Media Forum Yola

Media Forum  Yola Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Media Forum Yola, Media/News Company, Jimeta, Yola.

Welcome to Media Forum Yola
This platform shares the message of the Islamic Movement under Sheikh Ibrahim Zakzaky (H), focusing on Yola and Adamawa.

📢Follow us to stay updated on the Islamic Movement in Yola Zone and throughout the country.

KIRAN SHEIKH IBRAHEEM ZAKZAKY KAN ZAMAN LAFIYA DA HAƊIN KAI TSAKANIN MUSULMAI DA KIRISTOCISheikh Ibraheem Yaqoub Zakzaky...
07/11/2025

KIRAN SHEIKH IBRAHEEM ZAKZAKY KAN ZAMAN LAFIYA DA HAƊIN KAI TSAKANIN MUSULMAI DA KIRISTOCI

Sheikh Ibraheem Yaqoub Zakzaky (H) jagoran Harkar Musulunci, yana daga cikin fitattun malaman da s**a shahara wajen kira zuwa zaman lafiya, adalci, da haɗin kai tsakanin al’umma daban-daban a Najeriya da Afirka baki ɗaya. A cikin wa’azozinsa da sakonninsa da dama, malamin ya jaddada cewa al'umma ba za su zauna lafiya ba sai idan Musulmai da Kiristoci sun fahimci juna, sun yi adalci, sun guji ƙiyayya da rikicin addini.

Kiran Sheikh Zakzaky ga Haɗin Kai

A lokuta daban-daban, Malam Zakzaky ya sha bayyana cewa: “Ba addini ne matsalar Najeriya ba, rashin adalci ne. Idan gwamnati ta yi adalci, Musulmi da Kirista za su zauna lafiya, domin babu addinin da ke koyar da zalunci.”

Ya ƙara da cewa: "ƙiyayya tsakanin addinai tana da tushe a siyasa, ba a cikin Musulunci ko Kiristanci ba". A cewarsa, wasu ne ke amfani da bambancin addini wajen raba jama’a domin cimma manufofin siyasa.

Sheikh Ibrahim Zakzaky Da Kiristoci

Sheikh Zakzaky ya yi fice wajen tattaunawa da manyan shugabannin Kirista a cikin ƙasarnan. A cikin wani jawabinsa da ya gabatar a Zaria, ya ce: “Kiristoci abokanmu ne a ƙasa ɗaya. Manzon Allah (S.A.W) ya koyar da mu girmama mutanen littafi. Don haka, babu hujjar ƙiyayya da su.”

Haka kuma, ya jaddada cewa: "ƴan'uwa Kiristoci suna da haƙƙi iri ɗaya da Musulmi wajen samun tsaro, ilimi, da walwala a ƙasa."

Tsokaci kan Rikicin Addini a Najeriya

Malam Zakzaky na ganin cewa rikice-rikicen da ake kira "na addini” a arewacin Najeriya suna da alaƙa da manufofin ɓarna na ƙasashen waje da kuma rashin adalci a cikin gida.

A wani kalaminsa ya bayyana cewa: “Wasu ƙasashe na yamma suna son su raba Musulmi da Kiristoci domin su ci gaba da mulkar tattalin arzikinmu. Amma idan muka fahimci makircinsu, za mu zauna lafiya mu yi nasara tare.”

Irin Wa’azinsa a Fannin Zaman Lafiya

Sheikh Zakzaky (H) ya sha yin kira ga almajiransa da mabiya su guji tashin hankali, har ma wata rana yake cewa: “Ku zama masu sauƙi da biyayya ga dokokin Allah. Kada ku ɗauki makami ko ku shiga rikicin addini. Gaskiya askiya da adalci su ne makamin Musulmi.”

A cewarsa, ƙauna da mutuntawa ne ginshiƙin kowace al’umma. Don haka, duk wanda yake son samun zaman lafiya, dole ne ya gina rayuwarsa a kan gaskiya, adalci da haƙuri.

Sakonsa Ga Duniya

A cikin sakonsa ga duniya, musamman bayan wasu ƙasashe na yamma sun zargi Musulmi da “ƙin jinin Kiristoci,” Malam Zakzaky ya ce: “Ba Musulunci ke haifar da rikici ba. A zahiri, Musulunci yana koyar da mu zaman lafiya, da kare haƙƙin ɗan Adam ko Musulmi ne ko ba Musulmi ba.”

