GTA Hausa

GTA Hausa Wannan Shafin Na Amurka Ke Magana GTAHausa, an bude shi ne don samar da labarai da dumi-dumin su a duk fadin Duniya.

GOSERC Ta NemI Haɗin Kan Masu Ruwa Da Tsaki Wajen Inganta Wutar Lantarki A GombeHukumar Kula da Wutar Lantarki ta Jihar ...
09/17/2026

GOSERC Ta NemI Haɗin Kan Masu Ruwa Da Tsaki Wajen Inganta Wutar Lantarki A Gombe

Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Jihar Gombe, Gombe State Electricity Regulatory Commission (GOSERC), ta gudanar da taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki domin wayar da kansu kan hurumin hukumar, manufofinta da kuma nauyin da aka dora mata. Taron da aka gudanar a hedikwatar hukumar da ke Gombe, ya samu halartar wakilan kungiyoyi daban-daban, ciki har da Ƙungiyar Masu Nika Gyada, Ƙungiyar Masu Samar da Ruwan Sha a Roba, COREN, ASUU, sarakunan gargajiya da sauran masu ruwa da tsaki....

Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Jihar Gombe, Gombe State Electricity Regulatory Commission (GOSERC), ta gudanar da taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki domin wayar da kansu kan hurumin hukumar…

Ranar Zaman Lafiya: Pastor Yohanna Buru Ya Jagoranci Tawagar Kiristoci Zuwa JNI KadunaKafin bikin Ranar Zaman Lafiya ta ...
09/17/2026

Ranar Zaman Lafiya: Pastor Yohanna Buru Ya Jagoranci Tawagar Kiristoci Zuwa JNI Kaduna

Kafin bikin Ranar Zaman Lafiya ta Duniya ta 2026, wata tawaga ta malaman Kirista ƙarƙashin jagorancin Fasto Dr. Yohanna Buru, Babban Mai Kula da Christian Evangelical and Life Intervention Ministry a Jihar Kaduna, ta ziyarci hedikwatar Najeriya ta Jama’atu Nasril Islam (JNI) da ke Kaduna, domin ƙarfafa alaƙar Kirista da Musulmi da kuma inganta zaman lafiya, fahimtar juna da haɗin kan ƙasa....

Kafin bikin Ranar Zaman Lafiya ta Duniya ta 2026, wata tawaga ta malaman Kirista ƙarƙashin jagorancin Fasto Dr. Yohanna Buru, Babban Mai Kula da Christian Evangelical and Life Intervention Ministr…

Burkina Faso Ta Fara Kera Motocin YaƙiBurkina Faso 🇧🇫: Yanzu sojoji na kera nasu motocin. Sojojin kasar sun gabatar da s...
09/17/2026

Burkina Faso Ta Fara Kera Motocin Yaƙi

Burkina Faso 🇧🇫: Yanzu sojoji na kera nasu motocin. Sojojin kasar sun gabatar da sabon rukunin motocin yaki masu sulke da aka kera a cikin gida a hukumance domin fara amfani da su, wadanda aka yi wa lakabi da "Made in Burkina" (Wanda aka kera a Burkina).

Burkina Faso 🇧🇫: Yanzu sojoji na kera nasu motocin. Sojojin kasar sun gabatar da sabon rukunin motocin yaki masu sulke da aka kera a cikin gida a hukumance domin fara amfani da su, wadanda aka yi …

09/17/2026

Jami’an ’Yan Sanda Daga Kamaru Da Kongo Sun Karɓi Takardun Shaida Bayan Kammala Horo

Daga Mamman Awwal Garba a Kamaru A birnin Yaoundé Filin Makarantar Horar da 'Yan Sanda na karɓar baƙuncin wani babban taron bikin a ranar alhamis 17 ga watan Satumba, 2026, wanda aka shirya domin karrama ƙwararru da kuma bikin kammala karatun rukunin jami'an da s**a kammala horonsu. Ana karrama jami'an 'yan sandan da s**a nuna kwazo da jajircewa a yayin gudanar da ayyukansu a ranar 20 ga watan Mayu, 2026....

https://gtahausa.com/jamian-yan-sanda-daga-kamaru-da-kongo-sun-kar%c9%93i-takardun-shaida-bayan-kammala-horo/

Mutane 13 Sun Rasa Rayukansu A Sabon Harin Boko Haram A MadegwaDaga Mamman Awwal Garba Kamaru: Ana ci gaba da shirye-shi...
09/17/2026

Mutane 13 Sun Rasa Rayukansu A Sabon Harin Boko Haram A Madegwa

Daga Mamman Awwal Garba Kamaru: Ana ci gaba da shirye-shiryen binne mutane 13 da 'yan ta'addar Boko Haram s**a kashe a wani hari na kisan gilla da s**a kai da misalin karfe 3 na safiyar yau a Madegwa, a yankin Arewa mai Nisa a kasàr kamaru.

Daga Mamman Awwal Garba Kamaru: Ana ci gaba da shirye-shiryen binne mutane 13 da ‘yan ta’addar Boko Haram s**a kashe a wani hari na kisan gilla da s**a kai da misalin karfe 3 na safiya…

NCCE Za Ta Ƙarfafa Koyar Da Sana’o’i A Kwalejojin IlimiYa kamata yankin Arewa maso Gabashin Najeriya ya sake duba tare d...
09/17/2026

NCCE Za Ta Ƙarfafa Koyar Da Sana’o’i A Kwalejojin Ilimi

Ya kamata yankin Arewa maso Gabashin Najeriya ya sake duba tare da sauya tsarin iliminsa baki ɗaya, domin samar da waɗanda s**a kammala karatu da za su iya ƙirƙirar damar aiki maimakon jira a samar musu da ayyukan yi, in ji Mataimakin Gwamnan jihar Gombe, Dakta Manassah Daniel Jatau. Jatau ya bayyana hakane a Gombe lokacin da Sakatariyar Zartarwa na Hukumar Kula da Kwalejojin Ilimi ta Ƙasa (NCCE), Dakta Angela Ajala, ta jagoranci shugabannin Kwalejojin Ilimi daga jihohin Arewa maso Gabas zuwa ziyarar ban-girma ga gwamnatin jihar Gombe....

