Media Forum Yola

Media Forum  Yola Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Media Forum Yola, Media/News Company, Jimeta, Yola.

Welcome to Media Forum Yola
This platform shares the message of the Islamic Movement under Sheikh Ibrahim Zakzaky (H), focusing on Yola and Adamawa.

📢Follow us to stay updated on the Islamic Movement in Yola Zone and throughout the country.

DUK MUSULMI ZAI SHIGA ALJANNA; SAI WANDA YA ƘIDaga Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)“To duk wanda ya ke musulmi ne shi,...
11/10/2025

DUK MUSULMI ZAI SHIGA ALJANNA; SAI WANDA YA ƘI

Daga Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)

“To duk wanda ya ke musulmi ne shi, an bashi damar hayyakewa. Kamar yadda ya zo a hadisi cewa; Duk musulmi zai shiga Aljanna sai wanda ya ki, sai (sahabbai) su ka tambaye shi, Ya Manzon Allah wa zai ki shiga Aljanna? Sai ya ce wanda ya bi ni (inji Manzon Allah) zai shiga Aljanna, wanda kuma ya ki bina shi ne ya kiya, ya ki ya shigaAljanna kenan.

“Ka ga da wannan ibara din ina tunatar da ku wani abu da na taba tunatarwa a nan garin da dadewa, na ke cewa; kowane musulmi an bashi mabudin Aljanna a hannunsa, ya rage ya bude Aljannar ya shiga, ko kuma ya wurgar da (mabudin) ya fasa, a ce wane ina mabudin? Ya ce ai ya watsar, a ce to ai sai ka je daya gidan. Domin gidan dama gida biyu ne, in mutum bai shiga Aljanna ba, labudda daya gidan za shi, in ka shiga Aljanna ka ga ba ka ga wani ba to yana daya gidan, gidan kuma biyu ne kawai, su ne makoma ya zuwa ga Allah.

“Kamar yadda wannan hadisin ya ke cewa; Ku sanifa, makoma ga Allah imma Aljanna, wa imma Wuta. Ka ga kenan shi musulmi an bashi dama ya shiga Aljanna, ga mabudin shiga Aljanna. Mene ne mabudin? Ya bi Manzon Allah, tunda Allah Ta'ala Ya masa daraja babba, da Kafiri ne bai kai ga samun mabudin ba sai mu ce (to) ya yi Imani, in ya shaida da La'ilaha Ilallah Muhammadur Rasulullah ya samu mabudi, to yanzu ya rage aiki, in kuwa bai shaida ba, to ka ga bashi ma da rabo din.

“To duk musulmi ka ga yana da rabo din kenan, ya rage yanzu mene? Ya kyautata aiki, ya guje ma abinda aka hana, ya yi abinda umarce shi daidai gwargwado, tare da imaninsa, shi kenan. Allah kuma bai kallafa ma rai abin da ba ta iyawa ba. To kun ga kenan tamkar an bashi mabudin Aljanna ya bude ya shiga kenan, in ya ki yi, ya (jefar) da mabudin kenan.”

— Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) a yayin jawabin dare a wajen Mu'utamar Aamm a garin Azare shekarar 2008.





11/10/2025

DALILIN DA YASA MATAN SHI’A KE SAKA BAƘAKEN HIJABI (i) — Daga: Kausar Ammar ƊantinkaMace tana da daraja mai girman gaske...
07/10/2025

DALILIN DA YASA MATAN SHI’A KE SAKA BAƘAKEN HIJABI (i)

— Daga: Kausar Ammar Ɗantinka

Mace tana da daraja mai girman gaske a wurin Allah (T), wanda ta na buƙatar sa'ayi na musamman domin mallakar wannan darajar da Allah Ya bata. To, amma ta yaya take kare wannan darajar a cikin al’umma?

Ma’anar Hijabi

Kalmar Hijabi daga Larabci ce, tana nufin rufi, kariya ko katanga. A Musulunci Hijabi ba kawai mayafi bane ko tufafi, ba kuma ado ba ne— tsarin rayuwa ne da ke nufin kare mace daga abin da zai rage ƙimarta da darajarta ko cutar da ita gami da kaita zuwa ga halaka.

Hijabi ba tufafi ba ne kaɗai, garkuwa ce ta mutunci da Allah (SWT) ya yi wa mata. Duk lokacin da mace ta rufe jikinta cikin hijabi, tana ɗaukaka kanta sama da kowane kwalliya ta duniya, tana shiga jerin mata masu daraja a wurin Ubangiji.

