Mukhtar Yusuf

Mukhtar Yusuf FAN-AREWA

GASKIYAR YADDA AKA KASHE SARDAUNA AHAMADU BELLO A JUYIN MULKI NA 1966🔥A daren 15 ga Janairu, 1966, Najeriya ta shiga wan...
07/28/2025

GASKIYAR YADDA AKA KASHE SARDAUNA AHAMADU BELLO A JUYIN MULKI NA 1966🔥

A daren 15 ga Janairu, 1966, Najeriya ta shiga wani mawuyacin hali. Wasu sojoji, mafi yawansu daga Kabilar Ibo, s**a shirya juyin mulki na farko a tarihin ƙasar nan. Sun haɗa kai suna cewa za su “gyara Najeriya”, amma abin da s**a yi ya nuna ƙiyayya da ƙabilanci — musamman ga ‘yan Arewa da musulmai.

Jagoran harin a Arewa shi ne Major Chukwuma Kaduna Nzeogwu, dan kabilar Ibo daga kudancin Najeriya. Ya shirya harin kai tsaye a gidan Sardauna Ahmadu Bello a Kaduna, wanda ya kasance jagoran Arewacin Najeriya kuma Firayim Minista na yankin.

ME YA FARU?

Da misalin ƙarfe 2 na dare, sojojin Nzeogwu s**a kewaye gidan Sardauna da manyan bindigogi. Sun fara harbe-harbe, s**a tilasta masu gadi bude kofar gidan. Bayan sun shiga, s**a kashe Sardauna a gaban mai gadin. Har ma wasu na cewa s**a jefawa gawarsa bam bayan sun harbe shi, domin su tabbatar da ya mutu gaba ɗaya.

Matarsa Hafsatu da wasu daga cikin bayinsa suma aka kashe. Babu tsoron Allah, babu kunya, babu mutunci.

ME YA BIYO BAYA?

Arewa ta fusata. Jama’a s**a fahimci cewa wannan ba gyara ba ne, akidar kabilanci ce kawai, domin mafi yawancin wadanda aka kashe musulmai ne, kuma ‘yan Arewa.

An sauya gwamnati aka nada Major General Johnson Aguiyi Ironsi (Ibo) a matsayin Shugaban Kasa. Hakan ya kara janyo fushi, domin ana kallon k**ar “harin Ibo ne akan Arewa”.

Wannan ne ya haifar da mayar da martani daga sojojin Arewa a juyin mulki na Yuli 1966, inda aka kashe Ironsi da wasu manyan Ibo. Wannan ya kawo tashin hankali, kisan al’umma, da kuma farawar yaki na basasa (Nigerian Civil War)

Abba Gida gida ya kyauta.
07/28/2025

Abba Gida gida ya kyauta.

07/28/2025

Sowore ya tabo madugu fa.

Egyptian Museum"Unveiling History: The 4,500-Year-Old Tunic at the Egyptian Museum"       🌹🌹🌹🌹"Unveiling History: The 4,...
07/28/2025

Egyptian Museum"Unveiling History: The 4,500-Year-Old Tunic at the Egyptian Museum" 🌹🌹🌹🌹"Unveiling History: The 4,500-Year-Old Tunic at the Egyptian Museum"😱🥰🇯🇴😊

NAJERIYA TA ƘIRƘIRI MAKAMIN ZAMANI:Najeriya ta ƙaddamar da sabon makami mai kaifin basira mai suna EPX‑10, k**ar drone n...
07/28/2025

NAJERIYA TA ƘIRƘIRI MAKAMIN ZAMANI:

Najeriya ta ƙaddamar da sabon makami mai kaifin basira mai suna EPX‑10, k**ar drone ne mai gurneti da ke kai farmaki ba tare da abokan gaba ko yan ta’adda sun ganshi ba.

Wannan ya nuna cewa Najeriya tana tashi tsaye wajen ƙarfafa fasahar tsaro da dogaro da kai. EPX‑10 ya nuna ƙwazon injiniyoyin mu da ƙarfin masana’antar soja ta gida.

