24/04/2026
Zan rufe da labarin malam; wato Shaikh Albaniy Zaria (Rh).
Ana zaune lafiya, malam yana karantarwa. Kwatsam ya rufe makaranta, ya bar gari. Kuma babu ɓoye-ɓoye; kawai yace ya tafi neman kuɗi ne. Ya tafi boko. Malamin yace yana da plan na yadda yake son da’awar ta kasance ne, kuma sai ya ga plan ɗin ba zai fita ba sai da kuɗi.
To madadin ya fara maula wajen attajirai da ƴan kasuwa cewa don Allah su zo su taimaka; ko kuma ya rufe ƙofa da wani ɗan siyasa ya karɓo kwangilar masa kampen, ko ya ringa bambaɗanci, sai yace a’a. Shi da kansa zai nemi kuɗin, sannan ya zo yayi da’awar. Ai su masu kuɗin ba kawuna biyu bane da su. Kai ɗaya da Allah ya basu, shi ma kai ɗaya Allah Ya bashi. Kuma yana da yaƙinin Allah ba marowaci bane; kuma Allah Yana bada dukiya ga wanda ya gadama, har da kafiri mai zagin Allah. Idan Allah Ya ga dama sai ya bashi kuɗi duk da wannan shirkar tasa.
Malam ya ga to sai shi da yake neman kuɗi don ya taimaki addinin Allah, kawai sai kuma ya munanawa Allah zato cewa Allah ba zai bashi ba? Sai yace: a’a. Shi kam ya tafi neman kuɗi. Ai kuwa Allah Ya masa gamo da ƙatar. Ya samu kuɗi sosai wanda a lokacin mu dai bamu san wani malami wanda yake da kuɗi kamarsa ba. Malam attajirin gaske ne. Filaye kawai yake ta siya yana tattali domin gina abubuwan da a lokacin gwamnati kawai muka sani tana ginawa.
Malam ya siya fili hatta wanda yace jami’a zai gina; yana da filin da ya ware don gina gidan marayu; akwai filayen makarantu daban-daban; ga filin gidajen talabijin da rediyo. Da idanuna na ga sanda ya ɗaga takardun filayen nan kaf yace gasu nan ya gama siya! Yace kuma zai bi a hankali ya gina abubuwansa. Babu wanda ya san account number na makarantarsa ta Daarul Hadeethis Salafiyyah, don shi ba taimako yake nema ba. Filayen nan fa ba wai a gefen gari bane. A’a. A cikin Gaskiya Layout. Yanzu da ake magana, full plot ɗaya a gaskiya layout ai ya fi N20 million. Amma Malam ya tanadi filayen abubuwan da zai gina don da’awarsa.
Me ya sa nake bada labarin nan?
Don in ce muku Ustazai fa suna da damar rufe Islamiyyun nan. Su koma JS 1 ne, ko SS 1 ne, ko 100L ne, su yi bokon nan kamar ku. Suna da damar rufe Islamiyyun nan, su shiga kasuwa su nemi nasibi, kuma Allah Ya basu. Daga nan kuma sai me?
Shi Shaikh Albaniy Zaria bayan ya dawo garin, ai kawai duk abinda ya san halal ne, kuma bai saɓawa dokar ƙasa ba, in har yana so, kawai yi yake yi. Duk wanda kuma ya neme shi da rikici, sai yace a shirye yake ayi. To mutum ne, yayi ilimin addini, yayi na bokon, yanzu kuma yana da kuɗin. Sai kuma kace za ka raina masa wayo. Me kake tsammani dama? To shi ya sa ka ji yayi rikici da duk waɗannan shahararrun mutanen da ka ji labari. Asali na shi bane ya tsokane su. Su ne s**a shiga sabgarsa; shi kuma yace basu isa ba.
Yanzu idan Ustazan nan s**a yi ilimin boko s**a samu kuɗi, an faɗa maka ƴan matan unguwanku za su nema da aure? Ai sun wuce nan kuma. Yanzu kaima sun fi ka daraja a scale of materialism; domin su suna da ilimin addini wanda kai baka da shi isasshe. Ka ga matar aure kuwa sai sun darje, sannan su zaɓa. Daga lokacin ne kuma za a ce suna gudun dangi, sun yi kuɗi sun fara wulaƙanta mutane, suna da wahalar mu’amala. To ai dole. Class ɗin ne ba irin na sauran mutane ba. Ka ga dole su ci zamani su ma.
Amma duk kafin wannan ya yiwu, ina so ka sani cewa za su rufe makarantun Islamiyyar ne. Wannan kuma asararka ne, ba tasu ba. Lokacin da Shaikh Albaniy ya rufe makarantarsa ya tafi neman kuɗi, ai ba shi bane yayi rashi. Ɗaliban ne da al’umma masu saurarensa s**a ƙirga losses duk da cewa ba lefi s**a yi ba.
✍️ Ibrahiym A. El-Caleel