Demokradiya A Yau Radio Gotel Yola

Demokradiya A Yau Radio Gotel Yola This page was design to promote, The Program DEMOKRADIYA A YAU Radio Gotel Yola.

Gwamnan Jihar Kebbi, Dr. Nasir Idris, Kauran Gwandu, ya gargadi ’yan siyasa da sauran al’umma da su guji siyasantar da b...
08/10/2025

Gwamnan Jihar Kebbi, Dr. Nasir Idris, Kauran Gwandu, ya gargadi ’yan siyasa da sauran al’umma da su guji siyasantar da batun tsaro, yana mai cewa yaki da rashin tsaro abu ne na haɗin kai da ya shafi kowa ba wai jam’iyya ba.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a wajen taron shekara-shekara na Zauren Tuntuba na Dattijan Jihar Kebbi wanda na bana a ka yi kan Tattalin Arzikin Jihar a ranar Laraba, 8 ga Oktoba, 2025.

Ya bayyana cewa gwamnati tana ƙoƙari wajen magance matsalar tsaro musamman a yankin Kebbi ta Kudu, inda ta samar da kayan aiki, motocin sintiri da tallafin kuɗi ga jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya.

Gwamnan ya kuma yaba wa ƙungiyar dattawan jihar bisa shirya taron tattalin arziki da ke haɗa gwamnati da al’umma wajen inganta ci gaba.

Ya ce gwamnatin sa za ta ci gaba da mayar da hankali kan bangarorin noma, ilimi, lafiya, habakar matasa da ƙananan masana’antu, tare da jaddada cewa ci gaban jihar Kebbi abin haɗin kai ne da ke buƙatar gudunmawar kowa da kowa.

Tsohon Mataimakin Shugaban kasa Nijeriya  Atiku Abubakar ya bukaci a binciki takardun shaidar  karatun ministocin gwamna...
08/10/2025

Tsohon Mataimakin Shugaban kasa Nijeriya Atiku Abubakar ya bukaci a binciki takardun shaidar karatun ministocin gwamnatin shugaba Tinubu...

08/10/2025

ALH Shareef Alhassan Babban mai baiwa Gwamnan jihar Adamawa shawara akan kafafen yada Labarai, Yayi jawabi ne kan yadda bukin karrama Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri a Babban birnin tarayya Abuja da abokin aiki Mika'ila Danjuma Mubi..

06/10/2025

Rikicin Argungu ya rage tsakanin ƴan ADC da mutanen su domin kuwa a yanzu sauke nauyin al'umman Kebbi ne damuwan Gomnati Jahar Kebbi.

Kuma duk wani mai kishin Jahar Kebbi to zaka same shi mai Alfahari da Gomnatin Dr Nasir Idris Kauran Gwandu a cewar Alh Abuzaidu Abubakar Yari Mataimakin Gwamnan Jahar Kebbi kan kafofin yada labarai da na sada zumunta.

SAKON TAYA MURNA DAGA SAKATARE DIN DIN DIN NA HUKUMAR JIN DAƊIN ALHAZAN JIHAR ADAMAWA MALAM ABUBAKAR Salihu Abubakar Sad...
06/10/2025

SAKON TAYA MURNA DAGA SAKATARE DIN DIN DIN NA HUKUMAR JIN DAƊIN ALHAZAN JIHAR ADAMAWA MALAM ABUBAKAR Salihu Abubakar Sadiq , GA GWAMNA FINTIRI KAN LAMBAN YABO DA ƘUNGIYAR MALAMAI TA NUT TA BA SHI A MATSAYIN GWAMNA MAI AYYUKA MAFI KYAU A BANGAREN ILIMI.

Sakataren Dindindin na Hukumar Jin Daɗin Alhazan Jihar Adamawa, Malam Abubakar Salihu, ya taya Gwamnan Jihar Adamawa, Dokta Ahmadu Umaru Fintiri CON, murna bisa karramawar da Ƙungiyar Malamai ta Najeriya (NUT) ta ba shi, a matsayin Gwamna mafi nasara a bangaren ilimi da kuma kulawa da malamai.

