Ngurore Community TV

Ngurore Community TV Labarai ll Rahotanni II Al'amuran yau da kullum II Shirye Shirye ll

11/10/2025

Kusan shekaru huɗu kenan da wani matashi ɗan asalin Ngurore mai suna Haruna, wanda aka fi sani da Haruna Million, ya bar gida zuwa Abuja tare da yayansa.
Tun daga wannan lokaci ba a sake jin duriyarsa ba, lamarin da ya jefa iyalansa cikin damuwa da addu’a.

Wakilinmu Salihu Umar ya tattauna da ƙaninsa, wanda ya bayyana yadda lamarin ya faru tun daga farko.
A halin yanzu, ana kira ga duk wanda ya san inda Haruna yake ko kuma yana da labari a kansa da ya tuntuɓi lambobin 09041754099 ko 07068489244.

Allah ya sa a dace, kuma Allah ya dawo da shi cikin ƙoshin lafiya.

Daya daga cikin hazikan ‘ya’yan garin Ngurore, Babangida Abdullahi, ɗalibi mai karatu a Department of Chemistry, Level 4...
11/10/2025

Daya daga cikin hazikan ‘ya’yan garin Ngurore, Babangida Abdullahi, ɗalibi mai karatu a Department of Chemistry, Level 400 a Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) Bauchi, ya samu babban mukami na Chief of Staff a ƙungiyar National Association of Science Students (NASS), ATBU Bauchi Chapter.

Wannan na ƙunshe ne a wata takardar da Shugaban ƙungiyar, Comr. Idris Musa Adam, ya sanya wa hannu a ranar 10 ga Oktoba, 2025, inda aka bayyana cewa nadin ya biyo bayan jajircewar Babangida a fannin shugabanci, kishin ɗalibai da kuma gudunmawarsa ga ci gaban ƙungiyar.

A cikin takardar, shugaban ƙungiyar ya bayyana cewa:

“Wannan mukami alamar amincewa ne da jajircewa da nagartar Babangida Abdullahi, kuma muna sa ran zai ci gaba da wakiltar ƙungiyar da kwarewa da gaskiya.”

A matsayin sa na Chief of Staff, Babangida zai rika kulawa da ayyukan majalisar zartarwa ta ƙungiyar, ba da shawara ga shugaban ƙungiya, da wakiltar ƙungiyar a hukumance.

Al’ummar Ngurore sun bayyana farin cikinsu bisa wannan nasara, suna masu cewa wannan wata gagarumar dama ce da ke ƙara ɗaukaka sunan garin a tsakanin ɗaliban jami’o’i.

“Wannan nasara ce ba wai ta Babangida kaɗai ba, har da mu matasan Ngurore baki ɗaya,” in ji wani matashi da ke cikin garin.

Ngurore Community TV
📷Babangida Abdullahi

Kungiyar Izala (JIBWIS) Ngurore ta sanar da gudanar da gagarumar muhadara a yau bayan sallar Magariba zuwa Isha’i, a Mas...
10/10/2025

Kungiyar Izala (JIBWIS) Ngurore ta sanar da gudanar da gagarumar muhadara a yau bayan sallar Magariba zuwa Isha’i, a Masallacin JIBWIS 2 Bakin Kasuwa.

Taken Muhadara: Wajabci da Muhimmancin Bayar da Zakka a Musulunci
Mai Gabatarwa: Sheikh Ahmad Modibbo

Sanarwar ta fito ne daga Shugaban Majalisar Malamai, Sheikh Imam Muhammad Abubakar (Hafizahullah) a shafinsa na Facebook, inda ya gayyaci al’umma su halarta domin amfana.

Ngurore Community TV
📷Jibwis Ngurore /Facebook

Sakon taya Murna  ga Fidelis Yayirus – Sabon Jami’in ɗan Sanda danga Ngurore Muna taya Fidelis Yayirus murna bisa kammal...
10/10/2025

Sakon taya Murna ga Fidelis Yayirus – Sabon Jami’in ɗan Sanda danga Ngurore

Muna taya Fidelis Yayirus murna bisa kammala horo tare da halartar bikin Passing Out Parade (POP) a hukumance, inda yanzu ya shiga cikin rundunar ’Yan Sanda na Najeriya.

Wannan nasara ta Fidelis ba wai tasa kaɗai bace, nasara ce ga iyalansa da kuma al’ummar Ngurore baki ɗaya. Shiga sahun masu kare rayuka da dukiyoyi na ƙasar nan babban abin alfahari ne da kuma alamar jajircewa wajen bautawa ƙasa.

Muna fatan Allah ya ba shi tsarewa, basira, da ƙwarin guiwa wajen gudanar da wannan aiki mai muhimmanci.