Shari’a ta ce mace ta rufe jikinta gaba ɗaya, banda fuska da tafin hannu idan ba su zama ado ba. Launin hijabi ba a taƙaita shi ba, amma ya zama ba mai jan hankali ba. Sai dai malamai sun nuna cewa baƙin hijabi yana da falala ta musamman.

Akwai wani hadisi da malamai daga bangarorin Shi’a da Ahlus-Sunnah s**a rawaito a wajen fassarar ayar hijabi, wanda yake da ma’ana mai muhimmanci wajen fahimtar asalinsa.

A cikin Sunan Abi Dawud (hadisi mai lamba 4102), daga Ummu Salama (Allah ya yarda da ita) ta ce:

"Lokacin da aka saukar da ayar: Ya Annabi! Ka ce wa matanka da ’y’ayenka da matan muminai su saki mayafansu a kan jikinsu (Al-Ahzab: 59), sai matan Ansar s**a fito tamkar akwai tsuntsaye a kan kawunansu saboda baƙaƙen tufafi."

Haka kuma, a wajen Shi’a, an rawaito a cikin Tafsīr al-Qummi yayin da yake fassara ayar Al-Ahzab (33:59) ya ambaci cewa:

"Lokacin da wannan aya ta sauka, sai matan Muhajirun da Ansar s**a fito, s**a rufe kansu da mayafansu masu duhu."

Wannan ruwayoyi biyu daga bangarori daban-daban suna ƙara tabbatar da cewa hijabi ba kawai ado ba ne, sai dai alamar ibada da biyayya ga Allah (SWT).

Hadisi daga Imam Ja’afar as-Sadiq (a.s) ya ce:

“Mafi kyawun tufafi ga mata shine wanda zai rufe su gaba ɗaya, kuma ba zai ja hankali ba.”
(Al-Kafi, Juzu’i na 5, shafi na 521, Hadisi na 1)

Wannan hadisin yana jaddada cewa tufafin mace su kasance, masu rufe jikinta gaba ɗaya (satar), ba masu jawo hankalin maza ba (ghairu mulfitin). Ko da yake ba a ambaci launin baƙi kai tsaye ba, tufafi masu duhu suna ɗaya daga cikin hanyoyin tabbatar da wannan sharadi. Domin launuka masu haske ko masu armashi na iya jawo hankali, yayin da baƙi ke nuna ladabi da kamun kai a suturar mace.

Zan ci gaba.....✍️

Youth Forum Media Team
Sashen Marubuta
0 7 — 1 0 — 2 0 2 5

JAN HANKALI DANGANE DA HAƊIN KAN MUSULMI— Daga Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)“Saboda haka, mutum ya k**ata ya yi naz...
07/10/2025

JAN HANKALI DANGANE DA HAƊIN KAN MUSULMI

— Daga Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)

“Saboda haka, mutum ya k**ata ya yi nazarin wa yake ma aiki? Mun sha fada mukan nanata ba daya ba biyu ba, duk wanda ka ji ya na kira ga rarrabar kawukan Musulmi, ya yarda ko bai yarda ba, ya sani ko bai sani ba, yana ma makiya aiki ne—ko ya yarda ko kar ya yarda, ko ya sani ko kar ya sani yana ma makiya aiki ne. Domin aikin makiya ne, shirinsu ne na rarraba din. Yanzu al'ummar Musulmi ya zama abinda ya dame su shi ne; me ya raba su ba meya hada su ba.

“Na'am ba muce ba abinda ya raba su ba, Manzon nan (S) ya zo da sako, kuma ya isar da sako ɗin. Allah Ta'ala Ya saukar masa da Alƙur'ani kammalalle cikakke, babu abinda ya kara shi babu abinda ya rage shi. Kuma ya bayyana ma'anar Alƙur'anin, kuma bai bar duniyar nan ba sai da ya kafa al'umma akan Addini.

“To amma al'ummar ita ta bamu gadon waɗansu abubuwan. An samu sabani akan shugabanci—wannan sabani ne aka samu. Ba a samu sabani akan matsayin Allah Ta'ala a matsayin Shi ne kadai Abin bauta ba. Ba a samu sabani akan shi Manzon Allah ne, kuma bawan Allah Manzon Allah, ba wani wanda ya ke kiranshi Ubangiji ko ɗan Ubangiji, ko daya daga cikin wadanda s**a taru s**a yi Ubangiji. Har ma a tashahud (zaman tahiya) dinmu sai mun ambaci; shi bawa ne kafin mu ce shi Manzo ne. A kullum sai mun ce; “Wa Ashhadu Anna Muhammadan Abduhu wa Rasuluhu”.