Ya kuma yi kira ga kafafen yaɗa labarai na duniya su daina yaɗa ƙarya da ke neman raba al’umma.

Daga ƙarshe, Sheikh Ibraheem Zakzaky yana daga cikin manyan malaman da ke gina gada tsakanin Musulmi da Kiristoci ta hanyar kira zuwa adalci, fahimtar juna da zaman lafiya.

Kalamansa sun zama tushe mai ƙarfi na yaki da fitina, da ɗora al’umma kan tafarkin haɗin kai.

“Zaman lafiya ba zai tabbata ba sai idan muna son juna saboda Allah, ba saboda ƙabilanci ko addini ba," In ji Sheikh Ibraheem Zakzaky.

Zaman lafiya yana farawa ne daga zuciya. Sheikh Zakzaky ya nuna cewa idan zuciyarmu ta cika da ƙauna da adalci, to Najeriya za ta zama ƙasa ɗaya, mai albarka ga kowa Musulmi da Kirista, Arewa da Kudu, ya k**ata Musulmi da Kirista su gane Turawa arzikin ƙasarmu ne a gabansa ba mu ba.

Wata rana Marigayi Mai Tama Sule (Ɗan Masanin Kano) ya taɓa cewa sun je waje don nemawa Najeriya tallafi sai wani Bature ke nuna masa ba mutane ke nuna masa ba damuwarsa mutanen Najeriya ba, damuwarsu arzikin da ke kasarmu kuma za su iya yin duk mai yiwuwa wajen ganin sun mallaki arzikinmu.

Allah ya zaunar da ƙasarmu lafiya ya haɗa kanmu gaba ɗaya.

Rubutawa: Abubakar Yusuf
Youth Forum Media Team
Shahen Marubuta
0 7 — 1 1 — 2 0 2 5

RANAKUN JUYAYI A YOLA: ALMAJIRAN SHAIKH ZAKZAKY SUN KAMMALA ZAMAN TUNAWA DA SAYYIDA FATIMA AZ-ZAHRA (SA)A daren Alhamis,...
07/11/2025

RANAKUN JUYAYI A YOLA: ALMAJIRAN SHAIKH ZAKZAKY SUN KAMMALA ZAMAN TUNAWA DA SAYYIDA FATIMA AZ-ZAHRA (SA)

A daren Alhamis, 15 ga watan Jumadal-Ula, 1447 Hijira, almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) na Da’irar Yola s**a kammala zaman juyayin shahadar Sayyida Fatima Az-Zahra (S), wanda ya gudana tsawon kwanaki uku.

Hujjatul Islam, Sheikh Muhammad Gidado Hamman ne ya gabatar da jawabai a yayin taron, inda ya tabo fannoni daban-daban na rayuwar Sayyida Zahra (S) da irin musibobin da ta fuskanta a rayuwarta.

An kuma gudanar da Du’a’ul Khumail tare da wasu addu’o’i na musamman domin kammala zaman, a harabar Masallacin Juma’a na Nassarawo da ke garin Jimeta, Jihar Adamawa.

Taron ya kasance wani ɓangare na Ayyam Fatimiyyah, inda mabiya ke tunawa da rayuwa da shahadar Sayyida Zahra (S) cikin nutsuwa da ibada.



(07/11/2025)

Jagora (H) Ya Gabatar Da Zaman Juyayin Shahadar Sayyida Zahra (SA)Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky OfficeDa yammacin...
06/11/2025

Jagora (H) Ya Gabatar Da Zaman Juyayin Shahadar Sayyida Zahra (SA)

Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky Office

Da yammacin Laraba 14 ga Jimadal Ula, 1447 (daidai da 5/11/2025) ne Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya gabatar da jawabin tunawa da Shahadar Sayyida Fatima Azzahra (SA), a gidansa da ke Abuja.

Shaikh Zakzaky ya fara da taya jaje ga mahalartan zaman juyayin, wadanda s**a fito daga sassa daban-daban na kasar nan. Yace: “Zan fara da taya mu jajen musibar da ta auka ma gidan Manzon Rahma (S). Bayan rashin Manzon Allah din, da kuma duk abubuwan da aka yi, sannan karshe ya karata da shahadar Sayyidatu Nisa’il Alamin (SA), wanda ya auku, za mu iya cewa a rana mai k**ar ta yau.”

