Ngurore Community TV

Ngurore Community TV Labarai ll Rahotanni II Al'amuran yau da kullum II Shirye Shirye ll

ARDO WURO-YANKA YA MAYAR DA KUJERAR MAI ANGUWA GA MALAM YUSUF USMAN BIRI A safiyar yau Alhamis al’umma a Wuro-Yanka Ngur...
06/11/2025

ARDO WURO-YANKA YA MAYAR DA KUJERAR MAI ANGUWA GA MALAM YUSUF USMAN BIRI

A safiyar yau Alhamis al’umma a Wuro-Yanka Ngurore sun wayi gari da sabon labari yayin da Ardo Wuro-Yanka, Malam Abdulra’ufu Hamman Tukur, ya dawo wa Malam Yusuf Usman Biri kujerar Mai Anguwa na Sabon Gari Wuro-Yanka.

Wannan dai yana zuwa ne bayan bayan riƙon kwariyar wanna kujerar da aka baiwa malam Abdulrahman Excellency a wattani da s**a gabata.

Tuni dai Malam Yusuf Usman Biri tare tawagar sa ciki harda wakilin sa Habu Babangida s**a kai ziyarar jinjinawa a fadar Ardo Wuro-yanka daga nan s**a zarce zuwa isar da gaisuwa ta mussamman ga Hakimin Ngurore Alh. Abubakar Babbalawan.

Muna Addu'ar Allah ya bamu hadin kai, da cigaba a Ngurore baki ɗaya.

📷Ngurore Community TV

Sakon taya murna ga Mal. Bello Abubakar Ngurore bisa samun ƙaruwa ta ɗa na miji, tuna har an raɗa masa suna Ibrahim.Alla...
05/11/2025

Sakon taya murna ga Mal. Bello Abubakar Ngurore bisa samun ƙaruwa ta ɗa na miji, tuna har an raɗa masa suna Ibrahim.

Allah ya raya ya kuma sanya albarka.

Ngurore Community TV
📷Bello Abubakar /Facebook

Matashi Malam Modi Bappa ya nemi addu'oin  al-ummar Ngurore a yammacin yau Talata, inda suke shirin tashi daga Najeriya ...
04/11/2025

Matashi Malam Modi Bappa ya nemi addu'oin al-ummar Ngurore a yammacin yau Talata, inda suke shirin tashi daga Najeriya zuwa Madina domin gudanar aikin Umrah.

Ngurore Community TV
📷Modi Bappa

A cikin wata tattaunawa mai zafi dake cike da tunani, matasan Ngurore ward sun gudanar da muhawara a cikin WhatsApp grou...
04/11/2025

A cikin wata tattaunawa mai zafi dake cike da tunani, matasan Ngurore ward sun gudanar da muhawara a cikin WhatsApp group na Ngurore Youth Summit, inda s**a tattauna babban matsalar da ke addabar matasa, shaye-shaye da lalacewar rayuwa.

Tattaunawar ta fara ne da Husina Tukur wadda ta bayyana cewa babban kalubalen Ngurore yanzu shi ne shaye-shaye gaskiya, abin da ya tayar da hankali a cikin rukuni. Yakubu Abdulrazak ya mayar da martani da cewa rashin sani da ilimi ne ke jawo yawancin matasa fadawa cikin wannan hali, yayin da Musa Adamu ya jaddada cewa jahilci shi ne tushen shaye-shaye.

MD ya kawo bangaren kwarin gwiwa inda ya ce matasa 75% a Ngurore masu aiki tukuru ne, amma ya nuna damuwa da cewa kashi 65% daga cikinsu ba sa son yin karatu sosai.
Hauwa Umar ta dauki matsayin jagora, ta ce lokaci ya yi da za a shirya wayar da kai kan illar shaye-shaye, musamman ga kananan yara, sannan ta tambayi ko matasan Ngurore za su iya hada kai su fuskanci shugabanninsu cikin gaskiya da tsari.
Umar Yunusa ya bayar da shawarar kafa dokoki da ƙa’idoji na gari don rage yaduwar miyagun kwayoyi, yayin da Joel Akila ya jaddada cewa canji zai fara daga mu kanmu, ba daga gwamnati kawai ba.
Yunusa Abdullahi ya kawo jawabi mai zurfi da ke jan hankali:

“Ba aikin yi kawai muke bukata ba — muna bukatar gaskiya, soyayya da fahimta. Idan muna so mu ci gaba, mu guji abubuwan da ke lalata rayuwarmu.”
Tattaunawar ta kuma karkata zuwa batun ilimi da kwararru a Ngurore, inda Hauwa Umar ta tambayi ko akwai likitoci, lauyoyi, injiniyoyi, manazarta ko manyan jami’an gwamnati daga garin.
Abdullahi Musa da MD sun bayyana wasu kwararru kamar Halidu Dahiru (Chartered Accountant), Abdullahi Dauda (Software Engineer), Abdullahi Maigawa (Educationist), yayin da Umar Yunusa ya ƙara da cewa akwai Farfesa daga Ngurore mai koyarwa a jami’ar ABU Zaria fiye da shekaru goma.