“Saboda haka bamu da sabani akan matsayin Manzon Allah, ba wani wanda yake ce mishi Ubangiji ko ɗan ubangiji ko abinda ya yi k**a da haka. Bamu da sabani akan Alƙur'ani. Na'am za ku ji zancen wawayen gari suna ce muku akwai wani Alƙur'ani daban, amman dai ‘Fi'ilan' dai Alƙur'ani guda daya ne, bashi da ƙari ba ragi shi ne Wannan.

“To amma al'umma ta saba akan fassara da ruwayoyi, don haka aka samu abinda ake ce ma ‘Firƙa' an samu ‘Firƙoƙi’ an samu Mazahib— Mazhabobi, an samu ‘Ɗuraƙat’ an samu Ɗariƙoƙi, wannan a cikin addinin suke. Lokacin da muke magana kan Mazhaba ko Firƙa, ko Ɗarika, muna magana ne kan ‘Juz'i’ bangare muke magana akai. Amma in muka zo muna magana akan Musulunci muna magana ne akan abinda ya doru ne akan dukkan wadannan, shi ne a sama, Musulunci ne a sama. Su wadannan karkashin Musuluncin suke. Duk wanda ka ji yana rigima akan Firƙa to yana rigima akan bangare ne, ya bar tushe, ya bar asali, yana magana akan reshe ne.

“Duk wanda ka ji yana magana akan Mazhaba shi ma ya bar tushe ne ya koma yana rigama akan reshe ne. Duk wanda ka ji yana rigama akan Ɗarika shi ma ya bar tushe ne ya koma reshe, don wadannan rassa ne. Firƙoƙi, Mazhabobi, Ɗariƙoƙi, da ma yanzu da ake yayin ƙungiyoyi, duk waɗannan ƙungiyoyi juz'iyai ne.

“Na'am da manufofi daban-daban, ba su (manufofin) ne asasi ba, ba su ne kuma asali ba. Muna magana kan asali ne; sunanmu Musulmi, ba sunanmu wadannan rarrabe-rarraben ba. Sunan al'ummarmu Musulmi shi ne ainihin Allah Ta'ala Yake cewa: “Huwallazi Sammakumul Muslimin min Kab, Wafihazalik” Ainihin shi ne tun farko mun ambace ku addinin Babanmu Ibrahim shi ne ya ambace ku, ma'ana Allah Ta'ala shi ne Ya ambace ku Musulmi tun farko da kuma a wannan lokacin da wannan Manzon ya zo, domin ku zama shaida ga sauran al'ummu, kuma Manzo ya zama shaida akan ku.

“Yanzu kiraye-kirayen sunannaki da daukan kowwane suna a matsayin shi ne ma addinin ayi ta rigima akai. Da kuma katangar karfen da aka sa a kwakwalwa, babu katangar sam, ba ta da wujudi sam-sam! Amma sai a kirkireta a raba tsakanin al'umma, har mutum ya riƙa ganin cewa wancan tsakaninsa da shi akwai shamaki, ra'ayinsu daban ne, fahimtarsu daban ne, har ma in tayi k**ari ma sai ya ce addininsu daban ne, alhali katanga aka sa masa a kwakwalwarsa—ta fi katangar karfe karfi. Saboda ainihin ta raba shi da ɗan'uwansa Musulmi alhali addininsu guda.

“To wannan lokaci namu da ainihin bamu son ya zama sai maƙiya ne zasu ingiza mu izuwa hadin kai, don shi hadin kan nan a cikin addinin namu ne yake, umarni ne na Allah Ta'ala: “Wa Atasimu Bi Hablillahi Jami'an Wala Ta Farraƙu” ku yi riko da igiyar Allah gabadayanku kar ku rarraba, aka nuna illar rarraba tun a na farko, sannan kuma

harwalayau shi wannan Manzo ya k**anta al'ummar Musulmi da misalin jiki guda, wanda idan wani ɓangare nasa ya yi ciwo, duk sauran bangarorin za su amsa da rashin bacci da kuma zazzabi. Saboda haka idan aka taba wani bangare duk gabadaya jikin ne yake amsawa, to haka al'ummar Musulmi suke, tamkar jiki Guda ne”

— Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) yayin jawabinsa na Khatamar Makon Hadin kai na shekarar 1447/2025.