Ya kamata yankin Arewa maso Gabashin Najeriya ya sake duba tare da sauya tsarin iliminsa baki ɗaya, domin samar da waɗanda s**a kammala karatu da za su iya ƙirƙirar damar aiki maimakon jira a sama…

Rundunar ’Yan Sandan Gombe Ta Raba Makuden Kudade Ga Iyalan Jami’an Da S**a RasuRundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta gaba...
09/16/2026

Rundunar ’Yan Sandan Gombe Ta Raba Makuden Kudade Ga Iyalan Jami’an Da S**a Rasu

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta gabatar da cakunan inshorar rayuwa da inshorar hatsari na ƙungiya, waɗanda jimillar kuɗinsu ta kai naira miliyan 14.55, ga iyalai 21 na ’yan sandan da s**a rasu ko s**a samu raunuka. A cikin wata sanarwa da Kakakin Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ya rabawa manema labarai, an bayyana cewa Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Umar Ahmed Chuso, ne ya gabatar da cakunan a hedikwatar rundunar da ke Gombe, a wani mataki na tallafa wa jami’an ’yan sanda da iyalansu....

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta gabatar da cakunan inshorar rayuwa da inshorar hatsari na ƙungiya, waɗanda jimillar kuɗinsu ta kai naira miliyan 14.55, ga iyalai 21 na ’yan sandan da s**a rasu…

Maryam Dan’azumi Ta Zama Abin Alfahari Ga Najeriya Bayan Lashe Gasar Alƙur’ani Ta DuniyaGwamnan jihar Gombe a Najeriya M...
09/15/2026

Maryam Dan’azumi Ta Zama Abin Alfahari Ga Najeriya Bayan Lashe Gasar Alƙur’ani Ta Duniya

Gwamnan jihar Gombe a Najeriya Muhammadu Inuwa Yahaya ya gabatar da Maryam Ibrahim Dan’azumi, mai shekaru 19, wadda ta lashe gasar Alƙur’ani ta ƙasa da ƙasa ta Sarki Abdulaziz karo na 46 a Saudiyya, ga Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya, Sanata Oluremi Tinubu, a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja. Maryam, wadda take karatu a makarantar Abubakar Siddiq Community Islamic School for Qur’anic Memorization da ke Gombe, ta zama zakarar gasar bayan fafatawa da ɗaruruwan mahalarta daga ƙasashe daban-daban....

Gwamnan jihar Gombe a Najeriya Muhammadu Inuwa Yahaya ya gabatar da Maryam Ibrahim Dan’azumi, mai shekaru 19, wadda ta lashe gasar Alƙur’ani ta ƙasa da ƙasa ta Sarki Abdulaziz karo na 46 a Saudiyy…

Gabanin Zaɓe: Jam’iyyun Siyasa Sun Ƙuduri Aniyar Kare Zaman Lafiyar Jihar GombeRundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta yi ki...
09/15/2026

Gabanin Zaɓe: Jam’iyyun Siyasa Sun Ƙuduri Aniyar Kare Zaman Lafiyar Jihar Gombe

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta yi kira ga jam’iyyun siyasa, ’yan takara da magoya bayansu da su guji tashin hankali, daba, kalaman ƙiyayya da duk wani nau’in rashin da’a a harkokin zaɓe, gabanin zaɓen cike gurbin kujerar Majalisar Wakilai na ranar 19 ga Satumba da kuma Babban Zaɓen 2027. Kwamishinan ’Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, mnips, fwc, psc(+), ya yi wannan kiran ne a lokacin wani taron haɗin gwiwa na tsaro da sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin hukumomin tsaro da jam’iyyun siyasa a jihar....

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta yi kira ga jam’iyyun siyasa, ’yan takara da magoya bayansu da su guji tashin hankali, daba, kalaman ƙiyayya da duk wani nau’in rashin da’a a harkokin zaɓe, gaba…

INEC Ta Ce Ta Kammala Shirye-Shiryen Zaɓen Cike Gurbi A GombeHukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta a Najeriya wato INEC, ta ce...
09/15/2026

INEC Ta Ce Ta Kammala Shirye-Shiryen Zaɓen Cike Gurbi A Gombe

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta a Najeriya wato INEC, ta ce ta kammala shirye-shiryenta domin gudanar da zaɓen cike gurbin kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya mai wakiltar Gombe, Kwami da Funakaye, wanda za a gudanar ranar Asabar. Kwamishinan Zaɓe na jihar Gombe, Alhaji Umar Mukhtar Gajiram, ne ya bayyana hakan yayin taron Kwamitin Tuntuɓa kan Tsaron Zaɓe na Ƙungiyoyin Hukumomin Tsaro, ICCES, da aka gudanar domin duba shirye-shiryen zaɓen....

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta a Najeriya wato INEC, ta ce ta kammala shirye-shiryenta domin gudanar da zaɓen cike gurbin kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya mai wakiltar Gombe, Kwami da Funakay…

Address

Washington D.C., DC
20020

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GTA Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share