Demokradiya A Yau Radio Gotel Yola

Demokradiya A Yau Radio Gotel Yola This page was design to promote, The Program DEMOKRADIYA A YAU Radio Gotel Yola.

07/08/2025

Abubuwan da ke faruwa a PDP Wannan ita ta tabbatarwa da mutane cewa Jam'iyyar PDP ba kowa PDP ta zama kango, Domin gatan ta ya fita- Inji Sharfaddeen Kanti Kawari daga jihar Kano.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayar da kyautar fuloti da kuɗi naira miliyan biyar ga kowane ɗaya daga cikin iyalan tawagar ...
06/08/2025

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayar da kyautar fuloti da kuɗi naira miliyan biyar ga kowane ɗaya daga cikin iyalan tawagar ’yan wasan nan na Kano 22 da s**a rasu a wani mummunan haɗarin mota da ya auku a watan Yuni.

Mai bai wa gwamnan shawara kan yaɗa labarai, Ibrahim Adam, ne ya tabbatar da wannan kyauta cikin wani saƙo da ya wallafa a Facebook a wannan Larabar.

“Mai girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bai wa iyalan ’yan wasan da s**a rasu fuloti ɗaya da kuma naira miliyan biyar kowannensu,” in ji sanarwar.

Aminiya ta ruwaito cewa, tawagar ’yan wasan da s**a rasu ta yi hatsari ne a yayin da suke dawowa daga gasar wasannin ƙasa ta National Sports Festival da aka gudanar a Jihar Ogun.

Tawagar da lamarin ya rutsa da ita ta ƙunshi ’yan wasa, masu horarwa, mataimakansu, jami’an lafiya, direbobi, injiniyoyi da kuma ɗan jarida.

Ajali ya katse musu hanzari ne bayan samun nasarori daban-daban a gasar ta National Sports Festival da s**a haɗa da sarƙoƙin zinare 6, azurfa 13 da na tagulla 10 da s**a lashe.

Ana iya tuna cewa, mummunan lamarin ya auku ne a garin Dakatsalle da ke ƙaramar hukumar Bebeji, kimanin kilomita 50 daga Kano, a yayin da ya rage ƙiris tawagar ta ƙarasa gida.

Tun a wancan lokaci, jama’a daga ciki da wajen Jihar Kano s**a riƙa jimami da bayyana alhini, musamman duba da irin gudummawar da ’yan wasan s**a bayar kafin rasuwarsu.

05/08/2025

A wani mataki na ragewa jama'ar da ambaliyar ruwa ya shafa radadi, gidauniyar Baba 10 foundation ta gwangwaje wasu da kuɗi domin kyautatawa.....

05/08/2025

Bisa ga dukkan alamu dai kalaman da gwamna Ahmadu Umaru Fintiri yayi a lokacin kaddamar da yakin neman zaben dan majalisar dokoki a karamar hukumar Ganye ya bar baya da kura, ko meh yayi zafi haka? Ku saurari martani daga bakin Husaini Ahmadu Har...

04/08/2025

Shugabar mata na jam'iyyar ADC a jihar Adamawa Hon. Aisha Umar Sidi tana kalubalantar wanda ake ikirarin shine shugaban jam'iyyar ADC na jihar daya fito ya rantse bai ajiye mukamin sa ba a baya...

Hakan na faruwa ne sanadiyar yadda ake son ayi mata karfa- karfa da mukamin ta shugabar mata na jam'iyyar.

04/08/2025

A yanzu jam'iyyar ADC itace cikkakiyar jam'iyyar adawa da zata tinkari gwamnatin mai ci a kasar a cewar mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai ga Tsohon mataimakin shugaban kasa Najeriya Alh Atiku Abubakar -Hon Sharfadeen Kanti kwari...

03/08/2025

Ina kira ga matasa maza da mata su zauna su nasu kuma su tantance wanda zai wakilce su a mataki daban daban na kasar nan Inji Arc. Aji Paul Wampana Matashin Dan Siyasa a jihar Adamawa.

02/08/2025

Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasan Najeriya kan bukatu na musamman, Hon Muhammad Abba Isah yace an samu gagarumar gudumawa a wannan Gwamnatin daidai gwargwado wajen baiwa masu bukata na musamman hadin kai.

Kuma Hon Muhammad Abba isah yayi kira ga masu bukata na musamman na sauran jahohi da su hada kansu domin zama a inuwa daya su samarwa kansu cigaba...

01/08/2025

Ina kira ga talakawan kasar da su rungumi sabuwar tafiya, Kuma Munyi nadaman yiwa Tinubu aiki a 2023 kuma sai mun kawar da gomnatinsa a 2027, A cewar Hon Abdul'aziz Abubakar ( Dan Galadiman Daware).

31/07/2025

Rashin tantance kwararrun ƴan takara shi ke sa al'umma basu samun romon demokradiyya - Hamisu Idris Medugu (Sardaunan Duhu).

30/07/2025

Alh Abdurahman Buba Kwacham Sarkin Fulanin Mubi Emirate, Yace Aikin da shugabanin mu keyi idan bakayi bincike ba, Kake zagin su sai Allah ya tambayeka.

Tsohon Shugaban Karamar Hukumar Guyuk da ke Jihar Adamawa, Hon. Kube Donglock, ya bayyana a hukumance ficewarsa daga jam...
30/07/2025

Tsohon Shugaban Karamar Hukumar Guyuk da ke Jihar Adamawa, Hon. Kube Donglock, ya bayyana a hukumance ficewarsa daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP).

Hon. Kube, wanda fitaccen ɗan siyasa ne a matakin ƙasa da kuma ɗaya daga cikin dogarawan tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, ya yanke wannan shawarar ne bayan ficewar Atiku daga jam’iyyar PDP kwanan nan, abin da da dama ke kallon sa a matsayin babbar juyin-juya hali a siyasar jihar Adamawa.

A tafiyarsa ta siyasa, Hon. Kube Donglock ya rike muƙamai da dama da s**a haɗa da: Kwamishinan Ƙaramar Hukuma (Supervisory Councillor), Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukuma, Shugaban Ƙaramar Hukuma na Guyuk, da kuma na baya-bayan nan – Mataimaki na Musamman (Senior Special Assistant). Kwarewarsa da jajircewarsa wajen kula da al’umma ya tabbatar da irin tasirin da yake da shi da kuma yadda ke kasancewa kusa da jama’arsa.

Abin lura shi ne, Hon. Kube bai fice daga PDP shi kaɗai ba — ya fita tare da kusan mabiya 5,000 daga jam’iyyu daban-daban ciki da wajen Karamar Hukumar Guyuk. Wannan gagarumin ficewa ya nuna irin ƙarfinsa a siyasa, tare da yiwuwar sauyin salo da tsarin siyasa a yankin.

Ficewarsa daga jam’iyyar PDP na ɗaukar matsayin babban gibi ga jam’iyyar a yankin kudu na jihar Adamawa, musamman ganin yadda yake da ƙarfin jawo jama’a da tasiri a harkokin siyasa.

Address

Yola
652105

Telephone

+2348021453694

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Demokradiya A Yau Radio Gotel Yola posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share