Adamawa Media Forum

Adamawa Media Forum Adamawa Media Forum shafi ne da zai rika kawo abubuwan da s**a shafi harkar musulunci a Nigeria a yankin Adamawa.

An samar da da ita ne bayan cimma matsaya da akayi yayin zama da wakilai inda aka canza suna daga Media Forum Yola zuwa Adamawa media forum

MAJALISIN MAULIDIN AMIRUL MUMININ ALI BIN ABI TALIB (AS) YA ƘAYATAR TARE DA MALAM UZAIRU BADAMASI A GARIN YOLAMasoya sun...
12/01/2026

MAJALISIN MAULIDIN AMIRUL MUMININ ALI BIN ABI TALIB (AS) YA ƘAYATAR TARE DA MALAM UZAIRU BADAMASI A GARIN YOLA

Masoya sun yi tururuwa a wajen Majalisin Maulidin Imam Ali bin Abi Talib (AS), wanda ya gudana a daren jiya Lahadi a cikin ƙwaryar garin Jimeta.

Malam Uzairu Badamasi ne ya kasance babban baƙo kuma mai gabatar da majalisin, a wannan ƙayataccen taro da ’yan’uwa musulmi almajiran Sheikh Ibrahim Zakzaky (H) na da'irar Yola s**a shirya.

Taron ya gudana ne a unguwar Rumde, bayan Local Government, a cikin ƙwaryar Jimeta, Yola, babban birnin Jihar Adamawa.

Ga kaɗan daga cikin hotunan da wakilin mu ya ɗauka a yayin gabatar da taron.

12/01/2026
Adamawa Media Forum

"KULE GA MAGOYA BAYAN ISRA’ILA A WANNAN KASAR..!"_Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) yace;"Su waɗannan magoya bayan nasu a nan,...
12/01/2026

"KULE GA MAGOYA BAYAN ISRA’ILA A WANNAN KASAR..!"

_Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) yace;

"Su waɗannan magoya bayan nasu a nan, mun yi musu wani kaka-kara-kaka, muka ce ga wani kule! Idan muka fito muna goyon bayan ‘yan Palasɗinu, bamu yarda da zaluncin da ake musu ba, to ba bindiga za ku zo ku yi harbi ba. Abin da ya kamata, tunda kuna goyon bayan Isra’iliyawa, sai ku ajiye wata ranar, ba ranar Juma’ar karshen Ramadan ba, sai ku ce wannan kuma ranar Tadamuni ne da al’ummar Isra’ila, kun goyi bayan Isra’ila da ta’asar da suke yi, ku a wajenku daidai ne.

Duk da su fa basu dauke ku matsayin Bil-adama ba. Basu ma dauka ku Mutane bane, a luggarsu ku dabbobi ne ma! Amma dai tunda kuna goyon bayansu, shikenan sai ku ajiye wata rana, kuce duk mai goyon bayan Isra’ila shima sai yazo yayi Muzahara, yace ya goyi bayan Isra’ila, idan yaso ma duk abin da yaso yayi na nuna goyon baya, amma ba zai kai hari a kan wani Mutum ba, ba zai zagi kowa ba, yana goyon bayan Isra’ila ne, illa iyaka. Kun ga shikenan."

-Cikin Jawabin Sheikh Zakzaky (H) na 'Ranar Qudus' ta duniya. 14442023.



23/Rajab/1447
12/01/2026

12/01/2026
DAGA DA'IRAR IBEJU LEKKI, A GARIN LAGOS'Yan'uwa musulmi almajiran Sheikh Ibrahim Zakzaky (H) na Da'irar Ibeju Lekki sun ...
11/01/2026

DAGA DA'IRAR IBEJU LEKKI, A GARIN LAGOS

'Yan'uwa musulmi almajiran Sheikh Ibrahim Zakzaky (H) na Da'irar Ibeju Lekki sun gudanar da Maulidin Imam Ali (AS).