Wannan tattaunawa ta zama tamkar karamin taron manazarta — ta haɗa ra’ayoyi, gaskiya, da mafita, kuma ta nuna cewa matasan Ngurore sun fara gane muhimmancin haɗin kai, ilimi, da gyaran al’umma daga ƙasa.

“Yaki da shaye-shaye aiki ne na kowa — gwamnati, iyaye, malamai, da matasa.”
“Wayar da kai a makarantu da masallatai za ta iya ceci rayuka da dama.”
“Ngurore tana da ƙwararru — lokaci ne da zasu fito su ba da gudunmawa.”

Ku ci gaba da turo ra’ayoyinku, mu hada kai mu gina Ngurore — garin da kowa ke alfahari da shi.

Ngurore Community TV
📷Getty Images

03/11/2025

A cikin wannan shiri na musamman wanda Gambo Halidu Bin Sa'ad ya jagoranta, mun tattauna da Malam Aliyu Babangida Ngurore wanda ya samu gurbin aiki da gwamnatin jahar Adamawa a ɓangaren kiwon Lafiya.

Malam Isma’il Halidu yana sanar da jama’ar al’umma cewa za a gudanar da radin suna ga jaririn da Allah Ya azurta shi da ...
01/11/2025

Malam Isma’il Halidu yana sanar da jama’ar al’umma cewa za a gudanar da radin suna ga jaririn da Allah Ya azurta shi da shi, a gobe Lahadi da misalin karfe 6:00 na safe

Za'ayi raɗin sunan ne a ƙofar gidansu da aka fi sani da Gidan Abbasi, kusa da ƙofan Hakimin Ngurore, a Unguwar Wuro-yanka.

Ana gayyatar ‘yan uwa da abokan arziki da su halarta domin taya murna da addu’a. Allah Ya ba da ikon halarta, amin.

Ngurore Community TV

Matsalar Da Ke Ƙara Kamari a Ngurore da KewayeA cikin ‘yan shekarun nan, al’amuran shaye-shaye sun ɗauki sabon salo da y...
01/11/2025

Matsalar Da Ke Ƙara Kamari a Ngurore da Kewaye

A cikin ‘yan shekarun nan, al’amuran shaye-shaye sun ɗauki sabon salo da ya shafi sassa da dama na al’umma, musamman matasa da mata. Hoto kamar wanda ke sama ya nuna wani yanayi mai tayar da hankali — inda wasu matasa ke cikin mummunan halin shaye-shaye da taɓarɓarewar rayuwa, abin da ke nuna girman kalubalen da ke gaban al’umma.

A binciken da Ngurore Community TV ta gudanar, an gano cewa shaye-shaye tsakanin mata ya karu matuƙa musamman a yankunan karkara da birane. Wasu daga cikin dalilan da ke jawo hakan sun haɗa da talla da rayuwar wahala, rashin kulawar iyaye, tasirin abokai, da kuma damuwar tattalin arziki.

Wata uwa da muka tattauna da ita a Ngurore, ta bayyana cewa:

“Yanzu har ‘ya’yan mata da ake turo su talla suna fara haɗuwa da samari masu shaye-shaye, daga nan ake koya musu abubuwa marasa kyau. Da yawa suna fara da taba sigari ko sukun, daga baya sai su shiga cikin miyagun kwayoyi.”

Masu nazari kan al’amuran zamantakewa sun bayyana cewa yawancin matan da ke fadawa cikin shaye-shaye suna fuskantar matsaloli irin su cin zarafi, rashin karatu, ko kuma kuncin rayuwa. Wannan na nuna cewa shaye-shaye ba kawai matsalar mutum ɗaya ba ce — matsalar al’umma ce baki ɗaya.

Wani jami’in lafiya a yankin ya ce:

“Matsalar ta zama babbar barazana ga lafiyar mata. Wasu suna amfani da abubuwa kamar tramadol, codeine, da kuma taba mai ƙarfi. Wannan yana lalata kwakwalwa da jikinsu gaba ɗaya.”

Ngurore Community TV ta kuma gano cewa, rashin wayar da kai daga gida da makarantu ya taimaka wajen yaduwar wannan dabi’a. A wasu lokuta, ‘yan talla na samun masu amfani da su wajen aikata badala, wanda daga bisani ke jawo su cikin duniyar shaye-shaye da lalata.

