31/05/2026
A RANAR 13 GA WATAN YUNI, MU ZABI JAGORAN DA YA SAN CIWON AL'UMMA!
Hon. Salisu Muhammadu mutum ne mai hangen nesa da burin ganin Ngurore Ward ta samu ci gaba. Matashi ne da ke mutunta kowa ba tare da la'akari da yare, addini ko matsayi ba, domin a wajensa kowa ɗaya ne.
Burinsa shi ne gina matasan Ngurore Ward, ƙarfafa haɗin kai tsakanin al'umma, da kuma tallafawa masu buƙata a duk lokacin da dama ta samu. Manya da ƙanana sun san shi a matsayin mutum mai son taimako da cigaban al'umma.
A ranar zaɓen ƙananan hukumomi ta 13 ga Yuni, ku fito ku kaɗa ƙuri'arku domin Hon. Salisu Muhammadu a matsayin Kansila na Ngurore Ward.
Daga Prince Abdu B. Gongosh.
Note: Wannan talla ce da aka biya kuɗinta. Ra'ayoyin da ke cikinta na mai talla ne, ba lallai su wakilci matsayar Ngurore Community TV ba.