Taskiya Reporters

Taskiya Reporters ingantattun labarai domin tunatarwa, fadakarwa da ilmantarwa

HUDUBAR ANNABI MUHAMMAD ❤️ ﷺ WANDA YAYI  RANAR TARA GA WATAN ZUL-HIJJAH, SHEKARA TA GOMA DA HIJIRA A DUTSEN ARAFAT (RANA...
26/05/2026

HUDUBAR ANNABI MUHAMMAD ❤️ ﷺ WANDA YAYI RANAR TARA GA WATAN ZUL-HIJJAH, SHEKARA TA GOMA DA HIJIRA A DUTSEN ARAFAT (RANAR ARFA KENAN).
ANNABI (SAW)YA FARA DACEWA:
“Ya ku mutane ku bani hankalinku, domin mai Yiwuwa bazan sake kasancewa da ku bayan wannan shekaran ba, saboda haka ku saurari abinda nake gaya maku da kyau, kuma (ku isar da abinda zan gaya maku) ga wadanda basa wannan wuri a yau.
Ya ku mutane k**ar yadda kuka riki wannan wata, (na hajji) da wannan rana (ta arfa) da kuma wannan gari (na Makka) da girma kuma abin tsarewa, to, haka kuma ku riki Ran Musulmi da kuma Dukiyoyinsu da girma abin kuma karewa, ku maida wa Mutane kayan da s**a baku Amana. Kar ku cuci kowa, saboda kar wasu su cuce ku, ku tuna fa, hakika ALLAH zai yi sakayya akan ayukakanku, ALLAH (SWT) ya hana cin riba,(wato kudin ruwa) saboda haka, duk abin da aka kulla ta kudin ruwa sai an warware shi.
Ku yi hattara da shaidan, domin kiyaye Addininku. Yanzu kan ya fidda ran batar da ku akan manyan abubuwa (na sabo) saboda haka ku guji binshi akan kanana.
Ya ku jama'a hakika kuna da hakki bisa matayenku, amma suma suna da hakki bisa kanku, to hakkin su ne akanku da kuciyar dasu, Kuma ku tufatar dasu akan jin kai. ku bi dasu kyakkyawan biyarwa, ku kuma tausasa musu domin su majibintan al amurran kune, kuma mataimakan ku, Hakki ne akansu da kar su yi abota da duk wanda ba ku so, kuma su nisanci zina.
Ya ku jama'a kuyi kyakkyawan bauta ga ALLAH (SWT) ku tsaida salloli biyar(5) na farilla, Ku Azumci Watan Ramadan ku Kuma bada zakka. Ku aikata aikin hajji in har kun sami daman yi. KU SANI FA, ko wane musulmi dan uwan musulmi ne. Dukkan ku dai dai kuke. Ba wanda yake da fifiko saman wani sai ta tsoron ALLAH, da aikata kyawawan ayyukka.
Ku tuna fa (ya ku jama'a) wata rana za ku tsaya gaban ubangijinku, domin sak**akon ayyukanku, saboda haka ku yi hattara kada ku yi sake da hanya madaidaiciya bayan na kau.
Ya ku jama'a ba wani Annabi ko Manzo da zai zo bayana babu wani addini da zai zo (baya

Kotu Ta Ƙaryata Video'n Sheikh Sani Khalifa Da Aka Kawo Mata Alhamdu Lil-Lah.. Gobe Za'a Cigaba Da Shari'ar/13/05/2026Al...
15/05/2026

Kotu Ta Ƙaryata Video'n Sheikh Sani Khalifa Da Aka Kawo Mata Alhamdu Lil-Lah.. Gobe Za'a Cigaba Da Shari'ar/13/05/2026

