Al-HAQ True news

Al-HAQ True news Sahihan Labarai da Dumi Dumin su

🚨🚨Dean Huijsen: "Real Madrid ita ce ƙungiya mafi kyawu a duniya, ita ce ƙungiyar da nake burin zuwa, yanzu kuma na zo, b...
04/06/2025

🚨🚨Dean Huijsen: "Real Madrid ita ce ƙungiya mafi kyawu a duniya, ita ce ƙungiyar da nake burin zuwa, yanzu kuma na zo, ba zan jira ba wajen farawa da kyau a ƙungiyar da nake mafarki."

🚨🚨 BABBAN LABARI: AC Milan na mafarkin daukar dan wasa Luka Modrić a wannan bazarar.Sabon daraktan kungiyar Igli Tare na...
02/06/2025

🚨🚨 BABBAN LABARI: AC Milan na mafarkin daukar dan wasa Luka Modrić a wannan bazarar.

Sabon daraktan kungiyar Igli Tare na mafarkin kawo Luka Modrić zuwa AC Milan.

Modrić ya samu tayi da dama daga wasu kungiyoyi a fadin duniya tun lokacin da Real Madrid ta yanke hukuncin rabuwa da shi, sai dai har yanzu Modric din ba ya gaggawar zabin wata kungiya.

[Fabrizio]

🚨 YANZU-YANZU: Real Madrid na son daukar dan wasan Ajax wato Abdellah Ouazane. A na tattauna wa a halin yanzu kuma akwai...
02/06/2025

🚨 YANZU-YANZU: Real Madrid na son daukar dan wasan Ajax wato Abdellah Ouazane.

A na tattauna wa a halin yanzu kuma akwai kyakkawan zaton cinikin zai yiwu.

[Rodra]

🚨🚨Real Madrid za ta yanke hukunci nan ba da jimawa ba kan halin da Dan wasa Nico Páz ke ciki.  Ƙarin tuntuɓar da za su b...
02/06/2025

🚨🚨Real Madrid za ta yanke hukunci nan ba da jimawa ba kan halin da Dan wasa Nico Páz ke ciki. Ƙarin tuntuɓar da za su biyo baya a cikin kwanaki masu zuwa yayin da Real Madrid za ta iya dawo da shi kan Yuro miliyan 8.

A cewar- Fabrizio Romano

🛑An bawa Neymar  katin ja bayan ya karɓi katin gargaɗi na biyu a wasan da s**a fafata da Botafogo, bayan da ya yi yunkur...
02/06/2025

🛑An bawa Neymar katin ja bayan ya karɓi katin gargaɗi na biyu a wasan da s**a fafata da Botafogo, bayan da ya yi yunkurin jefa kwallo da hannu 🟥

Shugaban Gabon na riƙon-ƙwarya, Janar Oligui Nguema, shi ne ya ɗauki matakin kan jami’an gwamnatinsa.Ƙarin bayani - elam...
21/08/2024

Shugaban Gabon na riƙon-ƙwarya, Janar Oligui Nguema, shi ne ya ɗauki matakin kan jami’an gwamnatinsa.

Ƙarin bayani - elamdy.com.ng/livescore

TABBAS AKWAI MATSALAA ganawar da Shugaban Kasa Tinubu yayi da Hafoshin tsaro dazu, Shugaban Sojojin Nigeria General Chri...
06/08/2024

TABBAS AKWAI MATSALA

A ganawar da Shugaban Kasa Tinubu yayi da Hafoshin tsaro dazu, Shugaban Sojojin Nigeria General Christopher Musa yayi bayanin abinda s**a cimma da matakin da zasu dauka

(1) Hankalin Shugaban Kasa Tinubu yayi mummunan tashi bayan ganin masu zanga-zanga suna daga Tutar Kasar Russia, don haka sun tabbatar da cewa daga Tutar wata Kasa a lokacin zanga-zanga laifi ne na cin amanar Kasa (Treason) wanda ba zasu lamunta ba

(2) Sun tabbatar da cewa batagari sun kwace iko da zanga-zanga, don haka yanzu babu eata sauran zanga-zangar lumana da ta rage, zasu hukunta duk wanda aka gani ya fito zanga-zanga a matsayin batagari

(3) Shugaban Sojoji Christopher ya gargadi masu kira ga Sojojin Nigeria su kifar da Gwamnatin Tinubu, Shugaban Sojojin yace ba za'a taba yun juyin mulki ba, abinda s**a sa gaba a yanzu shine bawa tsarin mulkin Demokaradiyya cikakken kariya