Masana na ganin cewa mafita tana cikin haɗin gwiwar iyaye, malamai, hukumomin lafiya da cibiyoyin addini. Ya zama wajibi a wayar da kan matasa da mata kan illolin shaye-shaye, tare da kawo shirye-shiryen gyaran hali da sana’o’i domin mayar da su cikin tafarkin kirki.

“Idan aka bar wannan matsala haka, tana iya lalata gaba ɗaya tsarin rayuwar matasa da mata a yankinmu,” inji wani ɗan jarida daga Ngurore Community TV.

A ƙarshe, wannan batu ba wai na gwamnati kaɗai ba ne — yana buƙatar kowa ya ɗauki nauyi. Domin shaye-shaye ya zama makami mai kashe makomar mata da matasa idan ba a tashi tsaye aka hana shi tun yanzu ba.

Ngurore Community TV
📷GETTY IMAGES

A yau Jumma’a, majalisar Hakimin Ngurore ta tabbatar da nadin Malam Buba a matsayin riƙon kwariya na Sarkin Pawa na Ngur...
31/10/2025

A yau Jumma’a, majalisar Hakimin Ngurore ta tabbatar da nadin Malam Buba a matsayin riƙon kwariya na Sarkin Pawa na Ngurore, bayan dakatar da Malam Danladi AK daga wannan muƙamin.

Malam Buba dai dan uwa ne ga marigayi tsohon Sarkin Pawa na Ngurore, Marigayi Ahmadu, kuma tuni ya fara gudanar da ayyukansa kamar yadda doka da al’ada ta tanada.

Ngurore Community TV
📸 Gambo Halidu Bin Sa’ad


Cocin New Covenant Christian Ministries (NCCM) karkashin jagorancin Apostle Gideon Monday Thomas, na shirya wani gagarum...
31/10/2025

Cocin New Covenant Christian Ministries (NCCM) karkashin jagorancin Apostle Gideon Monday Thomas, na shirya wani gagarumin Salvation, Healing and Miracle Crusade da ake sa ran zai gudana a karshen wannan mako.

Taron, kamar yadda aka tabbatar wa da Ngurore Community TV, zai gudana ne a ranakun Asabar da Lahadi, 1 zuwa 2 ga Nuwamba, 2025, da misalin karfe 3:00 na rana, a Manna Model School, Cemetery Road, kusa da St. Charles Catholic Church, Kwanan Kuka, Mayo Belwa, Ngurore.

Fitattun baki da za su halarta sun haɗa da Prophet Williams Taku daga ƙasar Cameroon, tare da Min. Giftson Clarkson da Min. Doris David a matsayin masu waƙar sujada.

A cikin wata sanarwa da masu shirya taron s**a aika, sun bayyana cewa wannan taron “zai kasance lokaci na musamman na addu’a, warkarwa, da mu’ujizai ta ikon Ruhun Allah.”

Sun kuma ƙara da cewa, “Za a ga abubuwan ban mamaki kamar warkarwar marasa lafiya, ’yantarwa daga danniyar aljanu, da sabuntawar rai ga masu halarta.”

Rahotanni sun nuna cewa shirin ya ja hankalin jama’a daga sassa daban-daban na Ngurore da kewaye, inda ake sa ran hallartar dubban mabiya domin halartar wannan taron mai taken ‘Salvation, Healing and Miracle Crusade.’

Ngurore Community TV
📷 NCCM/Ngurore

Ngurore Community TV na taya Khalifa Bashir Muhammad Tarbiyya Mai diwani  Baraka  da juma'a. Muna yi maka fatan alheri t...
31/10/2025

Ngurore Community TV na taya Khalifa Bashir Muhammad Tarbiyya Mai diwani Baraka da juma'a.

Muna yi maka fatan alheri tare da addu’ar Allah ya albarkaci rayuwarka da aikinka.
Happy Juma’at Mubarak!

Gwanin ban sha’awa!Yadda Dalibai na Central Primary School Ngurore sun gudanar da Assembly na yau Jumma’a cikin tsari da...
31/10/2025

Gwanin ban sha’awa!

Yadda Dalibai na Central Primary School Ngurore sun gudanar da Assembly na yau Jumma’a cikin tsari da natsuwa sosai.

Ngurore Community TV
📸 Ahmad Modibbo /Facebook


30/10/2025

Tsohon kansilan Ngurore Hon. Jibir Abubakar Babbalawan ya bayyana dalilan sa na ficewa daga PDP zuwa ADC

Address

Ngurore Town, Yola South
Yola

Telephone

+2349035281825

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ngurore Community TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Ngurore Community TV:

Share