SHUNI

SHUNI Ingantattun labarai masu ɗaukar hankali—ilimantarwa, faɗakarwa, da nishadantarwa.

A cewar Gwamnan, an gudanar da zaben cikin gaskiya da adalci, wanda ya samar da sababbin shugabanni da za su jagoranci j...
28/09/2025

A cewar Gwamnan, an gudanar da zaben cikin gaskiya da adalci, wanda ya samar da sababbin shugabanni da za su jagoranci jam’iyyar tsawon shekaru hudu masu zuwa.

Fintiri ya kara da cewa gwamnatin jihar da PDP na aiki kafada da kafada wajen tabbatar da kyakkyawan mulki da kuma inganta jin daɗin al’umma.

A zaben da aka gudanar, Alhaji Hamza Madagali ya fito a matsayin sabon Shugaban PDP na Jihar Adamawa, tare da Malam Saleh Shelleng a matsayin sakatare.

APC Ta Ce Maganganun Atiku Kan Harin Boko Haram Cike Suke da MunafunciA cikin wata sanarwa da mai magana da yawunta, Hon...
28/09/2025

APC Ta Ce Maganganun Atiku Kan Harin Boko Haram Cike Suke da Munafunci

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunta, Hon. Mohammed Abdullahi, ya sa hannu, APC ta zargi Atiku da amfani da mummunan harin wajen neman maki na siyasa, maimakon nuna tausayin gaskiya ga mutanen da abin ya rutsa da su, kamar yadda Fombina Times ta ruwaito.

Sanarwar ta ce: “Maimakon Atiku ya tsaya a gefen al’umma, ya fitar da sakon ta’aziyya cike da ƙarya, wuce gona da iri da kuma jirkita gaskiya. Wannan hali ya nuna halin siyasa mai cike da son kai da munafunci.”

APC ta kuma danganta Atiku da gazawa wajen magance matsalar tsaro lokacin da yake a cikin gwamnatin PDP, tana mai cewa “tushen rashin tsaron da ake fama da shi a yau ya samo asali ne daga gazawar wannan gwamnati.”

Haka kuma jam’iyyar ta yi zargin cewa Atiku bai taba kawo muhimman ayyukan raya ƙasa ga jihar ba, illa gina harkokin kasuwancinsa, inda ta ce har ma da garinsa Jada ba ya da ingantaccen ruwa ko hanyoyi har sai lokacin da gwamnatin APC ta yi gyara.

Sanarwar ta ci gaba da tambaya: “Ina Atiku yake lokacin da Boko Haram ta mamaye Madagali, Michika da Mubi? Ina yake lokacin da sansanonin ‘yan gudun hijira s**a mamaye Bajabure, Malkohi da Fufore? Ina yake lokacin da ma’aikatar AUN tasa ta rufe saboda rashin tsaro? Shiru. Bai bayyana ba.”

Sai dai a ƙarshe, jam’iyyar APC ta miƙa ta’aziyya ga al’ummar Wagga Mongoro, ta yi addu’ar samun rahama ga waɗanda s**a mutu da kuma sauƙin jinya ga waɗanda s**a jikkata. Ta kuma tabbatar da aniyar gwamnati wajen kawar da ragowar Boko Haram gaba ɗaya.



Shin Atiku ya yi kuskure wajen yin wannan magana a irin wannan lokaci?

A yayin taron manema labarai da ya gudana a Kano ranar Lahadi, Olorunsola ya ce Shugaba Bola Tinubu da shugaban jam’iyya...
28/09/2025

A yayin taron manema labarai da ya gudana a Kano ranar Lahadi, Olorunsola ya ce Shugaba Bola Tinubu da shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, sun bai wa Kwankwaso kulawa fiye da yadda ya kamata, lamarin da ke janyo ce-ce-ku-ce.

Ya jaddada cewa jam’iyyar na da manyan jiga-jigai a jihar waɗanda za su iya tabbatar da nasarar APC, ciki har da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin; Ƙaramin Ministan Harkokin Gidaje, Yusuf Abdullahi Atah; da Sanata Kawu Sumaila.

A cewarsa, Atah zai fuskanci Gwamna Abba Kabir Yusuf a Kano ta Tsakiya, yayin da Barau Jibrin da tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje za su jagoranci Kano ta Arewa, sannan Kawu Sumaila ya kula da Kano ta Kudu.



Shin jiga-jigan APC a Kano za su iya haɗa kai don kayar da Gwamna Abba a 2027?

28/09/2025

A daren jiya, shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya kai ziyara ga tsohon Ministan Sadarwa, Prof. Isa Ali Pantami (CON), Majidadin Daular Usmaniyya, a Abuja.



