha za ta iya kawo ƙarshen rikicin, ko kuwa kowanne ɓangare zai ci gaba da dagewa bisa matsayinsa?

📷/: Hoto/: Vladimir Putin X Volodymir Zelensky/: credit/: X

Ƙungiyar Iyayen ’Yan Matan Chibok da s**a ɓace ta bayyana alhinin ta tare da jimamin rasuwar tsohon Shugaban Ƙasa Muhamm...
22/07/2025

Ƙungiyar Iyayen ’Yan Matan Chibok da s**a ɓace ta bayyana alhinin ta tare da jimamin rasuwar tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, tare da sake jaddada kira ga gwamnati da ta ceto sauran ’yan mata 87 da har yanzu ba a samo su ba tun bayan sace su a shekarar 2014.

A cikin wata sanarwa da Yana Galang da Zannah Mohammed s**a sanya wa hannu a madadin iyayen, ƙungiyar ta miƙa ta’aziyya ga iyalan Buhari tare da yabawa gwamnatinsa bisa ƙoƙarin da ya yi wajen kuɓutar da ’yan mata 103 daga cikin 276 da Boko Haram ta sace daga makarantar sakandaren gwamnati ta ’yan mata da ke Chibok, Jihar Borno.

📷/: Hoto/: Late Muhammadu Buhari/: Credit/: WSJ

Dangote ya bayyana hakan ne a yau, a yayin wani taro mai taken "Taron Bincike kan Kasuwar Man Da Aka Tace a Yammacin Afi...
22/07/2025

Dangote ya bayyana hakan ne a yau, a yayin wani taro mai taken "Taron Bincike kan Kasuwar Man Da Aka Tace a Yammacin Afirka, wato Global Commodity Insights Conference on West African Refined Fuel Markets.

Inda ya bayyana cewa sun sayi ƙasa mai faɗin hektar 2,700, wanda ya ninka girman Victoria Island da ke Legas har sau bakwai (7x).

Ya ce wannan matsala ta kawo babban cikas ga ci gaban ɗaya daga cikin manyan ayyukan masana'antu a nahiyar Afirka.

📷/: Hoto/: Aliko Dangote/: Credit/: Ernest Ankomah/Getty Images.

Aliko Dangote ya yi gargaɗin cewa Afrika ba za ta samu sabbin matatun mai masu girma ba, sai an yaƙi cin hanci da son ka...
22/07/2025

Aliko Dangote ya yi gargaɗin cewa Afrika ba za ta samu sabbin matatun mai masu girma ba, sai an yaƙi cin hanci da son kai da ke tattare da harkar man fetur ta hanyar ɗaukar matakan siyasa masu ƙarfi.

Dangote ya bayyana tashar ajiya ta mai da ke teku kusa da Lomé, Togo, wadda manyan ‘yan kasuwar ƙasa da ƙasa ke sarrafawa, a matsayin babban cikas. Tashar na ɗauke da fiye da ton miliyan biyu na man da ake Shigowa dashi daga ƙasashen waje wanda ake sayarwa da tsada saboda ƙarancin matatun mai.

Dangote ya ce masu cin moriyar tsarin za su yi yaƙi da duk wani yunƙuri na gina sabbin matatu. Ba tare da goyon bayan siyasa da haɗin kan yankuna ba, a cewarsa, babu wata babbar matatar mai da za a iya ginawa a yankin kudu da hamadar Sahara har ƙarshen rayuwarmu.

Shin kuna ganin shugabannin Afrika za su iya samun ƙarfin hali su karya tsarin da ke hana ci gaban masana'antar mai a nahiyar kamar yadda Dangote ya faɗa?

📷/: Aliko Dangote/: Credit/: LUDOVIC MARIN/Pool via Reuters

Birtaniya da wasu ƙasashe 27 na Yammacin duniya, ciki har da Ostareliya, Kanada, Faransa da Italiya, sun fitar da sanarw...
22/07/2025

Birtaniya da wasu ƙasashe 27 na Yammacin duniya, ciki har da Ostareliya, Kanada, Faransa da Italiya, sun fitar da sanarwar haɗin gwiwa a ranar Litinin inda s**a ce ya zama dole a kawo Ƙarshen yaƙin Isra’ila da Hamas a Gaza yanzu, suna mai jaddada cewa halin da fararen hula ke ciki ya taɓarɓare matuƙa.

Wannan sanarwa ta zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun yawan mace-mace a wuraren raba agaji, da kuma ranar da Isra’ila ta fadada ayyukan sojinta a gaɓar zirin Gaza, musamman a yankin Deir al-Balah.

Shin kuna ganin Isra’ila ta ɗauka wannan kira mai tsauri da muhimmanci kuwa?

📷/:Hoto/: Credit/: Quds NN/:X

Ƙungiyar Dillalan Man Fetur da Iskar Gas ta Ƙasa (NOGASA) ta bayyana rashin amincewarta da shirin da Matatar Man Dangote...
22/07/2025

Ƙungiyar Dillalan Man Fetur da Iskar Gas ta Ƙasa (NOGASA) ta bayyana rashin amincewarta da shirin da Matatar Man Dangote ke yi na rarraba mai kai tsaye ba tare da bin hanyoyin dillalan ba.

Shugaban NOGASA, Benneth Korie, ya yi gargaɗin cewa wannan mataki zai iya dagula harkokin masana’antar, ya haifar da barazanar rasa dubban ayyuka, tare da rugujewar tsarin rarrabawa da ake amfani da shi yanzu, musamman yayin da ake shirin fara rarraba dizal da fetur a faɗin ƙasar daga 15 ga Agusta. Korie ya kuma roƙi masu ruwa da tsaki su shiga cikin lamarin.

Shin kuna ganin matakin Dangote na rarraba mai kai tsaye zai kawo sauƙi ga masu amfani ko zai cutar da ‘yan kasuwa da ma’aikata a fannin mai?

📷/: Hoto/: Aliko Dangote/: File Photo

Address

Wuse

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when WAT News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share