Allah Ya Tabbatar Da Gaskiya 🤲

~Al-Ameen Sheikh Sani Khalifa ✍️
________________________________

Mun Dogara Da Allah, Ya Isar Mana
Mun Yarda Da Ƙaddara, Ya Yi Mana Sakayya

Alhamdu Lil-Lah
Alhamdu Lil-Lah
Alhamdu Lil-Lah

TARIHIN SHEIKH SANI KHALIFA ZARIA (Biography)Sheikh Khalifa Sani Abdulkadir Zaria (wanda ake kira Mallam Sani Zaria ko S...
14/05/2026

TARIHIN SHEIKH SANI KHALIFA ZARIA (Biography)
Sheikh Khalifa Sani Abdulkadir Zaria (wanda ake kira Mallam Sani Zaria ko Sheikh Sani Khalifa Zaria) ɗaya ne daga cikin manyan malamai na Musulunci a Najeriya, musamman a cikin darikar Tijjaniyya da kuma ƙungiyar Fityanul Islam a Zaria, Jihar Kaduna. Shi ne halaliffa (Khalifa) na mahaifinsa Sheikh Abdulqadir Zaria.

ASALINSA DA IYALANSA

An haife shi a ranar 27 ga Satumba, 1960 a Muchia Sabon Gari, Zaria, Kaduna State.
Shi ɗa ne na Sheikh Abdulqadir Zaria (wanda aka haife shi a 1909 a Agaie, ya rasu a kusan 1980). Mahaifinsa malami ne mai zurfin ilimi a fannoni da yawa k**ar Fiqhu, Nahwu, Balaga, Sarfu, Tawheed, da sauransu, kuma marubuci ne na wakoki na Sufanci.

BAYAN RASUWAR ƊAN’UWANSA SHEIKH TIJJANI ABDULKADIR ZARIA,

shi ya zama Khalifa Bayan Rasuwar Dan Uwansa.

ILIMI DA AYYUKANSA

Sheikh Sani Khalifa ya shahara da koyar da ilimin addini da zurfafa ruhaniya. Yana koyar da littattafai masu muhimmanci k**ar:
Akhdari
Burda
Hamziyyah
Tafsirin Alƙur’ani
Ibnu Ashir,
Ishmawi,
da sauransu
Mabiyansa suna yaba masa da tawali’u (ƙasƙantar da kai), rashin son duniya, kiran zuciya, zaman lafiya, da kuma nisantar siyasa ko rigima. Tasirinsa ya faɗaɗa a duk faɗin Najeriya, inda ɗalibai da mabiya da yawa ke kallonsa a matsayin jagora na ruhaniya.
Yana da shafukan koyarwa na bidiyo k**ar Fityanu Media, inda ake samun lectures, wa’azi, da karatu na litattafai.

HALIN DA YAKE CIKI A YANZU
(Mayu 2026)
Tun Disambar 11, 2025, yana tsare a hannun hukumomi (DSS da sojoji) bayan an hana asusunsa na banki. An samo kuɗi kusan Naira miliyan 2 daga wani sojan da ake zargi da shirin juyin mulki. Ana binciken lamarin a matsayin “kuɗin addu’a” (wanda ya zama al’ada a al’ummar Sufi).
Iyalansa (ciki har matar sa Hajiya Ramatu Khalifa Sani Abdulkadir da ’ya’yansa) sun tabbatar da cewa kuɗin al’ada ne na neman addu’a, ba siyasa ba. A watan Maris 2026, an tabbatar da cewa yana raye kuma lafiya a tsare (protective custody). Ana kai shi kotu a Federa

A Kullum Godiyar da Nakewa ALLAH Akan Sha'anin Khalifa Shine, Khalifa Ba ALLAH Yayiwa Laifi Ba, Wani Bawa ne Wanda Ranar...
14/05/2026

A Kullum Godiyar da Nakewa ALLAH Akan Sha'anin Khalifa Shine, Khalifa Ba ALLAH Yayiwa Laifi Ba, Wani Bawa ne Wanda Ranar Ƙiyama a Ɗaɗɗaure Zai zo Fagen Alƙiyama, Shine Yake Ganin Wai Anyi Masa Laifi.