Tarihin Mamman Vatsa: Abubuwan da s**a kai ga kisan saA shekarar 1985, bayan jan ragamar mulki da Janar Ibrahim Badamasi...
07/28/2025

Tarihin Mamman Vatsa: Abubuwan da s**a kai ga kisan sa

A shekarar 1985, bayan jan ragamar mulki da Janar Ibrahim Badamasi Babangida ya yi, kasar Najeriya ta shiga wani sabon yanayi na siyasa. A cikin wannan lokaci, an zargi Marigayi Major General Mamman Vatsa – wanda ya kasance babban amini, abokin karatu kuma abokin tafiyar Babangida tun daga makarantar sojoji har girman su a gidan soja – da hannu a yunkurin juyin mulki a watan Disambar 1985.

An k**a shi tare da wasu jami’an sojoji da dama bisa zargin cewa suna shirin kifar da gwamnati aminin sa Babangida. Bayan shari’ar kotun soja, an same su da laifi. Duk da rokon gafara daga ‘yan kasa da manyan mutane s**ayi, gwamnati ta dage cewa dole ne a aiwatar da hukuncin kisa don zama darasi ga sauran sojoji.

A ranar 5 ga Maris, 1986, an kashe Mamman Vatsa da wasu jami’an soja 9 ta hanyar harbi. Wannan lamari ya bar tarihi mai nauyi, inda mutane da yawa ke ganin kisan nasa ya shafi siyasa fiye da shari’a.

Shin kuna ganin hukuncin da aka yi wa Mamman Vatsa ya dace ne ko kuwa siyasa ce ta rinjayi adalci?

A yau muna tunawa da Lieutenant William Walbe, ɗan asalin Jihar Filato, ɗaya daga cikin jaruman sojojin Arewa da s**a ta...
07/27/2025

A yau muna tunawa da Lieutenant William Walbe, ɗan asalin Jihar Filato, ɗaya daga cikin jaruman sojojin Arewa da s**a taka muhimmiyar rawa a juyin mulkin ramuwar gayya na ranar 29 ga Yuli, 1966.

William Walbe daya ne daga cikin masu kula da tsaron lafiyar Janar Aguiyi-Ironsi, shugaban kasa na mulkin soja a wancan lokaci. Amma duk da wannan matsayin nasa na kusa da shugaban kasa, ya kasance ɗaya daga cikin sojojin da s**a taimaka wajen cafke Ironsi a Ibadan, tare da Lieutenant Colonel Theophilus Danjuma.

Wannan juyin mulki na biyu ya zo ne a matsayin ramuwar gayya bisa kisan da aka yi wa shahararrun shugabannin Arewa irin su:

• Sir Ahmadu Bello
• Tafawa Balewa
• Brigadier. Maimalari
• Lt. Col. Yakubu Pam

William Walbe ya tsaya tsayin daka wajen kare muradun yankin Arewa a lokacin da kasar ke cikin rikici da rudani. Ko da yake ba a cika ambaton sunansa ba k**ar wasu, amma rawar da ya taka ba za a manta da ita ba.

5d mark 4 with three lenses50mm (F 1., 24-105mm (F4.0) and 16-35mm (F2.Everything going for 6.5Million There's room for ...
07/26/2025

5d mark 4 with three lenses
50mm (F 1., 24-105mm (F4.0) and 16-35mm (F2.
Everything going for 6.5Million There's room for Negotiation

Dan Bello sun gyara wannan aji a kudi Naira Miliyan uku da dubu dari shida kachal.
07/26/2025

Dan Bello sun gyara wannan aji a kudi Naira Miliyan uku da dubu dari shida kachal.

07/26/2025

Allah ya yi wa Sarkin Katsinan Gusau, Dakta Ibrahim Bello rasuwa a daren Juma'a bayan jinya a wani asibiti da ke Abuja.

Ya rasu yana da shekara 71 kuma za a yi jana'izarsa bayan Sallar Juma'a a garin Gusau da ke jihar Zamfara.

An naɗa marigayin ne a matsayin Sarkin Katsinan Gusau na 15 a watan Maris shekarar 2015.

Ƙarin bayani - https://bbc.in/456gahY

TA FARU TA KARE SUMAYYA
07/25/2025

TA FARU TA KARE SUMAYYA

Address

Oklahoma City, OK
840223

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mukhtar Yusuf posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mukhtar Yusuf:

Share