AMB HAUSA TV

AMB HAUSA TV Shirye Shiryen mu zasu fara zuwa muku nan bada jimawa ba

Wani ɗan kabu-kabu mai suna Hanafi Abubakar ya rasa ransa sanadiyar hatsari da ya yi shi da mai Mota. Hatsarin ya afku n...
07/05/2025

Wani ɗan kabu-kabu mai suna Hanafi Abubakar ya rasa ransa sanadiyar hatsari da ya yi shi da mai Mota. Hatsarin ya afku ne a Gada Biyu, Gusau.

Wannan ita ce motar da Atiku ya bukaci Tinubu ya sauya da mota ƙirar Najeriya. Idan yana so a tabbatar cewa yana son gya...
07/05/2025

Wannan ita ce motar da Atiku ya bukaci Tinubu ya sauya da mota ƙirar Najeriya. Idan yana so a tabbatar cewa yana son gyaruwar Najeriya.

Wannan motar sunanta (Cadillac Escalade-V 2024 ) motar da ake amfani da shi a fadar shugaban ƙasa):

A kasar Amurka Farashinta ya kai dala $154,290

A Farashin Najeriya (da haraji, kwastan:
Ts kaiwa Kusan Naira ₦115,000,000 zuwa ₦130,000,000, bisa yadda aka shigo da ita.

Ya Kamata Iyaye Su Dinga Binciken Wa Ya Kamata Su Baiwa Aurèn Ya'yansuJiya misalin karfe 02:19 na dare na shawo kwana da...
07/05/2025

Ya Kamata Iyaye Su Dinga Binciken Wa Ya Kamata Su Baiwa Aurèn Ya'yansu

Jiya misalin karfe 02:19 na dare na shawo kwana dai dai Court Road kawai na ga wannan baiwar Allah da goyo kuma ga mijinta a baya da bulala yana kora ta wai sai ta tafi gidan iyayen ta a wannan mummunan daren, duk sabida wai ya sa ta ta dafa masa abinci karfe 1:30 na dare ta dora bacci ya dauketa ta mance.

Tabbas wasu mazan idan s**a yi wani aikin ďabba ma ba za ta yi ba, don haka muna Allah wadai da irin wadannan mazan.

Kuma so da dama Wallahi iyaye ke jefa yaransu a hannun irin wadannan jàķan mazan.

Daga Aminu Tura Hadejia

Bayan Kwanaki 40 da faruwar lamarin, yau iyalan mafarautan da aka kashe a Edo S**a gudanar da Zanga-zanga
06/05/2025

Bayan Kwanaki 40 da faruwar lamarin, yau iyalan mafarautan da aka kashe a Edo S**a gudanar da Zanga-zanga

Gwamnan Jihar Katsina da ke arewacin Nijeriya Dikko Umaru Radda ya ce ba su ce wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu babu ƙ...
06/05/2025

Gwamnan Jihar Katsina da ke arewacin Nijeriya Dikko Umaru Radda ya ce ba su ce wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu babu ƙorafi a Katsina ba kamar yadda ake ta muhawara a kai a ƙasar, yana mai cewa sun shaida wa Tinubu manyan matsaloli uku da Katsina ke fama da su.

Matasan APC A Jihar Zamfara Suna Kokawa Kan Cewa Dattawa Yan Shekara 50 Zuwa 60 Sune S**a Wakilci Matasan Jam'iyar APC N...
06/05/2025

Matasan APC A Jihar Zamfara Suna Kokawa Kan Cewa Dattawa Yan Shekara 50 Zuwa 60 Sune S**a Wakilci Matasan Jam'iyar APC Na Jihar Zamfara A Zaman Da Su Kayi Da Dan Dan Shugaban Kasa Sheyi Tinubu Yau A Abuja.

Mi zaku ce ?

Matashi ya halaka Mahaifin shi da Adda a Jigawa.. Rahotannin da Jaridar Taskar Labarai ta samu daga karamar hukumar Gwar...
06/05/2025

Matashi ya halaka Mahaifin shi da Adda a Jigawa..