Taron Maulidin Imam Ali (AS) ya gudana cikin daren yau Lahadi, 11/01/2026, a garin Lagos. Taron ya samu halartar masoya daga sassa daban-daban na garin Ibeju Lekki.

Bayan buɗe taron da addu’a da karatun Alƙur’ani Mai Girma, sai aka saurari ƙasida (wake) na yabo ga Imam Ali (AS). Daga bisani aka gabatar da Diwani.

Malam Bashir, limamin Masallacin Ɗariƙa, ya gabatar da jawabi kan Imam Ali da Ahlul Baiti (AS), sai ɗan’uwa Bashir ya yi ta’aliƙi. Daga ƙarshe aka gabatar da addu’a, aka sallami kowa.

🖋️ Musa Muhammad Butu

11/01/2026

KAITSAYE DAGA DA'IRAR YOLA.

MAJALISI TARE DA SIDI UZAIRU BADAMASI KANO .

11/01/2026

SIDI UZAIRU BADAMASI A DA'IRAR YOLA

MAULIDIN IMAM ALI (AS) A DA'IRAR YOLA.A SAFIYAR YAU LAHADI 11-1-2026 WANDA YAYI DAIDAI DA 22, RAJAB 1447AH, YAN'UWA ALMA...
11/01/2026

MAULIDIN IMAM ALI (AS) A DA'IRAR YOLA.

A SAFIYAR YAU LAHADI 11-1-2026 WANDA YAYI DAIDAI DA 22, RAJAB 1447AH, YAN'UWA ALMAJIRAN SHAIKH IBRAHIM ZAKZAKY (H) NA GARIN YOLA S**A SHIRYA GAGARUMIN TARON RANAR TUNAWA DA AMIRUL-MUMININ ALIY (AS) A GARIN JIMETA - YOLA JAHAR ADAMAWA.

Bayan bude taron da Addu'a Sai karatun kur'ani Daga bakin Zainab Dawud Zakariyyah, mawakan masoya Annabi (SAWW) da Iyalan Gidansa S**a raira wakokin ga Imam Ali(AS).

Hujjatul-Islam Shaikh Muhammad Gidado Hamman ya kasance mai gabatar da jawabi a muhallin taron. wanda ya gudana a babban dakin taro na U.B.E dake garin Yola.

A Karshe, Malam Muhammad Gidado ne ya rufe taron da Addu'a bayan isar da sakonnin Mu'assasatush-Shuhada daga bakin wakilansu.

Taron zai cigaba da gudana da misalin Karfe 7:00 na daren yau a unguwar Rumde Bayan Local Government

.
.

© Usamatu Yola/ Muhammad Al-Amin Auwal (ElmaaYola).
®ADAMAWA MEDIA FORUM(AMF).

MAULIDIN IMAM ALI (AS) A DA'IRAR YOLA.A YAU LAHADI 11-1-2026  YAN'UWA ALMAJIRAN SHAIKH IBRAHIM ZAKZAKY (H) NA GARIN YOLA...
11/01/2026

MAULIDIN IMAM ALI (AS) A DA'IRAR YOLA.

A YAU LAHADI 11-1-2026 YAN'UWA ALMAJIRAN SHAIKH IBRAHIM ZAKZAKY (H) NA GARIN YOLA S**A SHIRYA GAGARUMIN TARON RANAR TUNAWA DA AMIRUL-MUMININ ALIY (AS) A GARIN JIMETA - YOLA JAHAR ADAMAWA.

TUNI AN FARA GABATAR DA MAULIDIN INDA YAN'UWA S**A MAHALARTA, INDA YANZU HAKA MAWAKA MASOYA IYALAN GIDAN MANZON ALLAH SUKE GABATAR DA WAKOKIN IMAM ALI(AS)

.
.
®ADAMAWA MEDIA FORUM(AMF).