Ya bayyana Shahadar Sayyida Zahra (S) da abubuwan da s**a faru kafin Shahadarta a matsayin “Musiba babba da ta shafi al’umma gabadaya, musamman ma magoya bayan iyalan gidan Annabi (S).” Yace: “Domin su s**a san da musibar, su kuma s**a san irin abinda ya samu al’umma sak**akon wannan abin, a yayin da mafi yawan ‘yan al’ummar ba su san da wannan ba. Ba kawai basu san da shi ba, akwai ma wadanda suke musanta aukuwarsa.”

Jagora ya yi bitan falala da darajar Sayyida Zahra (S) wanda Manzon Allah (S) yace, “Ita ce shugaban matan Aljanna.” Yace, don haka ta fi duk matan talikai daraja. “Ka ga ace, al’umma gabadaya ta jahilceta, bata santa ba, wannan ba karamin musiba ba ne.”

Jagora ya bayyana dalilin yin jajen Shahadar Sayyida Zahra (S) a lokuta daban-daban, musamman a tsakiyar watan Jimadal Ula da kuma a uku ga watan Jimadat Thani, inda yace, hakan saboda ruwayar da aka samu ne wanda aka kasa bambance kwanaki 75 ne, ko 95 ake nufi tsakanin wafatinta da na Babanta (S), saboda yanayin rubutun zamanin da, wanda bashi da dige-dige.

Shaikh Zakzaky ya bayyana yadda wadanda s**a zalunci Sayyida Zahra (S) s**a bayyana manufarsu na yin wannan aikin a sarari ba tare da boyewa ba, shi ne kare muradin mulkinsu. Inda ya nuna mamakinsa ga wanda suke kokarin basu uzuri akan abubuwan da s**a yi wanda yake k**ar hasken rana.

Jagora ya yi bitan ta’annutin da aka yi ga Sayyida Zahra (SA) bayan wafatin Babanta (S), inda aka kai hari, aka cinna wuta a kofar gidanta, aka caka mata karfen da ke tokare kofa, ya karya kashin awazanta, har ta yi barin cikin da take da ita, tare da marinta, da k**a mijinta da sunan kai shi ya yi bai’a ga Khalifa. Inda Jagora ya bayyana cewa, abu ne tabbatacce da idan mutum ya bincika zai gani, kar a ce Shi’a ne s**a rubuta.

Ya kuma ba da amsa ga masu cewa, ya za a ce an mata haka a gaban Ali, alhali shi jarumi ne? A nan ne ya yi bitan irin wasiyoyin da Manzon Rahma (S) ya yi ga Amirulmuminin Ali (AS), inda ya bashi labarin abubuwan da za su faru da shi a bayansa, har ta kai ma ga Amirulmuminin kan fadi abut un kafin ya faru, saboda wannan masaniyar, da kuma yi masa wasiyya akan yin hakuri. Yace: “Manzon Allah ya umurce shi, yace mashi ya daure, ya bashi labarin duk abinda zai faru sanka-sanka.”

Ya kara da cewa, “Duk abinda ya farun nan gabadaya an gaya masa, kuma an ce ya daure. Daurewan da ya yi ne kuwa ya sa s**a iya (masa hujumin). Shi yasa suke cewa, ai shi an masa wasiyya, kuma ba zai kauce ma wasiyyar Annabi ba, ko me muka yi masa ba zai rama ba.”

Jagora ya kuma karanto yadda aka yi mata janaza, aka bizne ta da daddare,bisa wasiyarta ga Amirulmuminin (AS) akan kada ya yarda wadanda s**a zalunce ta su yi mata sallah. Yace: “Don haka Imam Ali tare da mutum shida, su bakwai s**a yi mata sallah. Har ma a ruwaya ya zo cewa, su wadannan da s**a tsaya tare da Ali aka yi sallah din nan daga sahabbansa, albarkacinsu ake yin ruwan sama. Har ma in ana wuyan ruwa, in aka yi tawassuli da su, to yanzu sama za ta yi ruwa.”

Ya jaddada jaje akan yadda ya zama an boye kabarin Sayyida Zahra (SA) saboda tsoron cutar da ita, tunda akwai wadanda s**a yi yunkurin a nuna musu su hako su mata sallah, wanda a nan ne Amirulmuminin ya zare musu takobi. Yace: “Ba wanda ya san inda kabarinta yake, har izuwa yanzu din nan. Sai dai in danta Imam (AJ) ya zo, zai nuna inda aka bizne mahaifiyarsa. Amma har yanzu a boye yake.”