A wata sanarwa da Malam Abubakar Salihu ya sanya hannu a kai ta bayyana wannan lambar yabo a matsayin girmamawa ta gaskiya ga jajircewar Gwamna Fintiri wajen sauya fasalin bangaren ilimi da kuma bai wa matasa damar samun ingantaccen ci gaba.

Ya jaddada cewa, jajircewar Gwamnan wajen tabbatar da ci gaban kowa da kowa ta haifar da gagarumin ci gaba da samar da Ribobin DEMOKRADIYA a dukkan sassan mulki, inda wannan karramawa ta kara tabbatar da ingancin shugabancinsa da manufofin sa masu kula da bukatun jama’a.

Malam Abubakar Salihu ya yi addu’ar Allah ya kara wa Gwamnan hikima da ƙarfi wajen ci gaba da inganta harkar ilimi da dorewar cigaba a Jihar Adamawa.

WANNAN SAKO NE DAGA SHASHIN; LABARU DA AL'AMURAN YAU DA KULLUM NA HUKUMAR JIN DAƊIN ALHAZAN JIHAR ADAMAWA
OKTOBA 6, 2025.

A yau ne kungiyar malamai ta Najeriya NUT ta karrama Ahmadu Umaru Fintiri da lambar yabo ta NUT Golden Award saboda irin...
05/10/2025

A yau ne kungiyar malamai ta Najeriya NUT ta karrama Ahmadu Umaru Fintiri da lambar yabo ta NUT Golden Award saboda irin gudunmawar da ya bayar a fannin ilimi da walwalar malamai.

An bayar da kyautar ne a yayin bikin ranar malamai ta duniya na shekarar 2025 da aka gudanar a dandalin Eagle Square dake Abuja.

Da yake ba da lambar yabo, shugaban kungiyar NUT na kasa, Kwamared Audu Titus Amba, ya bayyana Gwamna Fintiri a matsayin “Gwamnan da ya fi kowa tausayin malamai a Najeriya.”

Ya yaba da irin sauye-sauyen da Gwamnan ya yi a fannin ilimi, musamman a bangaren daukar malamai, samar da ababen more rayuwa, da inganta walwala.

A cewar Amba, Gwamna Fintiri ya dauki malamai sama da 10,000 aiki, ya gina ajujuwa sama da 6,000, sannan ya kafa kwalejin kimiyya da fasaha ta Mega a shiyyar sanatoci uku na jihar Adamawa.

Ya kuma bayyana yadda Fintiri ya aiwatar da tsarin karatun firamare da sakandare kyauta, biyan kudin WAEC da NECO, tsawaita wa’adin ritayar malamai da shekaru biyar, da fara aiwatar da mafi karancin albashi ga malaman firamare da sakandare—wanda shi ne irinsa na farko a Arewacin Najeriya.

Sauran gwamnonin da s**a samu karramawa a wajen taron sun hada da Dr. Nasir Idris na jihar Kebbi, Dakta Dikko Radda na jihar Katsina, da gwamnonin jihohin Ebonyi, Kogi, da Delta.

Tawagar jihar Adamawa da s**aje wajen taron a Abuja sun hada da kakakin majalisar dokokin jihar Rt. Hon. Bathiya Wesley, tare da Sanata Iya Abbas, shugaban ma'aikata, Dr. Emos Edgar, shugaban ma'aikata, Pharmacist Ardo Isa Shehu (mni), da kwamishinan ilimi, Hon. Garba Pella.

Sauran sun hada da Dr. Aliyu Idi Hong, Farfesa Maxwell Gidado (SAN), Cif Kennedy Dauda (mni), Dr. Sulaiman Bashir, Zakariah Nyanpa, mambobin kungiyar kwadago karkashin jagorancin Comrade Emmanuel Fashe (Shugaban NLC), da shugabannin kungiyar NUT ta jihar Adamawa.