📢 BUDADDIYAR GAYYATA 📢DAGA RUGAR FULANI (KAUTAL KO'IE JULƁE) 🌿 ZUWA GA ƊAUKACIN AL'UMMAR JIHAR ADAMAWAYan’uwa Musulmi Fu...
11/01/2026

📢 BUDADDIYAR GAYYATA 📢
DAGA RUGAR FULANI (KAUTAL KO'IE JULƁE) 🌿

ZUWA GA ƊAUKACIN AL'UMMAR JIHAR ADAMAWA

Yan’uwa Musulmi Fulani, waɗanda aka fi sani da Kautal Ko'ie Julɓe, ƙarƙashin jagorancin Sheikh Ibrahim Zakzaky (H) na Da’irar Yola, suna farin cikin gayyatar ɗaukacin al’ummar Jihar Adamawa gaba ɗaya zuwa:

🌸✨ GAGARUMIN TARON MAULIDIN IMAM ALI DA SAYYIDA FATIMA AZ-ZAHRA (SA) ✨🌸
wanda ake gabatarwa duk shekara.

Taron zai gudana ne kamar haka:
🗓️ Rana: Talata, 14 ga watan Janairu, 2026
⏰ Lokaci: 10:00 na safe
📍 Wuri: Rugar Fulani

🤲 Muna roƙon Allah (SWT) Ya ba da ikon halarta. Amin 🤍

🖋️ Adamawa Media Forum

“Kun ga Allah (T) yadda ya tsinewa Fir’auna, yace: “Inna Fir’auna Ala Fil-ard wa ja’alaha shiya’an yastad’ifu da’ifatan ...
11/01/2026

“Kun ga Allah (T) yadda ya tsinewa Fir’auna, yace: “Inna Fir’auna Ala Fil-ard wa ja’alaha shiya’an yastad’ifu da’ifatan minhum yuzabbihuna abna’ahum wa yastahyi nisa’ahum, innahu kana minal mufsidin." "Wa nuridu anna munna alal-lazinas-tad’ifu fil-ard wa naj’alahum a’immatan wa naj’alahumul warisin.” “Wa numakkina lahum fil-ard wa nuriya Fir’auna wa Hamana wa junudahuma minhum ma kanu yahzarun.”

To Fir’auna ya raba kasa, ya raunana wasu, ya daura wasu a kan wasu, yace wadannan sunansu Kibɗawa, wadannan sunansu Isra’iliyawa. Yana yanka ‘ya’ya maza na Isra’iliyawa. To Allah (T) kuma yana son yayi tagomashi ga waɗanda ake zalunta, ya nunawa Fir’auna da Hamana da rundunoninsu cewa wannan abin da suke gudu zai same su. Kuma abinda ya faru kenan, karshe sai da Allah Ya gusar da Fir’auna, da Hamana da mulkinsu, kuma Ya taimaki wanda ake zalunta.

To yanzu irin wannan ne zai faru, kuma wannan ayar ma da yawa masu fassara suna fassara “Wa nuridu anna munna alal lazinas-tad’ifu fil-ard wa naj’alahum a’immatan wa naj’alahumul warisin.” Cewa da bayyanan Imam (Atfs) ne. Cewa lokacin bayyanar Imam (Atfs) insha Allah, waɗanda ake zalunta Allah zai yi tagomashi garesu, ya nuna wa Fir’auna da Hamana, wanda su ramzi ne na duk azzalumai, wannan (lokacin) sai ya nuna ma Amerika da Burtaniya da ire-irensu abin da suke gudu. Insha Allahul Azeem wannan rana tana tafe, muna fatan Allah (T) ya gaggauta bayyanan wanda da bayyanansa ne za a samu mafita.”

—Cikin Jawabin Shaikh Zakzaky (H) na nuna goyon bayan al'ummar Palasdinawa a Ramadan 1445 (2024).



22/Rajab/1447
11/01/2026

A shekara  #1200 kacal akace ka bayar.Muna saka katin nawa ?Datan nawa ?Ya kamata muyi tuna.
10/01/2026

A shekara #1200 kacal akace ka bayar.

Muna saka katin nawa ?
Datan nawa ?

Ya kamata muyi tuna.

Address

Jimeta
Yola

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Adamawa Media Forum posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share