Da yake ba da amsa ga masu ganin cewa, tarihin wani abu ne da ya wuce, ko babu bukatar tunawa da shi. Shaikh Zakzaky yace: “Ku baku san irin musibar da ya dubi al’ummar nan sak**akon wannan ba? Sak**akon wannan ne wannan al’umma ta fada cikin musibar da ta fada har yanzu.”

Ya kara da cewa: “In kuma ka ce mana, ai tarihi ne, a bar shi ya wuce. Sai mu ce maka in haka nan ne kuma, ai komai ma, har addinin ma gabadaya sai a tattara a bar shi, don tarihi ne. Kuma tunda addinin ta wajensu ya gangaro mana, to lallai abinda ya faru a tsakaninsu, dole ya shafi addinin.”

Yace: “Na shan fadan cewa, muna tsakanin tsoro biyu; tsoron boye gaskiya, da tsoron fitinar mutane. Za ka boye gaskiya ne? Ko kuwa za ka fadi gaskiyan ne mutane su fitinu?” Yace: “sai ka yi baina-baina. Baka yi boye gaskiya ba, baka kuma fitini mutane ba. Wanda ke bukatar shiriya, in yana son ya shiriya, k**ata ya yi ya bi ta hanya a hankali har ya fahimta, ba nan da nan da ya ji abu ya yi fada da abin ba.”

Ya kuma yi nasiha ga mabiya tafarkin Ahlulbaiti (AS) akan bin wasiccin Amirulmuminin (AS) na yin magana da mutane daidai da hankalinsu. Inda yace: “Wasu suna ganin k**ar burgewa ne su fadi maganar gatsar. Kuma su kansu in ma sun shiriya, inda wannan gatsal din aka musu, da basu shiriyan ba. Saboda haka dole ka yi magana da mutane da tausayi. Ba burgewa ne ka fadi magana gatsal ba.”

Yace: “Ana kokari a shiryatar da mutane ne, ba a batar da su ba. In ya zama yadda baka iya magana ba, ka yi maganar da ya zamana sanadiyar wani maimakon ya shiriya ya bace, kana da laifi, domin Manzon Rahma (S) da kyakkyawan usulubi ya isar da sako ga mutane, har yana magana da mutane marhala-marhala ne, yana magana da mutane da daidai gwargwadon darajojin fahimtarsu.”

Don haka ya bukaci a sanya lura da dabara wajen sanar da al’umma Mazlumiyar Ahlulbait (AS) maimakon yi masu baro-baro. Yace: “Ka san wani lokaci in kana gaya ma mutum magana, in ka gaya masa gatsal, ba ganewa zai yi ba, gara ka ahhala shi, shi ya gano da kansa, sai ya fi fahimta.”

Ya kuma yi nasiha akan al’umma da su guji musanta abinda suke ji na zaluntar Ahlulbaiti (AS) da aka yi, inda ya yi kira ga wadanda suke da damar bincikawa kan su bincika ne su gano gaskiya, don su yi riko da sahihin addini. “Wasu da zaran an ce musu ga abinda ya faru, ina! Ai sai fada da zage-zage. Kaga sun dode kofar su fahimci komai.”

A karshe, Jagora ya jaddada godiyarsa ga Allah Ta’ala da tagomashin da ya mana na fahimtar hakikanin sahihin addini, da ilimin da Manzon Rahma (S) ya bari, wanda duk da an yi kokarin rufe shi don kokarin tabbatar da mulkin wasu mutane, amma Allah Ya nufa a sani.

Da yake bayani dangane da darussan da ake dauka daga tunawa da Masa’ib din Ahlulbaiti (AS), Jagora ya bayyana cewa: “Darussan da ke tare a cikin tuna Musibobin Ahlulbaiti (AS) yana da yawa. Na farko, kun ga muna raya al’amarinsu. Kun ga muna kara son su. Kun ga muna koyon dauriya daga gare su. Kuma muna koyon turjiya, mu cije akan abinda s**a ba da rayukansu akai.”