06/10/2025

Asirin Masu Tada Fitina a Kafafen Sadarwa ta Hanyar Zage-Zage:Daga Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)“Kun ga k**ar misal...
06/10/2025

Asirin Masu Tada Fitina a Kafafen Sadarwa ta Hanyar Zage-Zage:

Daga Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)

“Kun ga k**ar misali wanda su ke zage-zagen nan, (mutum) yana zagin ne, amma ba ya son a san shi yake zagin, Ko ba a lura ba? Suna sa ainihin sunan ƙarya ne, mutum za ka ga ya sa sunan ƙarya, sannan kuma sai ya yi zage-zage. Mutum ɗaya ne za a bashi Computer k**ar guda goma zuwa sha biyar, duk yana da account da suna daban-daban duk na ƙarya, sai ya yi post a wannan, nan da nan sai ya koma wannan ya yi comment sai ya zagi wannan maganar.

“Wato post ɗin da zai yi (na farko) zai yi k**ar yabo ne, kai kuma sai ka ɗauka k**ar mutumin kirki ne, sai ya ce ai Shi'a masu faɗin gaskiya ne, su kaza-kaza, shi fa ya yi abinsa, sai ya koma nan sai ya zubo ashar, sai ta koma can ya zubo ashar, sai ya sake komawa wani ma, sai ya dinga zuba ashararori.

“To kai kuma da ka ke kallo sai ka ɗauka mutane ne, nan kuwa mutum ɗaya ne ya yi kiɗansa da rawarsa, an fahimta ai. Za ka iya gane wannan; in ka ga an sa wani abu, koda da Language ɗin ƴan'uwa aka yi, indai ka ji farkon comment zagi ne to wanda ya yi zagin shi ya shigar, ya shigar ne don ya yi zagin. Sai ka ga ma tsakanin post da comment ba nisa, tabbatar su abin nasu ma basu da wayo.

“To irin wannan sun yi a Iran, s**a yi ta sa sunayen Iraniyawa sai ya zama ashe daga America ne suke yi, s**a dinga zuba sunayen k**ar wai suna fadin suna s**ar Jamhuriyar Musulunci, da sunan cewa wai su ƴan Iran ne, nan kuwa ma'aikata ne s**a dauke su aiki. Fi'ilan a aikace ba za ka gani ba.

“Kun san lokacin da aka yi sahawa ɗin Arabiyya, lokacin da Misra ta yamutse ɗin nan bayan Tunisia sai Misra ta karba. To shi kenan sai Amurkawa s**a shigo da nasu s**a je s**a shiga Libiya s**a rugurguza Libiya, s**a ce Iran ma gashi can ana yi. S**a dinga irin wannan rubuce-rubucen kai kace da gaske ne, s**a yi ta rubuce-rubuce.

“To shi kenan sai ƴan Iran s**a fito s**a ya Muzaharar nuna goyon baya ga nizamin Musulunci, sai aka ga iyakacin gani miliyoyi kuma, to sai s**a yi shiru da bakinsu. S**a ga abin ya fi karfinsu, ina waɗannan mutanen masu comment a Computer na Internet? Ka ga ba su, tabbatar basu da wujudi.

“To shi kenan, nan ina baku labari ne. A nan suna yi mana wannan, koda kana ganin zage-zage sune, sun dauka za su iya impressing ɗin mutane ne, ka ga a nan ɗin zage-zagen duk da Hausa suke yi, kuma za ka ga da ganin rubutun ma basu iya Hausan ba, ka ga an jona wannan kalma da waccar, ƙarshen wannan an dau wannan an maka a can, bai iya ma Hausan ba, tabbatar bai ma yi makaranta ba, zage-zage amma da Hausa. Amma ba su yi da Ingilishi, an fahimta ai.

“In mutum ya je Twitter, zai ga cewa idan wani ya yi zagi, in aka dirar masa sai ya ga comments wajen daruruwa, sai ya yi shiru, sai su yi shiru a nan, don suna ganin shi wannan international ne, amma na Hausa kam ana nan, amma abin zagin zai kawo karshe tunda yake yanzu asirinsu ya fara tonuwa, an fahimta ai”.

