Littafin Abokin fira Na Fatima Dahiru Funtuwa

Littafin Abokin fira Na Fatima Dahiru Funtuwa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Littafin Abokin fira Na Fatima Dahiru Funtuwa, Lagos.

Sunana Fatima Dahiru Funtuwa, an haifeni a 1997, tun tasowata inada sha'awar rubutu, ina godiya ga Allah da yayini a marubuciya, Allah ya 'kara mani fasaha da juriya tare da sauran marubuta, ya kuma cika mana burinmu na Al-kairi

18/05/2025

With Malam Geenty Zaria โ€“ I just got recognized as one of their top fans!

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“                          NAFATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA Page      39            Hajiyar taci gaba da cew...
15/05/2025

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“

NA

FATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 39



Hajiyar taci gaba da cewa "Ni kin ganni nan mu uku ne wurin mujin mu, amma ba'a ta'ba jin wata hayaniya ta fito damu waje ba, muna zamanmu lafiya da mujin mu, amma ita daga anyi mata kishiya ฤ‘aya kawai, duk tazo ta hargitsa mana unguwa!! ta tada hankalin kowa! Muna zamanmu lafiy! Kaih!! Wannan ba'kin kishi nata dai Allah wadaran shi!! gashi nan zai ja mata muguwar nadama! Kisan kai!! Kisan kai!!!saboda kishi? Kaih!! Wannan mata wallahi ta bada mata!!!Zatayi dana sani!! Mujin da take ta'k**a dashi 'karshen ta ta rasa shi har abada! Zaman gidan yari ya same ta!! kitnga mujin da take kishi akanshi saima ya auri mata huฤ‘u in yaso, onii Nafisa yau naga tashin hankali!!!"

Kafin kace miye wannan, unguwa ta kuma cika, fiye da ฤ‘azun, kowa na faฤ‘in Al-barkacin bakin shi.

Waฤ‘anda basuga hayaniyar da H-Amina tayi ba ฤ‘azun sunata tambaya, waฤ‘anda kuma s**a sani sunata 'kara bada labarin abinda H-Amina tazo tayi ฤ‘azun, jama'a nata Allah wadai da irin wannan ba'kin kishin nata.

Cikin mintina Ashirin da faruwar wannan abu, saiga motar 'yan sanda, kai tsaye s**a shiga ciki, don suga gawar, daga bisani su mi'ka ma likitoci, su wuce da ita Asibiti.

Haka akayi wannan yammaci cikin tashin hankali,awannan gari.........

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“                          NAFATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA Page      38                 Cikin kuka Mama Jum...
15/05/2025

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“

NA

FATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 38



Cikin kuka Mama Jummai ta ce "WACECE?"

Ya ce "Kishiyar ta mana!Matar mujin ta, ฤ‘azun tazo nan taita hayaniya harta tatara mutane, tana cewa saita kasheta, nan dai aka lallasheta, mun ฤ‘auka ma ta ha'kura ta tafi, ashe saida ta dawo ta kasheta ฤ‘in!!"

Mama jummai ta ce "Kishiyar tatace tazo gidan nan?"

Ya ce "Kwarai kuwa, don akwai waฤ‘anda s**a ganta da yawa, har tana ikirarin saita kashe ta! Bari in shiga in sanar da masu gidan nan, don suji abinda hayaniyar ฤ‘azun ta haifar."

Ya wuce cikin gidan da gudu-gudu, yana salati.

Nan-da-nan sai gashi ya fito tare da masu gidan, cikin sauri.

Koda s**azo mama jummai tazame 'kasa tanata kuka iya 'karfin ta.

Hajiya (matar gidan) ta ce "Kece mahaifiyar amaryar ko?"

Sannan tayi salati, tare da faฤ‘in s**au wasu matan ina zasu kai rayuwar su da irin wannan 'kazamin kishin?Ta kasheta kikace ko?"

Mama jummai ta ce. "Wallahi ta kasheta!! Bamu daฤ‘e da gama yin waya da ita ba, tace min inzo akwai matsala!!!Ashe ba zamu haฤ‘u da itaba!!"

Hajiya ta ce "Gaskiya tsakani da Allah wasu matan dai suna bada kansu!! Ina zamu kai rayuwarmu ne wai!? me zamu samu a duniyar nanne wai?"

Sannan ta koma da kallon ta zuwa ga mai gidanta, ta ce

"Alhaji a sanar da jami'an tsaro don su shigo suga abinda ya faru."