Ya kara da cewa: “Za ka ganmu ƙyam-ƙyam-ƙyam! Har wasu suna cewa za su kwaikwayo mu. Ina ku ina kwaikwayonmu? Wane ku nan! Mu k**a hanyar Ahlulbaiti (AS), ka zo ka yi irin namu? Ƙarya kake, ba zai yiwu ba! Kai da Musibar wane ne za ka tuna ka dake?” Ya tambaya.

Yace: “Wanda suke bin Ahlulbaiti (AS) su ne za su iya dakewa. Amma kuma kun san a cikin mabiya din, ba kowane ne mabiyi ba fa. Don Imam Jafarus Sadiq (AS) ya yi gaskiya da yace, ‘akwai masoyanmu, akwai masu ci da sunanmu.’ To masu ci da sunan Ahlulbaiti su ma in s**a danna a guje, sai sun fi sauran ‘yan Ƙungiya ma zubawa a guje, saboda su suna son su ci da sunan Ahlulbaiti ne. Allah Ya sa mu cikin masoya, ba maciya da sunan Ahlulbaiti (AS) ba.”

A karshe, Jagora (H) ya yi addu’a akan Allah Ta’ala Ya yi maganin masu wa al’ummar kasar nan barazanar za su zo su yi kashe-kashe da sunan baiwa Kiristoci kariya. Yace: “Allah Ta’ala Ka yi mana maganin Trumpopi da na can, da na gida, don a nan ma muna da Trumpopi. Allah Ka yi mana maganinsu. Allah Ta’ala muna rokonka, duk mai neman al’ummar Musulmi da sharri, Allah ka maida masa sharrinsa. Allah Ka daukaka Musulunci ka kaskanta Kafirci. Ka sa mu cikin jumlar wadanda za ka yi amfani da su wajen dawo da addinin nan. Ka bamu dauriya ka sa mu dake, har izuwa samun nasara, ko kuma mu cika kafin nasara. Ka gaggauta bayyanar wanda da bayyanarsa ne za a samu mafita. Ka saka mu cikin dakarunsa, in mun mutu kafin lokacin ka dawo da mu. Bi hakki Muhammadin wa alihid Dahirin.”

https://harkarmusulunci.ng/jagora-h-ya-gabatar-da-zaman-juyayin-shahadar-sayyida-zahra-sa/

GAYYATA ZUWA TARON  MAKON IMAM ALI (AS) Dandalin Matasan Harkar Musulunci ƙarƙashin jagorancin Sayyid Ibraheem Yaqub Zak...
06/11/2025

GAYYATA ZUWA TARON MAKON IMAM ALI (AS)

Dandalin Matasan Harkar Musulunci ƙarƙashin jagorancin Sayyid Ibraheem Yaqub Zakzaky (H) na farin cikin gayyatar ɗaukacin Matasan Harƙa Islamiyya zuwa taron "Makon Imam Ali (AS)" karo na biyu, tare da Mu’utamar “Amm” wanda s**a saba shiryawa karo na 37.

Wannan karon, taron zai gudana ne tsawon mako guda, inda aka zo da sabbin tsare-tsare waɗanda s**a haɗa da: karatuttuka, tattaunawa, wasanni, kyautata mu’amala tsakanin ‘yan uwa, da sauransu.

Akwai manyan malamai gami da masana da zasu gabatar da jawabai da tattaunawa akan maudu’ai daban-daban da s**a shafi ci gaban matashi a mahangar Harƙa Islamiyya.

Taken Taron:
“Gina Shaksiyyar Matashi Ɗan Gwagwarmaya Tare da Kusanto da Ƴaƴan ‘Yan Uwa Zuwa ga Harka Islamiyya.”

Tsarin Taron:
🗓 Rana: Litinin 9 ga watan Rajab zuwa Juma’a 13 ga watan Rajab
📅 Daidai da: 29 ga Disamba zuwa 02 ga Janairu, 2025.

Kuɗin Rajista:
👬 Brothers & Sisters: ₦5,000 (Naira Dubu Biyar)

Za a rufe rajista a ranar 20 ga watan Disamba (29 ga Jimada Thani), kwanaki goma kafin fara taron.
Ana roƙon duk wanda zai halarta da ya kammala rajistar sa kafin wannan lokaci.

Mun fitar da Google Form domin fara "Online Registration."
📱📎
https://forms.gle/4a5SU1B63pjiJ3Ny6

Domin tuntuɓa: 08140748841, 08179589825, 09061411874, 07035266571, 08035333179, 08083940490.

