
07/28/2025
GASKIYAR YADDA AKA KASHE SARDAUNA AHAMADU BELLO A JUYIN MULKI NA 1966🔥
A daren 15 ga Janairu, 1966, Najeriya ta shiga wani mawuyacin hali. Wasu sojoji, mafi yawansu daga Kabilar Ibo, s**a shirya juyin mulki na farko a tarihin ƙasar nan. Sun haɗa kai suna cewa za su “gyara Najeriya”, amma abin da s**a yi ya nuna ƙiyayya da ƙabilanci — musamman ga ‘yan Arewa da musulmai.
Jagoran harin a Arewa shi ne Major Chukwuma Kaduna Nzeogwu, dan kabilar Ibo daga kudancin Najeriya. Ya shirya harin kai tsaye a gidan Sardauna Ahmadu Bello a Kaduna, wanda ya kasance jagoran Arewacin Najeriya kuma Firayim Minista na yankin.
ME YA FARU?
Da misalin ƙarfe 2 na dare, sojojin Nzeogwu s**a kewaye gidan Sardauna da manyan bindigogi. Sun fara harbe-harbe, s**a tilasta masu gadi bude kofar gidan. Bayan sun shiga, s**a kashe Sardauna a gaban mai gadin. Har ma wasu na cewa s**a jefawa gawarsa bam bayan sun harbe shi, domin su tabbatar da ya mutu gaba ɗaya.
Matarsa Hafsatu da wasu daga cikin bayinsa suma aka kashe. Babu tsoron Allah, babu kunya, babu mutunci.
ME YA BIYO BAYA?
Arewa ta fusata. Jama’a s**a fahimci cewa wannan ba gyara ba ne, akidar kabilanci ce kawai, domin mafi yawancin wadanda aka kashe musulmai ne, kuma ‘yan Arewa.
An sauya gwamnati aka nada Major General Johnson Aguiyi Ironsi (Ibo) a matsayin Shugaban Kasa. Hakan ya kara janyo fushi, domin ana kallon k**ar “harin Ibo ne akan Arewa”.
Wannan ne ya haifar da mayar da martani daga sojojin Arewa a juyin mulki na Yuli 1966, inda aka kashe Ironsi da wasu manyan Ibo. Wannan ya kawo tashin hankali, kisan al’umma, da kuma farawar yaki na basasa (Nigerian Civil War)