04/11/2025
A cikin wata tattaunawa mai zafi dake cike da tunani, matasan Ngurore ward sun gudanar da muhawara a cikin WhatsApp group na Ngurore Youth Summit, inda s**a tattauna babban matsalar da ke addabar matasa, shaye-shaye da lalacewar rayuwa.
Tattaunawar ta fara ne da Husina Tukur wadda ta bayyana cewa babban kalubalen Ngurore yanzu shi ne shaye-shaye gaskiya, abin da ya tayar da hankali a cikin rukuni. Yakubu Abdulrazak ya mayar da martani da cewa rashin sani da ilimi ne ke jawo yawancin matasa fadawa cikin wannan hali, yayin da Musa Adamu ya jaddada cewa jahilci shi ne tushen shaye-shaye.
MD ya kawo bangaren kwarin gwiwa inda ya ce matasa 75% a Ngurore masu aiki tukuru ne, amma ya nuna damuwa da cewa kashi 65% daga cikinsu ba sa son yin karatu sosai.
Hauwa Umar ta dauki matsayin jagora, ta ce lokaci ya yi da za a shirya wayar da kai kan illar shaye-shaye, musamman ga kananan yara, sannan ta tambayi ko matasan Ngurore za su iya hada kai su fuskanci shugabanninsu cikin gaskiya da tsari.
Umar Yunusa ya bayar da shawarar kafa dokoki da ƙa’idoji na gari don rage yaduwar miyagun kwayoyi, yayin da Joel Akila ya jaddada cewa canji zai fara daga mu kanmu, ba daga gwamnati kawai ba.
Yunusa Abdullahi ya kawo jawabi mai zurfi da ke jan hankali:
“Ba aikin yi kawai muke bukata ba — muna bukatar gaskiya, soyayya da fahimta. Idan muna so mu ci gaba, mu guji abubuwan da ke lalata rayuwarmu.”
Tattaunawar ta kuma karkata zuwa batun ilimi da kwararru a Ngurore, inda Hauwa Umar ta tambayi ko akwai likitoci, lauyoyi, injiniyoyi, manazarta ko manyan jami’an gwamnati daga garin.
Abdullahi Musa da MD sun bayyana wasu kwararru kamar Halidu Dahiru (Chartered Accountant), Abdullahi Dauda (Software Engineer), Abdullahi Maigawa (Educationist), yayin da Umar Yunusa ya ƙara da cewa akwai Farfesa daga Ngurore mai koyarwa a jami’ar ABU Zaria fiye da shekaru goma.
Wannan tattaunawa ta zama tamkar karamin taron manazarta — ta haɗa ra’ayoyi, gaskiya, da mafita, kuma ta nuna cewa matasan Ngurore sun fara gane muhimmancin haɗin kai, ilimi, da gyaran al’umma daga ƙasa.
“Yaki da shaye-shaye aiki ne na kowa — gwamnati, iyaye, malamai, da matasa.”
“Wayar da kai a makarantu da masallatai za ta iya ceci rayuka da dama.”
“Ngurore tana da ƙwararru — lokaci ne da zasu fito su ba da gudunmawa.”
Ku ci gaba da turo ra’ayoyinku, mu hada kai mu gina Ngurore — garin da kowa ke alfahari da shi.
Ngurore Community TV
📷Getty Images