AKSAM MEDIA

AKSAM MEDIA This page was created for News establishment

Pakistan ta yabi Najeriya Bisa sayen jirgin yaƙi na JF-17 Thunder Block-II don Rundunar Sojin SamaAn bayyana godiya ga N...
23/11/2025

Pakistan ta yabi Najeriya Bisa sayen jirgin yaƙi na JF-17 Thunder Block-II don Rundunar Sojin Sama

An bayyana godiya ga Najeriya bisa zaɓen jirgin yaki na JF-17 Thunder Block-II domin ƙarfafa Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF).

A cikin saƙon, an bayyana fatan ƙarin haɗin gwiwa a nan gaba kadan tsakanin ƙasashn biyu, tare da addu’ar Allah Madaukaki Ya albarkaci kasashen. Ameen.

Source Pakistan strategic Forum

Yanzu-yanzu: Gwamnan Yobe ya Bayar da Umarin Rufe Dukkan Makarantun Kwana Nan takeGwamnatin Jihar Yobe ta umarci a rufe ...
23/11/2025

Yanzu-yanzu: Gwamnan Yobe ya Bayar da Umarin Rufe Dukkan Makarantun Kwana Nan take

Gwamnatin Jihar Yobe ta umarci a rufe dukkan makarantun sakandare na kwana a fadin jihar a matsayin matakin kariya domin tabbatar da tsaron daliban da ke makarantun.

Wannan mataki ya biyo bayan wani taron tsaro da ya gudana tsakanin Gwamna Mai Mala Buni da shugabannin hukumomin tsaro na jihar, inda s**a tattauna kan matsalolin tsaro da ke faruwa a wasu makarantun kasar nan.

Wata sanarwa da Sakatare Din-din-din na Ma’aikatar Ilimi ta Firamare da Sakandare, Dr. Bukar Aji Bukar, ya sanya wa hannu ta umarci a rufe dukkan makarantun sakandare nan take har sai an sami ci gaba a yanayin tsaro.

Gwamna Buni ya kira al’ummar jihar da su ci gaba da yin addu’a ga shugabanni, jami’an tsaro, zaman lafiya da ingantuwar tsaro a fadin kasa.

YANZU-YANZU: Kotu ta umarci Gwamnatin tarayya ta zayyana sunayen mutanen da s**a sace sama da  tiriliyon 6 a hukumar NDD...
23/11/2025

YANZU-YANZU: Kotu ta umarci Gwamnatin tarayya ta zayyana sunayen mutanen da s**a sace sama da tiriliyon 6 a hukumar NDDC

Babbar Kotun Tarayya da ke zama a Abuja ta yanke hukunci na tarihi, inda ta umarci Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarni ga Ofishin Babban Lauyan Ƙasa (AGF) da Ministan Shari’a su fitar da sunayen mutanen da ake zargi da wawurar sama da naira tiriliyan N6 da aka ware domin aiwatar da ayyukan da aka yi watsi da su — guda 13,777, da kuma kudaden gudanar da Hukumar Raya Yankin Niger Delta (NDDC) daga shekara ta 2000 zuwa 2019.

Kotun ta kuma umarci shugaban ƙasar ya wallafa kuma ya bai wa jama’a cikakken rahoton binciken kwararru (forensic audit) na NDDC wanda aka mika wa gwamnatin tarayya a ranar 2 ga Satumba, 2021.

Kasafin kuɗi na Tiriliyon guda da doriya yasa wani matashi yin tattaki daga Kaduna zuwa Kano domin jinjina wa Gwamnan Ka...
23/11/2025

Kasafin kuɗi na Tiriliyon guda da doriya yasa wani matashi yin tattaki daga Kaduna zuwa Kano domin jinjina wa Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf.

Matashin mai suna, Yusuf Umar Haskiya, ya ce ya ga dacewar yin tattakin ne domin ya samu ya ga Gwamnan Kano Abba Gida-gida kasancewar sa mai kishin al'ummar da ya mulka ta Hanyar gwangwaje su da managartan ayyukan cigaba.

Haskiya, bayan shafe kwanaki tara yana tafiya da Kafa Domin ya ga Gwamna Abba Gida-gida ya ce "Da ana sauya Gwamna da sun baiwa kanawa Gwamna Uba Sani su karbi Gwamna Abba Kabir Yusuf "saboda Yadda yake kawowa al'ummar Kano tagomashi kala-kala na domin dimokuraɗiyya.

Ya ce yana roƙon makusantan Gwamnan Kano da suyi wa Allah su yi masa hanya ya ga Gwamna Abba Gida-gida Ido da Ido domin cikar burin sa ko ya yi bacci da munshari

Ba zan bar jini ya cigaba da zuba a Arewa ba, zan magance matsalar tsaro: Shugaban Tinibu Shugaba Bola Tinubu ya ce gwam...
23/11/2025

Ba zan bar jini ya cigaba da zuba a Arewa ba, zan magance matsalar tsaro: Shugaban Tinibu

Shugaba Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa ba za ta bar Arewa ta ci gaba da zubar da jini ba, tare da tabbatar da cewa za a kawo ƙarshen matsalolin tsaro da s**a haɗa da ta’addanci da ’yan fashi da makami a arewacin Najeriya.

Tinubu ya bayyana cewa babu wani bangare na ƙasar da za a bari “ya ci gaba da zubar da jini yayin da gwamnatin tarayya ke kallo kawai”.

An isar da sakon shugaban ne a ranar Asabar yayin bikin cika shekaru 25 da kafuwar Arewa Consultative Forum (ACF) da aka gudanar a Kaduna. Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ne ya wakilci Shugaban Ƙasa a taron.

