SYS TV

SYS TV welcome to zeet hausa bt tv special thank for you contue following this page thanks business name zeetsani entertainment

Wannan Jari Ne Na Naira Dubu 500 Wanda Na Yi Alkawarin Zan Baiwa Duk Wanda Zai Aure Ni, Kawai Abinda Za Ka Yi Shine Ka A...
29/12/2024

Wannan Jari Ne Na Naira Dubu 500 Wanda Na Yi Alkawarin Zan Baiwa Duk Wanda Zai Aure Ni, Kawai Abinda Za Ka Yi Shine Ka Ajiye Min Hotonka, Zan Duba Na Gani Idan Ka Yi Min Zan Yi Ma Magana, Cewar Wannan Budurwar

Me za ku ce?

04/08/2024

tinubu address Nigeria nation �

Tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Kuma Karamin Ministan Tsaro Matawalle Yana Goyon Bayan Ta'addanci A Najeriya - Bello Turji...
21/07/2024

Tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Kuma Karamin Ministan Tsaro Matawalle Yana Goyon Bayan Ta'addanci A Najeriya
- Bello Turji

- Ya ce yana da shaidun da ke tabbatar da wannan ikirari, inda ya ce gwamnatin da ta shude, a karkashin Matawalle ta san kowa a yankin.

Shahararren shugaban ‘yan ta’adda, Bello Turji ya zargi karamin ministan tsaro, Bello Matawalle da hannu wajen tallafawa ta’addanci a Najeriya.

Bello Turji Kachalla, wanda aka fi sani da Turji, sanannen dan ta'adda ne kuma shugaban 'yan fashi da makami wanda ya yi ta kai hare-hare a jihohin arewacin Najeriya da s**a hada da Zamfara, Sokoto da Niger.

Ana zargin shugaban ‘yan ta’addan mai shekaru 28 da haihuwa ya jagoranci wasu ‘yan bindiga daga ranar 4 zuwa 6 ga watan Janairun 2022, inda ‘yan bindiga s**a kashe sama da mutane 200 da s**a hada da mata da kananan yara a jihar Zamfara.

Turji, a wani sabon faifan bidiyo da SaharaReporters ta samu ya yi zargin cewa batun rashin tsaro da ya addabi kasar nan na da cikakken goyon bayan tsohon gwamnan jihar Zamfara kuma karamin ministan tsaro na yanzu.

Ya ce yana da shaidun da ke tabbatar da wannan ikirari, inda ya ce gwamnatin da ta shude, a karkashin Matawalle ta san kowa a yankin.

Da yake magana da harshen Hausa, ya ce, “Sunana Muhammed Bello Turji, kuma na fitar da wannan bidiyon ne domin in isa ga daukacin ‘yan Nijeriya, tun daga shugabanni har zuwa talakawa. Wannan shine sakon da nake so in isar wa kowa

“Batun rashin tsaro da ya addabi kasarmu yana da cikakken goyon bayan gwamnatin da ta shude a jihar Zamfara. Ina da shaidar da za ta goyi bayan wannan ikirari. Gwamnatin da ta shude, karkashin Mai Girma Bello Mattawallen Maradun ( Karamin Ministan Tsaro), sananne ne ga kowa da kowa a yankin.

“Wannan gwamnati ta kasance mai hadin kai wajen tallafawa ta’addanci. Akwai mutane daga Shinkafi, Zurmi, da Issah da ba za su iya musun wannan bidiyo ba.

“Yawancin ‘yan Najeriya, misali wadanda ke Bauchi ko Kaduna, watakila ba su san matsalolin da ke faruwa a Zamfara

Majalisar Wakilai Taki amincewa da kudirin dakatar da Sabon Harajin internet da Babban bankin Najeriya Ya Buƙaci bankuna...
09/05/2024

Majalisar Wakilai Taki amincewa da kudirin dakatar da Sabon Harajin internet da Babban bankin Najeriya Ya Buƙaci bankuna Su fara

A zaman na ran Laraba, Hon. Mansur Manu Soro ya nuna damuwarsa, inda ya nuna cewa shirin karbar harajin bai dace ba, musamman idan aka yi la’akari da kalubalen da ‘yan Najeriya da dama ke fuskanta a halin yanzu.