Wace rawa kuke ganin malamai da shugabannin siyasa za su taka wajen inganta shugabanci a Najeriya?

27/09/2025

Atiku Abubakar tare da matarsa, T**i, sun halarci bikin ɗaura auren ɗan Rt. Hon. Chibuike Rotimi Amaechi, Chikamkpa da Amaryarsa Anita Akubudike Martin.



📹📽️Shafin Atiku Abubakar

Gwamnan Jihar Adamawa, Rt. Hon. Ahmadu Umaru Fintiri, ya bayar da umurnin sakin Naira biliyan 8 domin biyan bashin fansh...
27/09/2025

Gwamnan Jihar Adamawa, Rt. Hon. Ahmadu Umaru Fintiri, ya bayar da umurnin sakin Naira biliyan 8 domin biyan bashin fansho na ma’aikata da tsoffin ma’aikatan gwamnati a jihar.

Boya ya karɓi lambar yabo daga IBDFM kan jagoranci da hidima ga jama’aHon. Barr. Aliyu Wakili Boya, ɗan majalisar wakila...
27/09/2025

Boya ya karɓi lambar yabo daga IBDFM kan jagoranci da hidima ga jama’a

Hon. Barr. Aliyu Wakili Boya, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Fufore/Song kuma shugaban kwamitin majalisar kan cibiyoyin ‘yan sanda, ya samu lambar yabo ta Excellence Award daga Institute of Business Diplomacy and Financial Management (IBDFM) a matsayin girmamawa ga rawar da yake takawa wajen ci gaban al’umma da jagoranci nagari.

Lambar yabon, wacce aka amince ya cancanta da ita matuƙa, ta tabbatar da jajircewar Boya a fannin ci gaba mai ɗorewa, ayyukan jin ƙai da kuma shugabanci da maida hankali ga jama’a.

Wannan karramawar ta zo a matsayin tabbaci na irin tasirin da ya yi a mazabarsa da ma Najeriya baki ɗaya, wanda ya nuna tafiyar sa tana cike da manufa da hakuri.

⚽ SAKAMAKON WASANNIN YAU🏴 Premier LeagueBrentford 3️⃣ – 1️⃣ Manchester United 😳Manchester City 5️⃣ – 1️⃣ Burnley 🔥Crysta...
27/09/2025

⚽ SAKAMAKON WASANNIN YAU

🏴 Premier League

Brentford 3️⃣ – 1️⃣ Manchester United 😳

Manchester City 5️⃣ – 1️⃣ Burnley 🔥

Crystal Palace 2️⃣ – 1️⃣ Liverpool 😱

Chelsea 1️⃣ – 3️⃣ Brighton (Chelsea sun tashi da jan kati 🔴)

🇪🇸 La Liga

Atlético Madrid 5️⃣ – 2️⃣ Real Madrid 😲🔥

1. Wane sakamako ya fi baka mamaki yau? 🤔

2. Shin kuna ganin United da Chelsea suna cikin matsala?

3. Atlético Madrid sun ci Real da ci 5–2! Me wannan ke nufi ga gasar La Liga?

27/09/2025

Bidiyo da ya jawo ce-ce-ku-ce!
An nuna yadda jami’an tsaron Shugaban Ƙasa s**a dakatar da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso daga wucewa ta gaban tawagar Shugaban Ƙasa.

👉 Me kuke gani a nan: tsauraran matakan tsaro ne, ko rashin girmamawa ga manyan ‘yan siyasa?

26/09/2025

Yayin Tinubu ke gaisawa 🤝 da Kwankwaso
A bikin nadin sabon Olubadan na Ibadanland a Oyo State.

Matatar man fetur ta Dangote ta tabbatar da cewa ta sallami wasu daga cikin ma’aikatanta, tana mai cewa an yi hakan ne a...
26/09/2025

Matatar man fetur ta Dangote ta tabbatar da cewa ta sallami wasu daga cikin ma’aikatanta, tana mai cewa an yi hakan ne a matsayin garambawul don kare martaba da ci gaban kamfanin.

Prof. Nentawe Yilwatda, sabon shugaban APC, ya bayyana cewa ƙofar jam’iyyar tana buɗe ga dukkan waɗanda za su so komawa ...
26/09/2025

Prof. Nentawe Yilwatda, sabon shugaban APC, ya bayyana cewa ƙofar jam’iyyar tana buɗe ga dukkan waɗanda za su so komawa ciki, ciki har da Kwankwaso.

A ganin ku, menene zai sa Kwankwaso yin hakan—manufa ce ko ribar siyasa?

Address

Yirol
640101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when SHUNI posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to SHUNI:

Share