05/10/2025

Yana faruwa Yanzu!

NUT AWARD

Ku kalli yadda Gwamna Fintiri ya isa dandalin Eagle Square da ke Abuja, a daidai lokacin da kungiyar malamai ta Najeriya ke shirin karrama shi bisa jajircewarsa kan harkokin ilimi da walwalar malamai.

Zaku iya gani kai tsaye Daga Fresh air Tv..

I've just reached 25K followers! Thank you for continuing support. I could never have made it without each and every one...
04/10/2025

I've just reached 25K followers! Thank you for continuing support. I could never have made it without each and every one of you. 🙏🤗🎉

04/10/2025

Guda daga cikin yan siyasa a jihar Adamawa Alh. Sani Abdurahman ya bada yan shawarwari ga Kwamandojin baka da kuma taya murna ga Alh. Husseini Gambo bello Nakura daya shaki iskar yanci...

A wani gagarumin rikicin siyasa a jihar Adamawa, Cif Joel Madaki, babban mai bawa gwamna Ahmadu Umaru Fintiri shawara na...
04/10/2025

A wani gagarumin rikicin siyasa a jihar Adamawa, Cif Joel Madaki, babban mai bawa gwamna Ahmadu Umaru Fintiri shawara na musamman ya sauya sheka daga jam’iyyar PDP mai mulki zuwa jam’iyyar adawa ta All Progressives Congress (APC).

Madaki, tsohon shugaban jam’iyyar PDP a jihar Adamawa, kuma daya taba zama dan takarar gwamna, ana kallonsa a matsayin mai wayar da kan jama’a, wanda ake mutunta shi a matsayin shugaban al’umma, kuma jigo a siyasance. Masu fashin baki na kallon ficewar tasa a matsayin babbar illa ga jam’iyya mai mulki a jihar.

Masu lura da al’amuran jam’iyyar sun yi zargin cewa ficewar Madaki ya biyo bayan rashin jituwar da aka dade ana yi da Gwamna Fintiri, kan abin da sansaninsa keyi a matsayin “rashin kulawa da rashin goyon bayan da ya dace da matsayinsa na jigon siyasa.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Sakataren Tsare-tsare na Jam’iyyar APC na Jihar, Mustapha Atiku Ribadu, ya yi maraba da gogaggen dan siyasar cikin jam’iyyar, inda ya bayyana matakin nasa a matsayin “mai canza wasa” gabanin zaben 2027.

Ribadu ya ce: "Zuwar shugaban da ake mutuntawa wani mataki ne kawai na ganin jam'iyyarmu za ta iya jawo hankalin mutane masu kima.

Ya yi hasashen ficewar Madaki ta kara zafafa rigingimun siyasa a jihar, inda masu lura da al’amura ke cewa hakan na iya haifar da sauye-sauye a fagen siyasar Adamawa yayin da zabe mai zuwa ke kara kusantowa.

03/10/2025

Jawabin yadda Hon Husaini Gambo Bello Nakura ya tsinci kansa a gidan gyaran hali na yan kwanaki..

MURNAN KARIN SHEKARA GA KAMARA MAN NA TSOHON MATAIMAKIN SHUGABAN KASA ATIKU ABUBAKAR Auwal Saleh !!!Murnan Karin shekara...
03/10/2025

MURNAN KARIN SHEKARA GA KAMARA MAN NA TSOHON MATAIMAKIN SHUGABAN KASA ATIKU ABUBAKAR Auwal Saleh !!!

Murnan Karin shekara Auwal Saleh Kamara man na Wazirin Adamawa Alh Atiku Abubakar tsohon Mataimakin Shugaban kasa Najeriya, Auwal Saleh fatan rayuwar farin ciki Mai tsayi tareda tarin Albarka, Allah ya karawa rayuwa daraja, kima, daukaka da albarka, Ameen

Muna tayaka murna🎂🍮...

Address

Yola
652105

Telephone

+2348021453694

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Demokradiya A Yau Radio Gotel Yola posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share