Rahotannin da Jaridar Taskar Labarai ta samu daga karamar hukumar Gwaram ta jihar Jigawa, ya bayyana yadda rundunar 'yansanda ta Jihar ta damke wani matashi bayan ya kashe mahaifinsa ta hanyar da6a masa babbar wuka da ake kira "Adda"

Hukumar ta tabbatar da cafke matashin mai shekara 20 mai suna Muhammadu Salisu, da ake zargi da daba wa mahaifinsa Adda har ya mutu, inda tuni Kamishinan 'yansandan jihar ya umarci a mayar da binciken lamarin zuwa sashen binciken manyan laifuffuka na jihar (SCID) da ke Dutse..

Wannan mammunar lamarin dai ya faru ne a unguwar Bakin Kasuwa da ke yankin Sara, inda ake zargin matashin mai shekaru 20 ya kai wa mahaifinsa harin da ya jawo rasuwarsa..

Allah shi kyauta...

YANZU-YANZU: Lauyoyi na zanga-zanga a harabar majalisar tarayyar Nigeria domin majalisar ta amshe aikin majalisar dokoki...
06/05/2025

YANZU-YANZU: Lauyoyi na zanga-zanga a harabar majalisar tarayyar Nigeria domin majalisar ta amshe aikin majalisar dokokin Zamfara da Benue.

Nijeriya ita ce kasa ta biyu a duniya da yara milyan 2 ke fama da rashin abinci mai gina jiki - UNICEF.
06/05/2025

Nijeriya ita ce kasa ta biyu a duniya da yara milyan 2 ke fama da rashin abinci mai gina jiki - UNICEF.

Ana zargin wani gardi ya yiwa kolo karamin almajiri dukan koshi da belt din inji har ya yi masa rauni waje-waje, bayan d...
06/05/2025

Ana zargin wani gardi ya yiwa kolo karamin almajiri dukan koshi da belt din inji har ya yi masa rauni waje-waje, bayan da babban malaminsu ya tafi kauye ya bar almajiran nasa a hannun gardin.

Yanzu haka dai gardin Mai suna Adamu Ibrahim da karamin almajirin Ibrahim Abdussalam mai kimanin shekaru goma sha uku, suna hanun hukumar Hisbah sun fara da buncike tare da yunkurin mika batun zuwa hukumar NAPTIP dake dakile cin zarafin mata da kananan yara da Kuma hana safarar mutane.

Alhaji Muhammad Bello Abdullahi Gadon Kaya dake zaman shugaban kungiyar kare hakkin Dan Adam ta Human Right Foundation of Nigeria wanda kuma shi ne ya mika al'amarin zuwa ga hukumar ta Hisbah bayan da s**a yi arangama da yaron a t**i cikin wani hali, ya ce zasu ci gaba da bibiyar al'amarin don ganin an tabbatar da adalci tare da daukar matakin dakile faruwar hakan a nan Gaba.

Yan Adamawa ne Kaɗai Zasu Gane Inane Nan
06/05/2025

Yan Adamawa ne Kaɗai Zasu Gane Inane Nan

Ɗan majalisa  mai wakiltar mazabar Pankshin/Kanam/Kanke a jihar Filato, Hon Yusuf Gagdi,  ya shiga takaddama da wasu man...
06/05/2025

Ɗan majalisa mai wakiltar mazabar Pankshin/Kanam/Kanke a jihar Filato, Hon Yusuf Gagdi, ya shiga takaddama da wasu manyan shugabannin rundunar soji, inda ya bayyana rashin gamsuwarsa da yadda suke gudanar da yaki da 'yan ta'addan Boko Haram.

A cikin wata muhawara mai zafi, dan majalisar ya zargi shugabannin rundunar da gazawa wajen kawo karshen ta’addanci a Arewa maso Gabas, yana mai cewa:
"Tun shekaru da dama ana fada da Boko Haram, amma har yanzu ba a iya murkushe su ba. Wannan ya nuna akwai gazawa ko rashin niyya daga bangaren manyan hafsoshin tsaro.”

Shugabannin sojin da ke halartar zaman sun yi kokarin kare kansu, inda s**a ce ana kokari fiye da yadda ake tunani, kuma akwai ci gaba duk da kalubalen da ake fuskanta.

Wannan fada tsakanin wakilin jama’a da shugabannin tsaro ya sake janyo tambayoyi game da yadda ake tafiyar da yakin da ake da ‘yan ta’adda a Najeriya.

Address

Adamawa
Yola

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AMB HAUSA TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AMB HAUSA TV:

Share