AKSAM MEDIA

AKSAM MEDIA This page was created for News establishment

Kungiyar PENGASSAN ta dauki doka a hannunta tsakanin ta da matatar Dangote
30/09/2025

Kungiyar PENGASSAN ta dauki doka a hannunta tsakanin ta da matatar Dangote

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

Zargin Cin-hanci: ƙasar China ta yanke hukuncin kisa ga tsohon ministan Noma na kasarTsohon Ministan Noma da Harkokin Ka...
28/09/2025

Zargin Cin-hanci: ƙasar China ta yanke hukuncin kisa ga tsohon ministan Noma na kasar

Tsohon Ministan Noma da Harkokin Karkara na kasar Sin an yanke masa hukuncin kisa tare da jinkiri saboda laifin karɓar rashawa a wata kotu da ke lardin Jilin a ranar Lahadi, a cewar kamfanin dillancin labarai na gwamnati, Xinhua.

Xinhau ya ce, Mr. Tang, ya karɓi rashawa, na kuɗi da kadarori da darajarsu ta haura yuan miliyan 268 kimanin (dala miliyan 37.6) a wurare daban-daban da ya rike daga shekarar 2007 zuwa 2024, in ji Xinhua.

Kotun Changchun ta dakatar da aiwatar da hukuncin kisa na tsawon shekaru biyu, tana mai lura da cewa ya amsa laifukansa, in ji rahoton.

Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta kori Tang a watan Nuwamba 2024, watanni shida bayan hukumar yaki da cin hanci ta fara bincikensa tare da kwance masa mukami.

An karrama wani Dalibin Sakandire bisa wata bajinta da yayi a Ƙasar Dubai.Rundunar yan sanda ta Al Qusais a kasar Dubai ...
28/09/2025

An karrama wani Dalibin Sakandire bisa wata bajinta da yayi a Ƙasar Dubai.

Rundunar yan sanda ta Al Qusais a kasar Dubai takarram wani Dalibi bisa gaskiyar da ya yi na mayar da wallet da cakin banki da ya tsinta mai ɗauke da Dirham 200,000

Dalibin ya karbi kyautar girmamawar ne daga sashin "We Reach You to Thank You" initiative, dake cikin rundunar yan sanda ta Dubai.

NATO ta rage motsi a Poland bayan harin Rasha a Ukraine.A yanzu haka sararin samaniyar Poland ya yi shiru bayan da NATO ...
28/09/2025

NATO ta rage motsi a Poland bayan harin Rasha a Ukraine.

A yanzu haka sararin samaniyar Poland ya yi shiru bayan da NATO ta janye jiragen yaƙi da kayan tsaro.

Wannan ya biyo bayan mummunan harin sama da Rasha ta kai Ukraine. Sojojin Poland sun ce yanzu komai ya lafa, amma ba a cika yarda da Rasha za ta tsaya ba.

27/09/2025
Ƙasar Iran ta kira jakadunta daga Birtaniya, Faransa da Jamus bayan da MDD ta mayar mata takunkumin.”
27/09/2025

Ƙasar Iran ta kira jakadunta daga Birtaniya, Faransa da Jamus bayan da MDD ta mayar mata takunkumin.”

Sheikh Qaribullah Sheikh Nasiru Kabara ya magantu kan Malam ƙungiyar Izala da suke kare dayan su da yayi batanci ga Anna...
27/09/2025

Sheikh Qaribullah Sheikh Nasiru Kabara ya magantu kan Malam ƙungiyar Izala da suke kare dayan su da yayi batanci ga Annabi Muhammad S.A.W

Malamin ya ce babban abin Kunya ne su fito suna kare wanda ya yi batanci ga shugaban Halittar Allah Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama

Tsohon shugaban Amurka Barack Obama ya nemi a ware kasar Palastinu daga Isra'ila.Shugaban ya bayyana hakan ne yana mai s...
27/09/2025

Tsohon shugaban Amurka Barack Obama ya nemi a ware kasar Palastinu daga Isra'ila.

Shugaban ya bayyana hakan ne yana mai s**ar abin da Sojojin ƙasar yahudu ke ci gaba da yi a Gaza.

“Amurka ta Hana Jami’an Iran a Majalisar Dinkin Duniya ‘Yawon Siyayya’”Jami’an Iran da s**a halarci taron Majalisar Dink...
24/09/2025

“Amurka ta Hana Jami’an Iran a Majalisar Dinkin Duniya ‘Yawon Siyayya’”

Jami’an Iran da s**a halarci taron Majalisar Dinkin Duniya a wannan makon ba za su iya yin siyayya a New York ba, bayan da gwamnatin Amurka ta hana su sayen komai daga kayan gida da yawa har zuwa agogon alfarma.

Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ya bayyana waɗannan takurawa ga bakin Iran a matsayin wani ɓangare na “matsin lamba na ƙarshe.”

Yanzu-yanzu: ƙasar China na neman zama ƙasa mai riƙe da kanbun zinare na kasashen DuniyaHakan na nufin “China na shirin ...
23/09/2025

Yanzu-yanzu: ƙasar China na neman zama ƙasa mai riƙe da kanbun zinare na kasashen Duniya

Hakan na nufin “China na shirin zama mai kula da ajiyar zinaren kasashen Duniya.

Address

Istanbul

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AKSAM MEDIA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AKSAM MEDIA:

Share