— Ɓangaren jawabin Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) a yayin ganawa da 'Yan Ibn Fodio Forum, a ranar 15/1/2022 a gidansa da ke Abuja.






06/Octoberr/2025

A DAREN JIYA ASABAR AKA GABATAR DA GAGARUMIN TARON MAULIDIN MANZON ALLAH SAWW A GARIN NUMAN WANDA ALMAJIRAN SHEIKH IBRAH...
05/10/2025

A DAREN JIYA ASABAR AKA GABATAR DA GAGARUMIN TARON MAULIDIN MANZON ALLAH SAWW A GARIN NUMAN WANDA ALMAJIRAN SHEIKH IBRAHIM ZAKZAKY)H) S**A SHIRYA.

Jagora (H) ya bayyana manufar Media Forum a matsayin samar da tsari mai kyau na isar da sako a cikin 'yan uwa na Harka I...
05/10/2025

Jagora (H) ya bayyana manufar Media Forum a matsayin samar da tsari mai kyau na isar da sako a cikin 'yan uwa na Harka Islamiyya, kuma saƙo ya isa zuwa ga al'umma. Inda ya lissafa wasu ayyuka daban-daban da ya dace Media Forum din su tsayu da shi.

A karshe, Jagora (H) ya ja hankali akan yin aiki saboda Allah. Ya ce, aiki tare ya gaji matsaloli, da kushe, da guna-guni. Yace: "Amma in kana yi saboda mutane ne sai ka fasa in ka ji s**a, in kuwa don Allah ka ke yi, sai ka cigaba da abinka.”

Bayan jawabin Jagora (H), an assasa kwamiti mai dauke da mutane takwas, a matsayin masu kula da lamarin Media Forum a matakin baiɗaya (Centrallly), inda s**a ayyana Ammar Muhammad Rajab a matsayin shugaban Kwamitin na Media Forum. An baiwa kwamitin dama, su tsara ayyuka, da ayyana masu gudanar da Lajanar ta Media Forum a bangarori daban-daban na sassan Harka gabaɗaya.

-Baqeer consider

03/10/2025

Albarkacin wannan Rana ta Juma'a Mu Karanta Fatiha da Salatin Annabi (S) ladan Allah ya kai ga ruhin Shahidan Moqawamah Ya taimaki Al'ummar Palasdinu akan Maƙiya Ƴan Mamaya.

اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَ آلِ مُحَمَّدٍ







03/10/2025

ILLOLIN KWAƊAYI GA MUTUNCIN ƳA MACE—Daga: Fatima Adamu TinjaKwaɗayin abin hannun namiji ba kawai ya rage darajar mace ba...
03/10/2025

ILLOLIN KWAƊAYI GA MUTUNCIN ƳA MACE

—Daga: Fatima Adamu Tinja

Kwaɗayin abin hannun namiji ba kawai ya rage darajar mace ba ne, har ma yana iya rushe rayuwarta gaba ɗaya, idan mace ta maida hankalinta kan abin duniyar da namiji zai ba ta, maimakon neman abin da zai amfane ta a addini da duniya, tabbas ta shiga cikin wata mummunar hanya.

Ga wasu daga cikin illolin da hakan ke haifarwa:

* Yana rage darajar ki a idon mutane.

* Yana jefa ki cikin zunubi da saɓawa Allah.

* Yana haifar da damuwa da ƙasƙanci.

* Yana jawo kazanta ga sunan iyayenki da danginki.

Namijin arziki ba ya neman mace mai kwaɗayi, yana neman mace mai k**ala, mai hakuri, mai tarbiyya, wadda za ta iya zame masa mata ta gari kuma uwa ta gari ga ƴaƴansa, kwaɗayi yana nisantar da irin waɗannan mazajen daga gare ki.

NASIHA GARE MU MATA:

Mu tuna cewa darajarmu ba a cikin abin duniya ba ce, kuma ba'a cikin abin da namiji zai ba mu ba ne, darajarmu tana cikin Imaninmu, kunya, nutsuwa, tarbiyya, da kuma ƙoƙarinmu na neman ilimi da sana'a.

Mu dogara ga Allah dan shi ne mai bayarwa, mu nemi Ilimi da Sana'a, mu zaɓi abokai na gari, domin abokiyar banza takan jawo ki zuwa ga halaye marasa kyau, ki zaɓi abokan kirki waɗanda za su tunatar da ke game da kyawawan halaye da kuma muhimmancin kiyaye addini.