Shi kuwa dama yana nan ya rasa gurin tsayuwa, duk ya daburce, ya dauko wayar shi donya sanar da 'yan sanda.

Hajiyar taci gaba da cewa "Ni kin ganni nan mu uku ne wurin mujin mu, amma ba'a ta'ba jin wata hayaniya ta fito damu waje ba, muna zamanmu lafiya da mujin mu, amma ita daga anyi mata kishiya ฤ‘aya kawai, duk tazo ta hargitsa mana unguwa!! ta tada hankalin kowa! Muna zamanmu lafiy! Kaih!! Wannan ba'kin kishi nata dai Allah wadaran shi!! gashi nan zai ja mata muguwar nadama! Kisan kai!! Kisan kai

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“                          NAFATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA Page      37              Ta shiga tanata sallam...
11/05/2025

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“

NA

FATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 37



Ta shiga tanata sallama, bataji an kar'ba ba, tayi tsaye 'kofar falon tana sallama taji shiru, don haka sai ta shiga, a zaton ta ko Mariyar ta shiga kewaye ne.

Ta samu kujera ta zauna, shiru bataji motsin mutum ba, saita ฤ‘auki waya ta kira number Mariyar, harta gama ringing ba'a ฤ‘aga ba.

Ta ce "Aah! To wai lafiya?yanzunfa ta kira ni,ina kuma taje ne?"

Ta 'kara ha'kuri k**ar na mintina goma, don jiran Mariyar wai ko wani wuri ta shiga, amma shiru kakeji, don cikin gidan ma babu alamar motsin kowa, saita mi'ke tsaye tana kwala kira.

"Mariya! Mariya!! Mariya!!!
Taji shiru kawai saita shige ฤ‘akin.

kwance ta ganta a bisa gado
MALE-MALE CIKIN JINI, ga kuma wu'ka nan ajiye a gefen ta.

Mama jummai ta fasa wata gigitacciyar 'kara, tare da faฤ‘in Mariya!!!! La'ilaha illallahu muhammadurrasulillahi sallallahu alaihiwasallam!!!!!
Mariya!!!! tasa hannu ta juyo da ita, saita tafi yaraff! Alamar babu rai a jikin ta.

"Na shiga ukku Mariya waya kasheki!! ta fasa kuka sosai tana neman ฤ‘auki.

Tayo waje a guje, tana shaidama mutane, tana a taimaka mata.

To dayake unguwar ba mutane sosai, gidaje ko ina arufe.

Inbanda hayaniyar da H-Amina tazo tayi ฤ‘azun ta tara mutane, to yanzun kuma kowa ya k**a gaban shi, ba kowa a layin.

Don haka ta nufi 'kofar wani gida, tana bubbuga get ฤ‘in gidan, cikin sauri mai gadin gidan ya fito.

Ta 'kara fashewa da kuka, tana yimai nuni da gidan da Mariya take, tana cewa

"Don Allah ka taimakeni!!An kashe mani 'yata a can gidan!!"

Ganin ta nuna mai gidan kuma ta ambaci kisa, yayi saurin dafe kanshi, yana salati, ya ce

"Yanzun nan matar nan saida ta aikata wannan ฤ‘anyen aikin? mu munzacima ta tafi!yanzun nan saida ta tsaya ta kashe taฤ‘in?"

Cikin kuka Mama Jummai ta ce "WACECE?"

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“                          NAFATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA Page      36       "AA Mariya, kidai bari, inda ...
11/05/2025

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“

NA

FATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 36

"AA Mariya, kidai bari, inda zan fara biyawa ฤ‘in yanada muhimmanci sosai, sannan ta katse kiran, tana 'kara yin 'kwata, ta ce "Lallai kam! dani ake magana."

Ita kuwa mama jummai cewa tayi "Heeey!! Lallai kam!!Dama nasan ba'abinda zai hana yaron nan bai ฤ‘auki mataki ba!Amma dani yake magana, inyasan wata ai baisan wata ba!Watakan ya rikitamin yarinya a ฤ‘akinta, ya hanata zaman lafiya, wata 'kila ma ture yayi mata, ake bata tsoro a cikin gidan, bari dai inje in gani, don gara inyi maganin abin tunda wuri, shiyasa yanzun ma kafin in isa wurinta saina biya wurin boka na, nakai mashi bayani, donya ฤ‘aukar mani mataki akan yaron nan (Hashimu) don ba shakka ba kowa bane shine.

Ta ฤ‘aga matashin kanta ta ฤ‘auko kuฤi, ta 'kirga naira dubu goma ta fita da ita.