‘Yan majalisar sun bayyana imanin cewa bai kamata alhakin sarrafa kudaden da aka tara ya kasance ƙarƙashin kulawar mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro ba.

Kakakin majalisar Tajudeen Abbas ya bukaci dan majalisar ya janye kudirin, tare da baiwa shugabannin majalisar damar tattaunawa kan lamarin tare da tantance matakin da ya dace.

SABON NAU’IN HARAJIN JIKI MAGAYI: CBN ya umarci bankuna su riƙa cirar kashi 0.5 na Harajin Daƙile Harƙallar Kuɗaɗe a Int...
08/05/2024

SABON NAU’IN HARAJIN JIKI MAGAYI: CBN ya umarci bankuna su riƙa cirar kashi 0.5 na Harajin Daƙile Harƙallar Kuɗaɗe a Intanet

Yadda zan tsayar da taɓarɓarewar darajar naira – Cardoso, sabon Gwamnan CBN
Daga yanzu duk wani wanda ya tura kuɗaɗe ta hanyar amfani da waya, P.O.S, ATM da sauran hanyoyin hada-hadar tura kuɗaɗe na zamani, to za a riƙa cirar harajin kashi 0.5 da adadin kuɗaɗen da ya tura.

Babban Bankin Najeriya (CBN) ne ya bada wannan umarni ga dukkan bankunan kasuwanci a ƙasar nan baki ɗaya.

Sanarwar da CBN ya fitar a ranar Litinin, na ɗauke da sanarwar cewa za a fara cirar waɗannan kuɗaɗen haraji daga nan da makonni biyu bayan fitar wannan sanarwar.

Sanarwar ta ƙara da cewa tunatarwa ce aka yi wa dukkan bankuna, domin tuni sun san akwai wannan batu a ƙasa kwance, tun ranar 5 ga Yuni, 2018 da aka aika masu da sanarwa mai lamba Ref: BPS/DIR/GEN/CIR/05/008 da kuma ta ranar 8 ga Oktoba, 2018 mai lamba Ref: BSD/DIR/GEN/LAB/11/023, bisa yadda za a bi umarnin Dokar Haramcin Harƙallar Kuɗaɗe ta Intanet da Na’urorin Zamani, ta 2015.

“Duk wanda aka cirar wa kuɗin za rubuta a rasiɗin cirar kuɗi cewa: “Cybersecurity Levy’ a kan sa.

Sanarwar ta ce za a ci tarar bankunan s**a ƙi bin wannan umarnin za su fuskanci tara har ta kashi 2 bisa 100 na adadin yawan kuɗaɗen da aka yi hada-hadar na jimillar shekara ɗaya.

Cikin makon jiya ne dai PREMIUM TIMES Hausa ta buga labarin da Ofishin NSA ya yi kira a riƙa tilasta bin dokar haramta hada-hadar kuɗaɗen harƙalla ta hanyar intanet a Najeriya.

Ofishin Mashawarcin Musamman kan Harkokin Tsaro na Shugaban Ƙasa (NSA), ya yi kira da a tilasta bin doka da odar da ke shimfiɗe a ƙarƙashin Dokar Haramcin Hada-hadar Kuɗaɗen Harƙalla ta Hanyar Intanet, dokar da aka fi sani da ‘cybercrime law’.

Ofishin NSA Nuhu Ribadu ya yi wannan kira a cikin wata sanarwar da ya fitar a ranar Juma’a, bayan wani ƙasaitaccen taron Manyan Jami’an Yaƙi da Ta’addanci ta Ƙarƙashin Ƙasa a Afrika s**a gudanar.