MAFITA GA WANNAN MATSALA KIRA NA GA IYAYE:

Haƙƙi ne a kan ku da ku baiwa ƴaƴanku tarbiyya mai kyau, ku koya musu muhimmancin wadar zuci, da dogaro da kai, da kuma kiyaye addini. Ku zama misali a gare su.

KIRA GA SAMARI:

Ku ji tsoron Allah ku gu ji jan hankalin mata da kuɗinku ko dukiyarku, ku nemi mata masu tarbiyya da hankali, waɗanda za su so ku don halayenku, ba don abin hannunku ba.

Kwaɗayi wata cuta ce da ke kashe mutunci da lalata rayuwa, dan haka mu tashi tsaye, mu sanya mutuncinmu a gaba, mu kuma yi amfani da basirarmu da ƙarfin zuciyarmu wajen gina rayuwa mai ma'ana, wadda za mu zama abin alfahari ga iyayenmu, da addininmu, da kuma al'ummarmu baki ɗaya.

Youth Forum Media Team
Sashen Marubuta
0 3 — 1 0 — 2 0 2 5

29/09/2025
🌹 KARRAMAWA TA MUSAMMAN GA MASU YAƊA ƘAUNAR ANNABI (SAWW) A ADAMAWA 🌹A yayin babban taron Khatamar Makon Haɗin Kan Musul...
28/09/2025

🌹 KARRAMAWA TA MUSAMMAN GA MASU YAƊA ƘAUNAR ANNABI (SAWW) A ADAMAWA 🌹

A yayin babban taron Khatamar Makon Haɗin Kan Musulmi da aka gudanar a Da’irar Yola, ranar Asabar 27/09/2025, yan’uwa musulmi almajiran Sheikh Ibrahim Zakzaky (H) sun karrama wasu malamai da kyautar kambun yabo (Award).

Wannan karramawa ta kasance ne ga malamai da s**a kasance gwaraza (Heros) wajen yaɗa ƙaunar Annabi Muhammad (SAWW) da iyalan gidansa tsarkaka a fadin garin Adamawa.

Taron ya kasance na musamman, domin ya nuna muhimmancin girmama masu hidima wajen ƙarfafa soyayya da haɗin kan musulmi.

🕌 ALLAH ya ƙara mana son Manzon Allah (SAWW) da iyalan gidansa tsarkaka.

🗓 28/09/2025
✍ Media Forum Yola

Maulidin Manzon Allah (S.A.W) daga Halkar NEPA, da’irar YolaAn gudanar da taron Maulidin Manzon Allah (S.A.W) jiya Asaba...
28/09/2025

Maulidin Manzon Allah (S.A.W) daga Halkar NEPA, da’irar Yola

An gudanar da taron Maulidin Manzon Allah (S.A.W) jiya Asabar da dare a Masallacin Ganye Street da ke unguwar NEPA.

Dubban al’umma masoya Manzon Allah (S.A.W) daga sassa daban-daban sun samu damar halarta. Haka zalika, manyan malamai da mawaƙa masu yabon Ma’aiki (S.A.W) (sha’iran) sun halarci wannan babban taro domin fadakar da al’umma kan darajojin Manzon Allah (S.A.W).

📅 28-09-2025
©️ Adamawa Press Team Service

TARE DA WAKILN SARKIN SHARIFAI NA JIHAR ADAMAWA A WAJEN TARON KHATAMAR MAKON HAƊIN KAN MUSULMI A DA'IRAR YOLA Sidi Muham...
27/09/2025

TARE DA WAKILN SARKIN SHARIFAI NA JIHAR ADAMAWA A WAJEN TARON KHATAMAR MAKON HAƊIN KAN MUSULMI A DA'IRAR YOLA

Sidi Muhammad Bashir kenan yayin da yake gabatar da jawabi a wajen taron makon haɗin kai a garin Yola, wanda yan'uwa musulmai almajiran Sheikh Ibrahim Zakzaky (H) Na Da'irar Yola s**a shirya.

Sidi Muhammad Bashir wakilin Sarkin sharifai na jihar Adamawa yayi bayani mai muhimmanci kan haɗin kai dakuma soyayyar Annabi (saww).

Daga ɗakin taro na Jorkems dake garin jimeta

27/09/2025
Media Forum Yola 📸

Address

Jimeta
Yola

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Media Forum Yola posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share