Rahma TV

Rahma TV RAHMA TELEVISION FARIN CIKIN AL'UMMA. RADIO AND TV STATIONS

Domin aiko da abubuwan dake faruwa a inda kuke- 08100335970 , 07017233284
Domin samun sahihan labarai da shirye shirye kasance da Rahma TV da Rahma Radio 97.3FM dake Facebook da YouTube ko website a www.Rahma Tv.com

25/10/2025
25/10/2025

Shirin Lafiya Babbar Ni'ima.

Tare da Dr.Mahmoud Kawu Magashi Likita Mai Kula da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu daga Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano,(AKTH).

25/10/2025

KANU

Majalisar dattawa na zurfafa bincike kan zargin rashin daidaito a tsarin
daukar ma’aikata aiki aa hukumar Fansho ta Kasa.

Asusun bada lamuni na duniya IMF ya gargadi Najeriya da ta kula da
yadda bashin da ake karba ke ƙaruwa,

Gwamnan jihar Borno Babagana Zulum ya yi kira ga gwamnatin tarayya
da ta ɗauki matakin gaggawa wajen nazari tare da gyara harkokin
tsaron sararin samaniyar ƙasar nan

Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zaria, ta ƙaryata zargin cewa tana da
hannu wajen wani shiri na sirri domin haɗa makamin nukiliya a Nijeriya.

ASABAR
3 ga watan Jumada Ula 1447
25 ga watan Oktoban 2025

Gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusif, ya umarci dukkanin Sarakunan jihar da su ci gaba da gudanar da bikin hawa...
25/10/2025

Gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusif, ya umarci dukkanin Sarakunan jihar da su ci gaba da gudanar da bikin hawan sallah a kowacce shekara, domin tabbatar da ci gaba da adanawa da kuma yada al’adun gargajiyar Jihar.



Gwamna Yusif ya bayar da umarnin ne a wajen bude taron bikin Kalankuwa (KANFEST 2025), wanda aka shirya domin nuna ɗumbin al’adun Kano da ƙarfafa masu fasaha, da haɗa kan matasa da mata tare da gina haɗin guiwa ta duniya wacce za ta ɗora Kano a taswirar al’adu ta duniya.

25/10/2025

Shirin Mikiya.

Fashin baki kan sauye -sauyen Hafsoshin tsaro da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu yayi.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Ibrahim Mohamed, ya fitar yace sauyin ya fara aiki nan take.Sanarwar ta b...
25/10/2025

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Ibrahim Mohamed, ya fitar yace sauyin ya fara aiki nan take.

Sanarwar ta bayyana cewa an nada Adnan Nahabu a matsayin Kwamishinan Ilimi Mai Zurfi, Na Sana’a da Fasaha, yayin da Farfesa Ahmad Muhammad Bakori, wanda a baya ya shugabanci Ma’aikatar Noma da Bunƙasa Kiwo, yanzu zai jagoranci sabuwar Ma’aikatar Bunƙasa Kiwon dabbobi.

Haka kuma, an mayar da Aliyu Lawal Zakari daga Ma’aikatar Matasa da Wasanni zuwa Ma’aikatar Noma, yayin da Zainab Musa Musawa aka sauyata daga Ma’aikatar Ilimin Firamare da Sakandare zuwa Ma’aikatar ayyuka na Musamman.

Sakatariyar Hukumar kula da Kiwon Lafiya da Muhalli na Abuja Dr. Adedolapo Fasawe, ce ta  bayyana hakan yayin da ta ke z...
25/10/2025

Sakatariyar Hukumar kula da Kiwon Lafiya da Muhalli na Abuja Dr. Adedolapo Fasawe, ce ta bayyana hakan yayin da ta ke zantawa da manema labarai a ranar Juma’a, bayan kammala taron kwamitin zartarwa na hukumar kula da Birnin Tarayya Abuja wanda Ministan FCT, Nyesom Wike, ya jagoranta.

A cewarta hukumar kula da Birnin tarayya Abuja ta amince da sayen sabbin motocin jigilar majinyata zuwa Asibiti guda 12 wadanda su ke da cikakkun kayan aiki da kuma motocin daukar gawa na zamani.

Dr Fasawe ta ce samar da motocin zai taimaka wajen kai daukin gaggawa ga majinyata domin Jigilarsu zuwa Asibiti da kuma aiyukan daukar gawa har zuwa yankunan karkara da ke Abuja.

25/10/2025

KANUN LABARAI

Biyo bayan canja manyan shugabannin rundunonin tsaron kasar nan da
shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu yayi, Manyan sojoji masu mukamin
Janaral za suyi ritayar dole .

Gwamnatin jihar Jigawa ta buɗe tsarin neman kwangila don gudanar da
ayyukan wutar lantarki a ƙauyuka 11 a fadin jihar

Jam’iyyar Accord ta yi kira ga sabon shugaban hukumar zabe mai
zaman kanta ta ƙasa (INEC), da ya cika kyakkyawan fatan da ’yan
Najeriya ke da shi wajen gudanar da zaɓe mai inganci.