Taron dai kamar yadda sanarwar ta bayyana, an

Shugaba Tinubu zai dawo Najeriya A yau  Laraba Bayan Shafi kwanaki Baya ƙasar Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu zai da...
08/05/2024

Shugaba Tinubu zai dawo Najeriya A yau Laraba Bayan Shafi kwanaki Baya ƙasar

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu zai dawo Abuja daga ƙasar daga Turai, bayan shafe kwanaki ba ya nan.

Mai taimaka wa shugaban kan watsa labarai Ajuri Ngelale ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ran Talata, yana mai cewa shugaban zai koma ne tare da muƙarrabansa da s**a yi bulaguron tare.
Shugaba Tinubu ya yi tafiyar ne tun ranar 23 ga watan Afrilun 2024 zuwa ƙasar Netherlands inda daga can ya wuce Taron Tattalin Arziki na Duniya a ƙasar Saudiyya.

Rashin jin ɗuriyar Bola Tinubu ta sanya an fara yaɗa jita-jitar ba shi da lafiya.

Gwamnatin tarayya ta fito ta bayyana cewa lafiyarsa ƙalau.

A yau ake sa ran Tinubu zai dawo gida Najeriya. www.newhausatop.blogspot.com

Kungiyoyin SERAP Da CISLAC Sun Maida Martani Kan Sabon Harajin Tsaron IntanetWasu matakai da gwamnatin Najeriya ke dauka...
08/05/2024

Kungiyoyin SERAP Da CISLAC Sun Maida Martani Kan Sabon Harajin Tsaron Intanet

Wasu matakai da gwamnatin Najeriya ke dauka a baya bayan nan zasu kara kuntata wa talakawa, musamman a yanayin da ake ciki na matsin tattalin arziki, a cewar shugaban kungiyar CISLAC.

Kungiyar SERAP mai fafutukar yaki da cin hanci a Najeriya ta bukaci shugaban kasa Bola Tinubu da “ya gaggauta” umurtar Babban Bankin Najeriya (CBN) akan ya janye tsarin cire kudi kashi 0.5 cikin 100 akan kudin da aka tura ta asusun banki a Najeriya, da za a yi amfani da su wajen tabbatar da tsaron yanar gizo, saboda matakin ya saba wa tanadin kundin tsarin mulkin Najeriya da kuma hakkokin ‘yan kasa a cewar wata sanarwa da kungiyar ta fidda a shafinta na yanar gizo.

Kungiyar ta SERAP ta ce, “Ya zama wajibi gwamnatin Tinubu ta janye wannan umurni da bankin CBN ya sanar cikin sa’o’i 48 saboda ya saba wa doka.

Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Olayemi Cardoso (Hoto: Facebook/CBN)
Sanarwar ta ce idan ba a janye umarnin cikin sa’o’i 48 ba, kungiyar za ta garzaya kotu.

Da yake maida martani akan batun, Malam Auwal Musa Rafsanjani, shugaban kungiyar CISLAC, mai sa ido kan ayyukan Majalisar Dokoki a Najeriya, ya ce umurnin na CBN zai kara takura wa ‘yan Najeriya musamman marasa karfi da masu matsaikacin karfi, sannan zai yi wuya ‘yan Najeriya su ba da gudummuwarsu wajen habbaka tattalin arzikin kasar idan suna cikin matsatsi.

Auwal Musa Rafsanjani
Auwal Musa Rafsanjani
Bayan cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi a shekarar da ta gabata, da nufin kyautata rayuwar talakawa, har yanzu talakawan basu gani a kasa ba, a cewar Rafsanjani.

A kwanan nan kuma hukumar kula da lantarki ta kasa ta bijiro da matakin yin karin kudin wutar lantarki duk da cewa babu ingantacciyar wuta a sassan kasar da yawa.

Rafsanjani ya kara da cewa matakan da gwamnati ke dauka ba sa taimaka wa jama’a sai dai ma su kuntata musu, shi ya sa yanzu wasu ba sa kai kudadensu banki.