Shugaba Tinubu ya ce ya gaji matsalar tsaro mai “tsanani”, amma ya kuduri aniyar dawo da zaman lafiya a fadin ƙasa.

Haka kuma ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta farfaɗo da tattalin arzikin yankin Arewa, yana mai jaddada fatan fara fitar da danyen mai daga gonakin Kolmani da kuma wasu sabbin damar cigaba da ake sa ran za su farfado da tattalin arziki.

AIG, Aishatu Abubakar ya Zama shugabar kungiyar jami'an tsaro Mata ta Afrika Mataimakiyar Sufeto Janar na 'Yan Sandan Na...
23/11/2025

AIG, Aishatu Abubakar ya Zama shugabar kungiyar jami'an tsaro Mata ta Afrika

Mataimakiyar Sufeto Janar na 'Yan Sandan Najeriya, AIG Aishatu Abubakar Ta Zama Mace Ta Farko Da Ta Zama Shugabar Ƙungiyar Jami'an Tsaro Mata Ta Kasashen Afrika, Wato (African Women In Law Enforcement Association) a Taron G20 da ya gudana a Birnin Johannesburg Na Kasar Afrika Ta Kudu

Iran na shirin fitar da nata tsarin kwamfuta (operating system) na farko, wanda za a yi amfani da shi wajen sarrafa taur...
23/11/2025

Iran na shirin fitar da nata tsarin kwamfuta (operating system) na farko, wanda za a yi amfani da shi wajen sarrafa tauraron dan’adam, wayoyin salula da kuma tsaron bayanai na ’yan ƙasar.

Wannan mataki na nufin kawo ƙarshen dogaro da tsarin iOS, Microsoft da kuma wasu shirye-shiryen kasar China.

Da wannan sabon ci gaban, Iran za ta zama ƙasar farko da za ta gudanar da dukkan harkokinta na soja, farar hula da tsaron yanar gizo ta amfani da cikakken tsarin fasaha na cikin gida.

Pakistan ta rattaba hannu kan yarjejeniyar dala biliyan 5 da China domin sayen jiragen ruwa masu nutsewa guda takwas (Ha...
22/11/2025

Pakistan ta rattaba hannu kan yarjejeniyar dala biliyan 5 da China domin sayen jiragen ruwa masu nutsewa guda takwas (Hangor-class diesel-electric submarines).

An tsara cewa guda huɗu za a gina su a China, sauran huɗun kuma za a haɗa su a Pakistan karkashin tsarin musayar fasaha.

Yanzu-yanzu: Iran na shirin gwada Nuclear weapon da ta kammala, Mai haɗe da fasahar LaserRahotanni daga jaridar Daily Ir...
22/11/2025

Yanzu-yanzu: Iran na shirin gwada Nuclear weapon da ta kammala, Mai haɗe da fasahar Laser

Rahotanni daga jaridar Daily Iran News sun bayyana cewa Iran ta zama ƙasa mai makamin nukiliya, kuma yanzu tana shirin gwada makamin ta na nukiliya ta amfani da fasahar laser ba tare da yin fashewar gwaji ba.

Aljeriya da Najeriya suna shirin kaddamar da gagarumin luguden wuta ta jiragen sama kan Boko Haram da ake zargin Amurka ...
22/11/2025

Aljeriya da Najeriya suna shirin kaddamar da gagarumin luguden wuta ta jiragen sama kan Boko Haram da ake zargin Amurka ke tallafawa a Yankin Yammacin Sahara.

Najeriya ta zargi USAID da bayar da kuɗaɗen da ba bisa ka’ida ba ga kungiyar Boko Haram, wadda ake ɗauka a matsayin ɗaya daga cikin kungiyoyin ta’addanci mafi haɗari a Afirka.

China da Rasha da Koriya ta Arewa sun ci alwashin tallafawa wajen hana kifar da gwamnatin Imam Khumaini Rahotanni na nun...
21/11/2025

China da Rasha da Koriya ta Arewa sun ci alwashin tallafawa wajen hana kifar da gwamnatin Imam Khumaini

Rahotanni na nuna cewa China, Russia da Koriya ta Arewa sun bayyana matsayin su na kin amincewa da duk wani yunƙuri da zai haifar da rushewa ko kifar da gwamnatin Iran, duk da matsin lambar da ake danganta da bukatar Isra’ila na ganin an samu sauyin mulki a Tehran.

Kasashen uku, waɗanda ke da karfi a fannin tsaro da siyasa, sun sha alwashin tsayawa tare da Iran a duk wani yanayi da zai iya haifar da rikici ko barazana ga tsaron yankin. Rahoton ya ce wannan matsayi na iya ƙara taka rawa a rikice-rikicen siyasar duniya, musamman tsakanin manyan kasashen duniya.

Rashin halartar Trump ya ba wa China damar jagoranci a taron G20Rashin kasancewar shugaban Amurka Donald Trump a taron G...
21/11/2025

Rashin halartar Trump ya ba wa China damar jagoranci a taron G20

Rashin kasancewar shugaban Amurka Donald Trump a taron G20 ya buɗe wata mahangar sabon gurbin jagoranci ga China a muhimmin dandalin kasa da kasa.

Masana na cewa wannan gibi na ba wa Beijing damar ƙara tasiri da muradunta wajen tsara tattaunawar tattalin arziki da siyasa a cikin ƙungiyar manyan kasashe.

Address

Istanbul

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AKSAM MEDIA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AKSAM MEDIA:

Share