Sanarwa:
Youth Forum Media Team
0 2 — 1 1 — 2 0 2 5.

SABON TSARIN SAMAR DA MURYA GUDA A FACEBOOKKwamitin yaɗa labarai (Media Forum) na Harkar Musulunci na sanar da dukkanin ...
05/11/2025

SABON TSARIN SAMAR DA MURYA GUDA A FACEBOOK

Kwamitin yaɗa labarai (Media Forum) na Harkar Musulunci na sanar da dukkanin wakilai cewa; kowanne gari su samar da murya ɗaya wacce za ta riƙa yaɗa labarai da rahotanni na wannan yanki k**ar yadda yake bisa tsarin Harkar Musulunci a maimaikon muryoyi barkatai kuma birjik da ake da su a yanzu.

Alal misali Zariya su samar da murya ɗaya da zai rika yaɗa labarai da rahotanni na Zariya, Kidandan, Soba, Kudan, da sauran su a maimakon muryoyi barkatai. Sannan su fitar da tsarin sanya labarai da rahotanni da ayyukan kowanne garuruwan da suke haɗe domin bai wa kowa haƙƙinsa. A don haka za su haɗu ne su yi aiki tare.

Haka ma Kaduna, Kano, Bauchi, Yola, Potiskum, da sauran manyan garuruwa (k**ar yadda aka sanar da su aka kuma tura musu tsarin). A bisa haka, k**ar yadda aka tsara, ba a yarda a samar da murya fiye da ɗaya ba daga yanzu da sunan Harkar Musulunci daga garuruwa.

Kowanne yanki na Media, su yi zama domin samar da sunan da zai wakilce su.

Sannan ba a lamunce samar da shafi da sunan Media Forum na Harkar Musulunci ba; sai wannan guda ɗaya da aka sanya wa suna da 'Media Forum of the Islamic movement’ wanda za a iya samun shi a shafin Facebook.

Wannan yana ɗaya daga cikin matakan da kwamitin Media Forum ya ɗauka domin daƙile masu kutse da sunan Harkar Musulunci daga garuruwa a shafin Facebook.

Kazalika, Media Forum ta jaddada aniyarta na tsaftace shafukan dake yaɗa labarai da rahotanni da ayyukan Harkar Musulunci a nan Facebook.

Sanarwa:
-Kwamitin Dandalin Yada Labarai (Media Forum) na Harkar Musulunci

5/11/2025

Shaikh Zakzaky Ya Ce Rikicin Sudan Aiki Ne Na Biyan Buƙatar Ƙasashen Waje, Ya Nemi Haɗin Kai A Tsakanin Ɓangarorin Da Ke...
05/11/2025

Shaikh Zakzaky Ya Ce Rikicin Sudan Aiki Ne Na Biyan Buƙatar Ƙasashen Waje, Ya Nemi Haɗin Kai A Tsakanin Ɓangarorin Da Ke Yaƙi

Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky, ya bayyana rikicin da ake yi a Sudan a matsayin abin takaici da ke faruwa saboda tsoma bakin ƙasashen waje masu neman cin moriyar Sudan. Ya ce rikicin da ke tsakanin Sojojin Sudan da dakarun Rapid Support Forces (RSF) ba ya amfanar al’ummar Sudan, sai waɗanda suke amfana da albarkatun ƙasar.

Da yake bayani a cikin wata hira da Iran Press, Shaikh Zakzaky ya nuna takaici kan yadda ɓangarorin biyu da ke gaba da juna su s**a kasance ‘ya’yan ƙasa guda, amma kuma suke kashe juna. Ya bayyana damuwarsa kan yadda ake samun hatta ‘yan uwa daga iyaye ɗaya suna tsayawa a ɓangarori mabambanta suna hallaka juna saboda biyan buƙatar wasu. “Kana ganin ‘yan uwa suna kashe kansu don amfanin wasu,” in ji shi.

Shaikh Zakzaky ya bayyana cewa kowacce ƙasa tana buƙatar gwamnati ko hukuma da ke wakiltar muradunta gaba ɗaya. Ya ce a asali, RSF an kafa ta ne domin taimaka wa sojojin ƙasa wajen kare jama’ar Sudan, ba don shiga yaƙi da juna ba. Ya zargi ƙasashen waje da ƙara rura wutar rikicin, inda ya ce, “Tabbas, Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) ba ta yin wannan aiki don kanta, tana yi ne saboda ƙasashen yamma.” Ya ƙara da cewa muddin irin wannan kutse daga waje ya ci gaba, rikicin ba zai ƙare ba, kuma al’ummar Sudan za su ci gaba da zama cikin uƙuba da tashin hankali.