Rage Kudin Wutar 'Band A' Ba Zai Yi Tasiri Ga Halin Kunci Da ‘Yan Kasa Ke Ciki Ba -‘Yan NajeriyaBatun rage farashin wuta...
08/05/2024

Rage Kudin Wutar 'Band A' Ba Zai Yi Tasiri Ga Halin Kunci Da ‘Yan Kasa Ke Ciki Ba
-‘Yan Najeriya

Batun rage farashin wutar lantarki a Najeriya dai na ci gaba da jawo muhawara mai karfi ne tun bayan fito da sanarwa da kamfanin rarraba wutan lantarki na Legas wato Ikeja Electric ya yi a ranar Litinin.

A yayin da ‘yan Najeriya ke kara matsin lamba ga gwamnati a kan kudurori da s**a ce yana kuntatawa ‘yan kasa, wasu ‘yan kasuwa da masu sharhi a kan al’amurran yau da kullum sun ce rage farashin kudin wutan wadanda ke kan tsarin ‘Band A’ ba zai yi tasiri ga yanayin matsin da aka jefa ‘yan kasa a ciki ba, kuma kamata ya yi ana daukan matakan da s**a dace kafin fitar da kuduri ga kasa.

Rahotanni dai sun yi nuni da cewa matakin da kamfanin Ikeja electric ya fitar ya biyo umarnin da gwamnatin kasar ta bayar na amincewa da batun rage farashin wutar ga kwastomomin dake karkashin tsarin Band A biyo bayan kiraye kirayen da ‘yan kasa s**a yi tun ranar 4 ga watan Afrilu da tsarin ya fara aiki.

Wannan lamarin dai ya sanya ‘yan Najeriya cikin wani yanayin matsi kuma rage kudin wutan lantarkin da aka yi ba wani tasirin da zai yi kamar yadda fitacciyar ‘yar kasuwa kuma mazauniyar birnin tarayya Abuja, Hajiya Aisha Abubakar ta fada.

Mai Sharhi a kan al’amurran yau da kullum, Ibrahim Hussain Abdulkarim ya ce a fitar da mataki a janye da gwamnatin nan ta dauki salonsa ba abu ne mai kyau ba ganin irin barnar da ake tafkawa da kudurorin da aka yi ta bullo da su na baya-bayan nan.

A wani bangare kuwa masanin tattalin arziki, Mallam Kasim Garba Kurfi ya ce ragin da aka yi bai taka kara ya karya ba kuma kamata ya yi gwamnati ta kara Ninka kokari wajen kawo wa al’umma sauki.

Idan ana iya tunawa, a farko-farkon watan Afrilun da ta gabata ne gwamnatin Najeriya karkashin jagorancin shugaba Bola Tinubu ta amince da karin kudin wutan lantarki a kan Naira 225 killowatt 1 a sa’a 1 ga masu amfani da wutar lantarki na Band A a kasar.

Matakin da daga bisani ya haifar da rudani a cikin kasar inda

HOTO: Rahotanni na nuna cewa da alamu ko dai motocin hukumar Hisbah sun lalace ko kuma rashin mai yasa ba sa iya zuwa Op...
07/05/2024

HOTO: Rahotanni na nuna cewa da alamu ko dai motocin hukumar Hisbah sun lalace ko kuma rashin mai yasa ba sa iya zuwa Operation Kau da Baɗala da sauran ayyukan gyaran tarbiyya da suke fita....

Mecece shawara?

LIKE // SHARE & FOLLOW US >> Zeet hausa bt tv

Taron Shuwagabannin Addinai a Kasar Malaysia Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi Ya Halarci Taron Shuwagabannin Ad...
07/05/2024

Taron Shuwagabannin Addinai a Kasar Malaysia

Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi Ya Halarci Taron Shuwagabannin Addinai a Kasar Malaysia

Inda Ya Hadu da Shugaban Kasar Malaysia Hadi da Shugan Rabidatul Alam Wal Islamiyya Na Duniya

Alhamdulillah Allah Ya Dawo Mana Dashi Lafiya

Address

Zurmi
6311011

Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00
Saturday 09:00 - 17:00
Sunday 09:00 - 17:00

Telephone

+2349071671930

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when SYS TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to SYS TV:

Share