Ngurore Community TV
📷Benjamin Samuel

Rashin Kyawun Hanya Yana Hana Mutane Daga Filin Jirgi da Goduwo Shigowa NguroreHanyar da ta haɗa Filin Jirgin  da Mboi, ...
10/10/2025

Rashin Kyawun Hanya Yana Hana Mutane Daga Filin Jirgi da Goduwo Shigowa Ngurore

Hanyar da ta haɗa Filin Jirgin da Mboi, Goduwo har zuwa Kulangu wacce ake dogaro da ita wajen harkokin gona da kasuwanci, yanzu ta zama abin damuwa ga mazauna yankin. Lalacewar gadan da ke kan hanyar ta hana mutane samun sauƙin sufuri, musamman a lokacin damuna, inda ruwa ke toshe hanya da kuma hana ababen hawa wucewa.

Wakilin Ngurore Community TV ya ziyarci wurin, inda ya tabbatar da irin koken da jama’a ke yi. “Idan damuna ta k**a, manoma ba za su iya kai kayan gonar su kasuwa ba, dabbobi ma sai sun makale. Hanya ta zama tamkar barazana ga rayuwar mu,” in ji wani mazaunin yankin cikin damuwa.

Wannan yanki dai na da muhimmanci wajen samar da hatsi, kayan marmari, da kuma kiwon shanu da raguna, waɗanda su ne ginshiƙin kasuwancin al’umma. Rashin gyaran hanyar na nufin asarar dukiya, wahalar sufuri, da kuma toshe damar tattalin arzikin dubban jama’a.

Jama’a na cigaba da kira ga gwamnati daga matakin ƙananan hukumomi har zuwa jiha, da ta yi gaggawar ɗaukar mataki domin ceton wannan hanya. A cewar su, gyaran wannan hanyar ba kawai taimakon manoma bane, illa kuwa jari ne da zai bunƙasa tattalin arzikin ƙasa baki ɗaya.

Ngurore Community TV
📷Ngurore Community TV Reporter

Ngurore Ta Yi Babban Rashi: Rasuwar Alhaji Musa ‘Yanga (Agogo)A safiyar yau ne muka  tashi cikin jimami  bayan labarin r...
09/10/2025

Ngurore Ta Yi Babban Rashi: Rasuwar Alhaji Musa ‘Yanga (Agogo)

A safiyar yau ne muka tashi cikin jimami bayan labarin rasuwar ɗaya daga cikin dattawan gari, Alhaji Musa ‘Yanga, wanda aka fi sani da Agogo.

Marigayin ya shahara a cikin al’umma da kyawawan ɗabi’u da kuma kasancewa mai kishin jama’a. Tunanin yara da matasa na wancan lokaci ya sanya masa laƙabi da Agogo, saboda kasancewarsa mai jajircewa wajen tsare lokaci da zama abin koyi ga kowa.

Tun daɗewa, jama’ar Ngurore na bayyana shi a matsayin mutumin al’umma, wanda rayuwarsa ta kasance darasi da ƙarfafawa ga ƙarni na gaba.

Daya daga cikin mazauna Ngurore Malam Abu Mustapha S Abubakar ya ce: “Ya kasance mutum mai sauƙin hali, mai ƙaunar mutane da jajircewa wajen jagorantar al’umma da kyawawan dabi’u.”

Za a gudanar da jana’izarsa da ƙarfe 9:00 na safiyar yau, inda jama’a za su taru domin yi masa rakiya ta ƙarshe.

Ngurore Community TV na mika ta’aziyya ga iyalan marigayin da dukkan al’ummar Ngurore. Muna addu’a Allah Ya jikansa da rahama, Ya ba iyalansa haƙuri da juriya, Ya kuma sa mu kasance masu jan darasi daga irin rayuwar kirki da ya rayu.

Ngurore Community TV.
📷Abu Mustapha S Abubakar /Facebook

Ɗan asalin garin Ngurore, Mohammed B. Abubakar (Book Fighter – Nazeer), ya yi nasara a babban zaɓen da aka gudanar a Col...
08/10/2025

Ɗan asalin garin Ngurore, Mohammed B. Abubakar (Book Fighter – Nazeer), ya yi nasara a babban zaɓen da aka gudanar a College of Health and Technology Michika, Mubi Campus.

An zaɓe shi a matsayin Mataimakin Shugaban Ƙungiyar Pharmacy Health Technician Department, inda ya samu goyon baya daga ɗalibai sak**akon jajircewa da nagartar sa.

Wannan nasara ta kara ɗaukaka sunan Ngurore, tare da zama abin alfahari ga iyalai, abokai, da al’umma gaba ɗaya.

Ngurore Community TV na taya shi murna tare da fatan alheri a sabon mukamin jagoranci.