Shaikh Zakzaky ya kuma yi Allah wadai da kisan kiyashin da aka yi a yankin Darfur a kwanan nan, inda aka ruwaito cewa mata da ƙananan yara ma ba su tsira ba. Ya kwatanta wannan kisan da abin da sojojin Sahyoniyawa ke yi wa Falasɗinawa, yana mai cewa wannan ma ya fi ciwo saboda “Ƴan Sudan ke kashe ƴan Sudan.”

Daga ƙarshe, ya nemi shugabanni da al'ummar Sudan su kawo ƙarshen wannan yaƙi, su haɗa kai domin amfanin ƙasar su. “Lokaci ya yi da za su gane cewa yaƙar juna saboda son ran wasu ba zai kawo ci gaba ba, sai dai lalacewa. Ya k**ata su haɗa kai don kare ƙasar su,” in ji Shaikh Zakzaky, yana mai kira da a kawo ƙarshen tasirin ƙasashen waje tare da sake farfaɗo da haɗin kan ƙasa.

Kar Ku Yarda A Haɗa Ku Rigima Da Juna— Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky ga Musulmi da Kiristan da s**a ziyarce shi. Jagora...
05/11/2025

Kar Ku Yarda A Haɗa Ku Rigima Da Juna

— Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky ga Musulmi da Kiristan da s**a ziyarce shi.

Jagora (H) ya yi kira ga al'ummar unguwar Nasarawan Kaduna da cewa, kar su yarda a hada su rigima da junansu, ko da da wane irin abu za a kira rigimar.

Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky ya yi kiran ne a yayin da mutanen unguwar ta Nasarawa daga garin Kaduna, wadanda s**a hada da Musulmi da Kirista, s**a ziyarce shi a gidansa da ke Abuja, a ranar Talata 13 ga Jimadal Ula 1447 (4/11/2025), k**ar yadda shafin ofishinsa ya ruwaito.

Shaikh Zakzaky ya bayyana cewa: "Ko da sunan addini, ko da sunan ƙabila (aka bullo aka yi kokarin hada ku faɗa), kar ku yarda, ku haɗe kai, ku zauna lafiya.”

Cikin maziyartan akwai Mista Zakari, wakilin Ƙungiyar Kiristoci ta Ƙasa (CAN) a Ƙaramar Hukumar Chikun. Da Alh. Aliyu Mai Lafiya, Chiroman Nasarawa. Sai Mista Dominic, babban Paston Catholic Church da ke unguwar Nasarawa, da kuma Alaramma Shaikh Jabir Muhammad, babban Limamin Masallacin Juma'a na Nasarawa, da sauran abokan rakiyarsu.

Da yake bayani akan zaman lafiya, Shaikh Zakzaky ya ja hankali akan rashin dacewar kiran Kiristoci da sunan 'Arna', inda yace: "Sunan da Allah ya ambace su a cikin Alkur’ani shi ne 'Ma'abotan Littafi'."

Maziyartan sun karrama Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), inda s**a bashi allo wanda a jiki aka bayyana shi a matsayin mutum na farko a ƙasar nan da ke ƙoƙari wajen haɗa kan al'umma, don su rayu cikin aminci. Sannan sun ayyana shi a matsayin Malami na farko a wannan nahiyar, da ke kira zuwa ga dawo da ikon addini a wannan lokacin.

Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky
Www.cibiyarwallafa.org
Telegram: t.me/cibiyarwallafa

Sheikh Zakzaky Says Sudan Conflict Serves Foreign Interests, Urges Unity Among Warring ForcesLeader of the Islamic movem...
05/11/2025

Sheikh Zakzaky Says Sudan Conflict Serves Foreign Interests, Urges Unity Among Warring Forces

Leader of the Islamic movement, His Eminence Sheikh Ibraheem Zakzaky, has described the ongoing war in Sudan as “unfortunate” and a tragedy driven by the interests of foreign powers. He said the conflict between the Sudanese Army and the Rapid Response Forces (RSF) is not a fight for the people of Sudan but for outsiders seeking to exploit the nation’s resources.