Wannan shine abubuwa uku wanda Shugaban Kasa Tinubu da Hafsoshin tsaro na Kasa s**a tattauna a kai, kuma s**a cimma matsaya

A shawarce duk wanda ka sani dan uwanka ne ko aboki to ka bashi shawara ya janye daga fita zanga-zanga, domin abinda tattaunawar Tinubu da Hafsoshin tsaronsa suke nufi shine zasu dakile duk wanda aka gani ya fito zanga-zanga, kun ga dai yadda aka harbe wasu bayin Allah

Don haka 'yan uwa ayi hakuri, mutanen nan babu Allah a lissafinsu, kuskure ne munyi tunda farko muka biye wa yaudaran wasu miyagun Malamai da s**a saka rigar Malaman Allah s**a yaudaremu da addini

Mafita shine mu kai karan azzaluman Nigeria da miyagun Malamansu zuwa gurin Allah Madaukakin Sarki, mu tashi cikin dare muyi Sallah da Karatun Qur'ani mu saka goshin mu a Kasa mu kai karan azzalumai gurin Allah, babu shakka Wallahi Allah zai mana maganinsu ba tare da bata lokaci ba tunda sun zaluncemu

Yaa Allah Ka isar mana, Ka mana maganin abinda yafi karfin mu 🙏

DDatti Assalafiy
Me za ku ce

IIndararo Hausa

Gwamnan jihar Katsina da ke arewacin Nijeriya, Dikko Radda ya yi zargin cewa akwai wasu manyan mutane a ƙasar da ke ɗauk...
31/07/2024

Gwamnan jihar Katsina da ke arewacin Nijeriya, Dikko Radda ya yi zargin cewa akwai wasu manyan mutane a ƙasar da ke ɗaukar nauyin masu shirya zanga-zangar da matasa ke son yi.

A wata hira ta musamman da ya yi da TRT Afrika, Gwamna Radda ya ce duk da yake kundin tsarin mulkin Nijeriya ya bai wa ‘yan ƙasa damar yin zanga-zangar lumana, barin ta zai fi alheri saboda tsoron abin da ka iya biyo bayanta na yiwuwar tashin hankali.

Amma ya ce ya yarda ana cikin wahala, kuma dole gwamnatocin jihohi da na tarayya su tashi tsaye wajen kawo sauƙi ga al’ummominsu.

Da Ɗumi-Ɗumi 🔥An Gwabza Ƙazamin Faɗa Tsakanin Ɓangarorin Ƴan Bindiga Biyu A JIhar ZamfaraƳan Ta’adda Da dama sun mutu a ...
28/02/2024

Da Ɗumi-Ɗumi 🔥

An Gwabza Ƙazamin Faɗa Tsakanin Ɓangarorin Ƴan Bindiga Biyu A JIhar Zamfara

Ƴan Ta’adda Da dama sun mutu a wani kazamar fada Da ya barke tsakaninsu a kauyen Hayin Alhaji da Dajin Munhaye Na karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara ta arewacin Najeriya.

Rahotanni sun Bayyana cewa gwabzawar ta faru ne a sakamakon yunkurin da wasu ‘yan bindiga daga jihar Katsina s**a yi na yin garkuwa da wasu mazauna kauyukan Zamfara a karshen makon nan.

A Cewar rahotannin bayan da 'yan bindigar na Katsina s**a mamaye kauyukan na Zamfara ne, kasurgumin dan bindigar nan na jihar Ado Alero ya yi Gaggawar kai wa kauyukan dauki don dakile Yunkurinsu na satar jama'a.

Shaidun gani da ido sun tabbatarwa manema labarai Cewa a wannan yunkuri an gwabza kazamin fada Tsakanin bangarorin biyu wanda ya kai ga asarar Rayuka, duk da cewa dai bangaren Ado Alero sun Dakile shirin garkuwa da mutanen kauyen.

A halin yanzu, bayanai sun ce mazauna kauyukan da Aka gwabza kazamin fadan sun shirya gudanar da Birne gawarkin 'yan ta'addan da s**a mutun, Wadanda har zuwa yanzu ba a kai ga tantance Adadinsu ba.

Address

Wuse

Telephone

+2349122140537

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Al-HAQ True news posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Al-HAQ True news:

Share