04/05/2026
Mai Martaba Sarkin Katsina, Alhaji (Dr) Abdulmumin Kabir Usman CFR Ya Taya Tasi’u Sanusi Saulawa Murnar Samun Sabon Matsayin Mukaddashin Provost Marshal na Hukumar Kwastam ta Najeriya
Mai Martaba Sarkin Katsina, Alhaji (Dr) Abdulmumin Kabir Usman CFR ya aike da saƙon taya murna ga Tasi’u Sanusi Saulawa bisa naɗinsa a matsayin Mukaddashin Provost Marshal na Hukumar Kwastam ta Najeriya.
A cikin wasiƙar mai ɗauke da kwanan wata 3 ga Mayu, 2026, Sarkin ya bayyana cewa naɗin Saulawa ya zo ne bisa cancanta da ƙwarewa, tare da nuna jin daɗinsa da alfahari ga wannan matsayi da ɗan asalin Jihar Katsina ya samu.
Mai Martaba ya ƙara da cewa wannan naɗi babban nauyi ne da ke buƙatar jajircewa, riƙon amana da kuma aiki tukuru domin tabbatar da an cika amanar da aka ɗora masa.
Sarkin Katsina ya yi addu’ar Allah Ya ba Saulawa lafiya, hikima da nasara wajen gudanar da wannan sabon aiki, tare da fatan zai ci gaba da kawo ci gaba ga ƙasa da al’umma baki ɗaya.
Haka kuma, ya bayyana cewa wannan nasara abin alfahari ne ga masarautar Katsina da ma Jihar baki ɗaya, yana mai fatan za ta ƙara inganta suna da martabar jihar a matakin ƙasa.
A ƙarshe, Mai Martaba ya yi fatan Allah Ya ƙara masa ɗaukaka tare da ba shi ikon sauke nauyin da aka ɗora masa yadda ya kamata.