📷 It Real Nazeer/Facebook

LAMIDO ADAMAWA YA ZIYARCI NGUROREMai Martaba Lamido Adamawa, Alhaji Dr. Muhammadu Barkindo Aliyu Musdafa (PhD, CFR), wan...
08/10/2025

LAMIDO ADAMAWA YA ZIYARCI NGURORE

Mai Martaba Lamido Adamawa, Alhaji Dr. Muhammadu Barkindo Aliyu Musdafa (PhD, CFR), wanda shi ne Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya na Adamawa kuma Grand Patron na Tabital Pulaaku International, ya kai ziyara a gonarsa da ke Ngurore a yau da rana.

An tarbe shi cikin girmamawa da farin ciki daga Chiroman Ngurore, Walin Namtari, Babban Limamin Masallacin Juma’a na Ngurore tare da wasu daga cikin masoyansa da magoya bayansa.

📷Khalifa Babagari

08/10/2025

Za,agudanar da jana izan in sha Allah ,da misalin 4:00pm.Akofan gidan Alhaji sule wurodole.Amman in ansami canji zamu sanar

08/10/2025

Allah yayi wa Alhaji Aminu Wurodole rasuwa. Lokacin jana’izarsa za a sanar nan bada jimawa ba. Kamar yadda Mal. Ahmad Modibbo ya wallafa a shafinsa Allah ya jikansa, ya gafarta masa.

NGURORE COMMUNITY TA KARRAMA NEDC ADAMAWA KAN AYUKAN CI GABAAl’ummar Ngurore karkashin jagorancin Hakiminsu, Alhaji Abub...
08/10/2025

NGURORE COMMUNITY TA KARRAMA NEDC ADAMAWA KAN AYUKAN CI GABA

Al’ummar Ngurore karkashin jagorancin Hakiminsu, Alhaji Abubakar Lawan, ta karrama Hukumar North East Development Commission (NEDC) ta Jihar Adamawa da kyautar girmamawa (Award of Excellence) bisa ayyukan raya kasa da ta gudanar a yankin.

An mika wannan lambar yabo ne ga Ko’odinetan Jihar Adamawa na NEDC, Barista Khalifa M. Lawan, yayin da tawagar shugabannin Ngurore ta kai ziyarar ban girmamawa ofishin hukumar a Yola.

Yayin zantawa, Hakimin Ngurore, Alhaji Abubakar Lawan, ya bayyana cewa ziyarar ta kasance domin nuna godiyar al’umma kan manyan ayyukan ci gaba da hukumar ta kawo, wanda s**a inganta rayuwar jama’a a fannoni daban-daban.

“Mutanen Ngurore suna daga cikin masu cin gajiyar ayyukanku kai tsaye. Mun zo ne domin mu ce mun gode sosai,” in ji Hakimin.
“Muna kallon NEDC a matsayin abokin ci gaba na gaskiya wanda ke kula da bukatun jama’a.”

A nasa bangaren, Barista Khalifa M. Lawan ya gode wa shugabannin Ngurore bisa wannan yabo, yana mai cewa karramawar ta kara musu karfin gwiwa wajen gudanar da ayyukan ci gaba a Adamawa.

“Wannan karramawa zai karfafa mana gwiwa mu kara aiki tukuru don ci gaban al’umma,” in ji shi.

Ya kuma bukaci al’ummar Ngurore da su kare da kula da ayyukan da aka gina domin su amfane su da kuma zuri’a masu zuwa.

Taron ya kare cikin nishadi da musayar gaisuwa, wanda ya kara dankon zumunci tsakanin hukumar NEDC da al’ummar Ngurore domin ci gaba mai dorewa.

📷 Miracle Musa Adamawa News Agency

Manu Ngurore Foundation ta KARRAMA MASU DIGIRI.A jiya Lahadi ne, Manu Ngurore Foundation ta shirya liyafa ta musamman do...
06/10/2025

Manu Ngurore Foundation ta KARRAMA MASU DIGIRI.

A jiya Lahadi ne, Manu Ngurore Foundation ta shirya liyafa ta musamman domin taya murna ga Tahir Aminu da Naja’atu Usman bisa nasarar kammala karatunsu a jami’a.

Taron ya samu halartar manyan baki ciki har da Alh. Aminu Mohammed Tahir da Engr. Bashir Buba, tare da jagorancin Alh. Manu Ngurore wanda ya mika kyaututtuka na musamman ga masu karramawa.

Liyafar ta kasance abin tunawa da karfafa gwiwa ga matasanmu.

Ngurore Community TV
📷Manu Ngurore Foundation /Facebook

Address

Ngurore Town, Yola South
Yola

Telephone

+2349035281825

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ngurore Community TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Ngurore Community TV:

Share