Shirye shirye sun kammala domin kulla yarjejeniyar bunkasa harkokin
kimiyya da fasaha da Kuma kirkira tsakanin Najeirya da kungiyar
tarayyar Turai wato EU.

ASABAR
3 ga watan Jumada Ula 1447
25 ga watan Oktoban 2025

Dama tun lokacin dana dawo tsarin Ja'oji na tabbatar da cewa ni Sanisco na Ja'oji ne kawai, harna kaddamar da sunana nak...
25/10/2025

Dama tun lokacin dana dawo tsarin Ja'oji na tabbatar da cewa ni Sanisco na Ja'oji ne kawai, harna kaddamar da sunana nakoma Sanisco na Ja'oji.

Yanzu naga siyasa a karamar hukumar tarauni Ta 'dauki wani layi na munafurci, wallahi tallahi bana tare da kowa a karamar hukumar tarauni sai Ja'oji kawai, karkashin umarninsa nake.

Mal. Nasir Ja'oji shine mutum daya tilo da yasan darajar 'dan adam a karamar hukumar tarauni, shine mutum na farko da yasama mana 'yanci a siyasasance a karamar hukumar tarauni dama jihar kano baki daya.

Bansan kowa ba, bana tare da kowa, Ja'oji kawai nasani, shi yasan darajata data iyayena, shi yake mutuntani da bani duk wata kulawa, Ja'oji kawai Ja'oji kurum.

Daga yanzu nadawo da rigar rashin mutuncin dana cire na ajiye abaya, duk wanda yafasa taba martabar uban gidana ubansa yadaki hancin uwatar kowaye shi.

Sakon Sanisco Na Ja'oji Kawai.

A rahotonsa da ya fitar ayayin taron tattalin Arziki da ya gudana a birnin Washington DC na Amurka, Asusun ba da lamuni ...
25/10/2025

A rahotonsa da ya fitar ayayin taron tattalin Arziki da ya gudana a birnin Washington DC na Amurka, Asusun ba da lamuni na duniya IMF ya kada Kuri'ar gamsuwa matsakaiciya ga matakan farfado da tattalin arziki da Nigeria ta ke dauka a 2025.

Daraktan Asusun Ba da lamuni na duniya da ke kula da Kasashen Afirka, Abebe Selassie ya ce IMF ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Nigeria zai habaka da kaso uku da Digo tara a cikin dari sabanin kaso uku da digo hudu daa cikin dari da aka fuskanta a cikin watan yuli na shekarar nan ta 2025.

A cewar IMF hakan kuwa na da nasab da karuwar adadin man da Nigeria ta ke hakowa da kuma karuwar masu zuba jari daga tsakiyar shekarar 2023.

Sai dai kuma Asusun na IMF ya yi gargadin cewa akwai rauni a harkokin hadahadar kudade a Nigeria da kuma karuwar Dimbin Bashi wadanda su ke da hadari ga kokarin da Kasar ta ke na farfadowa daga komabayan tattalin arziki idan har ba a nuna kwarewa wajen tunkarar matsalar hakan ba.

Jakadan Tarayyar Turai a Najeirya da ECOWAS Gautier Mignot ne ya bayyana haka a yayin taron baje kolin bincike karo na 1...
25/10/2025

Jakadan Tarayyar Turai a Najeirya da ECOWAS Gautier Mignot ne ya bayyana haka a yayin taron baje kolin bincike karo na 18 da ya gudana a jihar Lagos.

Mignot yace yarjejeniyar zata bada dama wurin Samar da hadakar bincike da musayar ilimi da zuba jari a fannin ci gaban fasaha.

Yace hadakar Najeriya da tarayyar Turai zata taimaka wurin karfafar kanana da manyan masu bincike ta yadda za'a aiwatar da binciken da aka gudanar zuwa ga matakin aiki, musamman a fannonin fasahar sadarwa ta AI da sabunta makamashi da Kuma harkokin lafiya.

Jakadan yace, tuni tarayyar ta Turai EU da sauran ƙasashe mambobin ta s**a yi nisa wurin zuba jari kan harkokin bincike a'a kasashen su, Wanda Kuma suke alfaharin yin aiki tare da Najeriya.

An gudanar da buɗe shirin ne ta hannun hukumar samar da wutar lantarki a ƙauyuka ta jiha, a matsayin wani ɓangare na man...
25/10/2025

An gudanar da buɗe shirin ne ta hannun hukumar samar da wutar lantarki a ƙauyuka ta jiha, a matsayin wani ɓangare na manufofin gwamnati na samar da muhimman kayan more rayuwa kamar wutar lantarki mai ɗorewa.

Wannan shiri yana da nufin bunkasa masana’antu ƙanana da kuma ƙarfafa cigaban tattalin arzikin jama’a.

Ayyukan sun haɗa da gyara da sabunta na’urorin wuta da layukan kebul a wasu ƙauyuka da s**a dade fiye da shekaru goma ba tare da samun wutar lantarki ba, sakamakon lalacewar da iska mai ƙarfi ta jawo a baya.

Address

Kano

Telephone

+2348023724111

Website

http://www.youtube.com/@rahmaTv1

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Rahma TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Rahma TV:

Share