Mun Karɓi Wannan Jarabawa Hannu Bib_Biyu Matsayinmu Na Musulmai, Mun Tabbata Allah Zai Kawowa Khalifa Mafita Nan Kusa Ƙadan. INSHA ALLAHU.

~. Muhammad Bello Agaji

KOTU: Masoya Annabi ﷺ A Ci Gaba Da Addu'a, Allah Ya Nasarci Maulānā Khalipha Da Dukkan Masu Son Ganin Nasarar Shi 🤲
13/05/2026

KOTU: Masoya Annabi ﷺ A Ci Gaba Da Addu'a, Allah Ya Nasarci Maulānā Khalipha Da Dukkan Masu Son Ganin Nasarar Shi 🤲

INNALILLA6HI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN.Ɗaya Daga Cikin Mahaddata Kuŕ'ani Na Farko A Jihar Kogi, Gwani Pa-Ochalifu Ya RasuMa...
12/05/2026

INNALILLA6HI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN.

Ɗaya Daga Cikin Mahaddata Kuŕ'ani Na Farko A Jihar Kogi, Gwani Pa-Ochalifu Ya Rasu

Marigayin, wanda ya kasance babban limami a yankin Okotonwa da ke ƙaramar hukumar Idah a Kogi, ya shahara wajen koyar da addini da haddar Alƙur’ani tsawon shekaru.

Allah Yajiƙanshi Yayi Mishi Rahama..AMIIN 🤲

INNA-LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN 😭Mun samu labarin rasuwar ɗaya daga cikin matasan Ɗariƙar Tijjaniyya, Sayyadi Rufa’i...
10/05/2026

INNA-LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN 😭

Mun samu labarin rasuwar ɗaya daga cikin matasan Ɗariƙar Tijjaniyya, Sayyadi Rufa’i (Labbaika), wanda ya koma ga Mahaliccinsa bayan rayuwa mai cike da hidima da soyayya ga addini.

Rahotanni sun bayyana cewa rasuwar tasa ta jefa ‘yan uwa, abokai da masoya cikin alhini da jimami, musamman matasan Ɗariƙar Tijjaniyya da ya kasance tare da su wajen ayyukan addini da hidimar al’umma.

Marigayin ya kasance matashi mai kyawawan halaye, ladabi da biyayya ga malamai, abin da ya sanya yake da masoya da dama a cikin al’umma.

Ana ci gaba da karɓar saƙonnin ta’aziyya daga mabiyansa da ‘yan uwa, inda ake roƙon Allah Ya jikansa da rahama, Ya gafarta masa, Ya sanya Aljannatul Firdausi ce makomarsa.

🤲 Allah Ya bai wa iyalai da ‘yan uwa haƙurin jure wannan babban rashi

Kuyi following Taskiya Reporters

TIKTOK YA KARESojojin Nigeria sun k**a shahararren dan bindiga Ibrahim Adamu wanda yake yawan yin TikTok a dajin su na t...
10/05/2026

TIKTOK YA KARE

Sojojin Nigeria sun k**a shahararren dan bindiga Ibrahim Adamu wanda yake yawan yin TikTok a dajin su na ta'addanci

Sojoji sun k**a Ibrahim a shingen duba ababen hawa dake yankin Damari, Birnin Gwari jihar Kaduna

Kayan da aka samu a hannunsa sun hada da bindiga kira AK-47, wayoyin hannu da tabar wiwi

Binciken farko da aka yi a wayarsa ya nuna hotunansa da yake Tiktok da na ‘yan bindiga masu dauke da mak**ai

Su Ibrahim dan bindiga Tiktok ya kare kuma, saura a hadu da Allah Madaukakin Sarki a girbi sak**akon ta'addanci

Masallaci Mai cike da Tarihi a Kusfa Zaria, wannan masallaci Jami'ace, Tsangayace, Makarantace da a ke daukan Ilimin Add...
10/05/2026