Speaking in an interview with Iran Press, Sheikh Zakzaky lamented that the two warring factions are “sons and daughters of the same soil” yet continue to kill one another. He expressed deep sorrow that even brothers from the same parents have taken opposing sides in the conflict, destroying their own nation for the sake of others. “You see brothers killing themselves for the interests of others,” he said.

The cleric explained that every nation must have an authority that represents its collective will. According to him, the RSF was originally supposed to cooperate with the national army to defend the Sudanese people, not to engage in a proxy war. He accused external actors of fueling the violence, saying, “Definitely, the UAE is not doing the job on its own; it is doing it for the sake of the West.” He added that as long as such outside support continues, the conflict will not end, and the Sudanese people will remain the victims.

Sheikh Zakzaky also condemned recent massacres in Darfur, where innocent civilians, including women and children, were reportedly killed. He likened the atrocities to what Zionist forces are doing to Palestinians, stressing that it is even more painful because “these are Sudanese killing Sudanese.”

He urged the Sudanese people and their leaders to end the fighting and unite for the good of their country. “It is high time they realised they should stop fighting on behalf of outsiders and come together to defend their nation,” Sheikh Zakzaky said, calling for an end to foreign manipulation and a renewed commitment to national unity.

أعظم الله أجورنا وأجوركم بمصابنا بشهادة سيدة نساء العالمين سلام الله عليها
05/11/2025

أعظم الله أجورنا وأجوركم بمصابنا بشهادة سيدة نساء العالمين سلام الله عليها

Ku guji rikici da sunan addini — Shaikh Zakzaky ya faɗa wa Musulmi da Kiristoci da s**a kai masa ziyara a AbujaJagoran H...
05/11/2025

Ku guji rikici da sunan addini — Shaikh Zakzaky ya faɗa wa Musulmi da Kiristoci da s**a kai masa ziyara a Abuja

Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya karɓi baƙuncin wakilan al’ummar Unguwar Nasarawa da ke Kaduna, a wata ziyara ta musamman da ta ƙunshi manyan shugabannin addinai daga ɓangarorin Musulmi da Kiristoci.

Cikin tawagar akwai Mista Zakari, wakilin ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya (CAN) a ƙaramar hukumar Chikun, Alhaji Aliyu Mai Lafiya Chiroman Nasarawa, Mista Dominic, babban faston cocin Katolika na Unguwar Nasarawa, da Shaikh Alaramma Jabir Muhammad, babban limamin masallacin Juma’a na yankin.

A yayin ganawar wacce ta kasance a ranar Talata 13 ga Jimada Ula, 1447, daidai da 4 ga watan Nuwamban 2025 wacce Ofishin Shehin Malamin ya labarta, Jagora Shaikh Zakzaky (H) ya yi kira mai ƙarfi ga al’umma da su guji kowacce irin fitina ko rikici da za ta iya kawo rabuwar kai tsakanin Musulmi da Kiristoci.

Ya ce, “Kar ku yarda a haɗa ku rigima da juna, ko da da sunan addini ko da da sunan ƙabila. Ku zauna lafiya, ku haɗa kai domin amfanin kowa da kowa.”

Jagoran ya bayyana cewa Kiristoci ba arna ba ne, yana mai tunatar da cewa Allah Maɗaukaki ya ambace su a cikin Alƙur’ani da suna “Ma’abota Littafi”. Ya ce wannan dalili ne da ya wajabta a ci gaba da girmama juna da ƙarfafa zumunci da fahimtar juna a tsakanin mabiya addinan.

Wannan ganawa ta kasance wata dama ta ƙarfafa haɗin kai da fahimtar juna a tsakanin shugabannin addinai a Nasarawa, abin da da dama s**a yaba da shi a matsayin mataki mai muhimmanci wajen gina zaman lafiya da haɗin kai a Kaduna da ma kasar baki ɗaya.

05/11/2025
أعظم الله أجورنا وأجوركم بمصابنا بشهادة سيدة نساء العالمين سلام الله عليها       04/11/2025
04/11/2025

أعظم الله أجورنا وأجوركم بمصابنا بشهادة سيدة نساء العالمين سلام الله عليها





04/11/2025

Address

Jimeta
Yola

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Media Forum Yola posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share