Masallaci Mai cike da Tarihi a Kusfa Zaria, wannan masallaci Jami'ace, Tsangayace, Makarantace da a ke daukan Ilimin Addini tin safe har dare, kuma ta haifar da wasu makarantu na haddan Alƙur’ani Mai Girma a Zaria

Na dinga ganin sako a na tambaya ta gaskiyar shekarun da ake cewa masallacin tayi na shekaru 500? Gaskiyar magana itace Masallaci ta jima kwarai amma bata k**a hanyar wannan shekarau ba

Zamuzo maku da cikakken bayani da Tarihi na wannan masallaci.

Kungiyar Fityanul Islam reshen jihar Kaduna ta bayyana wasu daga cikin manyan nasarorin da ta samu a karkashin shugabanc...
09/05/2026

Kungiyar Fityanul Islam reshen jihar Kaduna ta bayyana wasu daga cikin manyan nasarorin da ta samu a karkashin shugabancin Sheikh Rabiu Abdullahi Ganganfa.

Nasarorin sun hada da samar da hadin kai tsakanin mabambantan fahimtar addinin Musulunci da kuma kyautata alaka tsakanin Musulmi da wadanda ba Musulmi ba a jihar.

Kungiyar ta kuma bayyana cewa tana gudanar da wayar da kai ga al’umma ta hanyar wa’azi a kananan hukumomi da gundumomin jihar Kaduna domin inganta tarbiyya da fahimtar addini.

Haka kuma, Fityanul Islam ta kafa cibiyar karantar da marayu da masu bukata ta musamman a Nagoyi, Zariya, domin tallafa wa marasa galihu a cikin al’umma.

Kungiyar ta ce tana daukar nauyin yada karatuttukan malamai a kafafen yada labarai irin su talabijin, rediyo da kuma kafafen sada zumunta domin isar da sakon addini da zamantakewa.

Bugu da kari, ta bayyana kyakkyawar alakar da take da ita da gwamnati da masarautu, wadda ke taimakawa wajen samar da guraben ayyukan yi da tallafi ga ‘ya’yan kungiyar.

Fityanul Islam ta kuma ce tana kai ziyara zuwa zawiyoyi da gidajen malamai domin duba halin da suke ciki tare da bayar da gudummawa inda ya dace.

A cewar kungiyar, tana kuma magance duk wata matsala da ta taso tsakanin ‘ya’yanta da masoyanta domin tabbatar da zaman lafiya da fahimtar juna.

Hakazalika, tana shirya tarurruka da ziyarce-ziyarce domin karfafa tafiyar kungiyar da hada kan mambobinta.

Kungiyar ta bayyana cewa tana amfani da kafafen yada labarai, ciki har da rediyo, talabijin, jaridu da kafafen sada zumunta wajen yada ayyukanta ba dare ba rana.

Duk a cikin kokarinta tayi kokari na mallakar katafaren fili domin gina jami’a a jihar Kaduna.

Wannan wasu kenan daga cikin nasarorin wannan kungiya ta Fityanul Islam a jihar Kaduna, karkashin jagorancin Sheikh Rabiu Abdullahi Ganganfa.

DAGA FEDERAL UNIVERSITY OF EDUCATION ZARIA (FUE) WAJEN BUDE MASALLACI.Wurin Bude Masallacin Juma,a Wanda A A Rano Ya Gin...
08/05/2026

DAGA FEDERAL UNIVERSITY OF EDUCATION ZARIA (FUE) WAJEN BUDE MASALLACI.

Wurin Bude Masallacin Juma,a Wanda A A Rano Ya Gina inda Mai Girma Shugaban Fityanul Islam na Jihar Kaduna
Sheikh Rabi,u Abdullahi Ganganfa Zaria Yasamu Halarta.

Mai Girma Shugaba Muna Fatan Alkhairi.

Address

Zaria

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Taskiya Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share