Bata zame ko ina ba sai gidan mai maganin ta.

Ta ce "Boka akwai matsala!Yanzun yarinyarnan Mariya take kira na, tace inyi maza-maza inje gidan ta akwai gagarumar matsala! Nina tabbatar yaron nan bazai barta hakananba, shiyasa nazo ka taimakamin, asamu yarinyar nan ta zauna ฤ‘akin ta lafiya, inba haka ba kuwa zamuga samu muga rashi."

Boka ya ce "Ki kwantar da hankalin ki, tunda kikazonan komai ya biya, maganar zaman lafiyar 'yarki a ฤ‘akin mujinta angama!! bawanda ya isa ya tada ta, indai kina tare dani."

Ta ce "Kuma Boka so nake a.mantar da Hashimu cewa ya ta'ba son yarinyar nan, ya manta da ita kwata-kwata, don inba haka ba, nima bazai barni in zauna lafiya ba, don ranar bikin tafa har somewa yayi."

Boka yace "Indan wannan ne ba matsala."

Ya ฤ‘auki 'yan saddabarun dazai bata ya mi'ka mata.

Ita kuma ta karba tana farin ciki, ta tafi ta samu adai-daita sahu ta hau.

Bata zame ko inaba sai gidan 'yarta Mariya.

Ta shiga tanata sallama, bataji an kar'ba ba, tayi tsaye 'kofar falon tana sallama taji shiru, don haka sai

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“                          NAFATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA Page    35      H-Amina ta kalleta ta ce "Ki biy...
11/05/2025

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“

NA

FATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 35

H-Amina ta kalleta ta ce "Ki biyo ni bashi, duk ranar da muka sake haฤ‘uwa, zan gaya maki, yanzun lokaci ya 'kure mani."

Halima ta ce "Gaskiya kin bani labarin dazai daฤ‘e Mani a zuciyata, Allah dai ya kiyaye."

Sannan ta fito daga cikin motar.

H-Amina ta ฤ‘auki hanyar komawa Kano daga Manumfashi.

BAYAN AWANNI UKKU

Mariya ce keta kai da komowa cikin falon ta, hannun ta ri'ke da waya, tanata latsawa, zuwa can ta kanga ta a kunnan ta, harta kusa yankewa ba'a ฤ‘aga ba, taci gaba da kewaye a falon, tana 'kwata tana tsaki, rannan nata a 'bace, da ganinta cikin masifa take, ta tsaya wuri ฤ‘aya tana karkaฤ‘a 'kafa.

Tace "Waini ฤ‘in?! Hummf!Ba'a sanni ba wallahi!!"

Sannan ta 'kara kiran number da take nema, harta kusa yankewa sannan aka ฤ‘aga.

Ta ce "Mamammu tun ฤ‘azu inata neman ki a waya, baki ฤ‘aga ba!!"

Mama Jummai ta ce "Mariya bani gidan ne, yanzun na shugo, wayar kuma na barta tana caji, lafiya dai ko?"

Mariya ta ce Bata!!Mamammu ba lafiya!! gaba ฤ‘aya na 'kosa in ganki, in gaya maki damuwata, don Allah Mama ki tafo yanzun."

"Wani abune ya faru Mariya??"

Mariya Ta ce "AA nidai Mama kawai sai kinzo, maganar bata waya bace."

Mama jummai ta ce ince dai ba yaron nan bane Hashimu?"

Mariya ta ce Mama kedai kizo kawai, ba wanda nake so in gayama damuwa ta saike, kiyi maza-maza don Allah kizo kar in huce!!"

"To shikenan Mariya ki bani mintina talatin, don in biya wani wuri tukunna, sannan inzo."

Mariya ta ce "Mama da dai kin fara zuwa nan ฤ‘in."

"AA Mariya, kidai bari, inda zan fara biyawa ฤ‘in yanada muhimmanci sosai, sannan ta katse kiran, tana 'kara yin 'kwata, ta ce "Lallai kam! dani ake magana."

Ita kuwa mama jummai cewa

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“                          NAFATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA Page    34*+*+*+*+*+*+*+++*+*+*+*+*+*+*+    Shi ...
11/05/2025

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“

NA

FATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 34

*+*+*+*+*+*+*+++*+*+*+*+*+*+*+

Shi yasa nake son Alhaji Mansur, domin shi mutum ne wanda ya iya lallashin mace, ya iya tarairaya, ya iya kalamai, kuma koda yaushe jin shi yake tamkar wani saurayi, yasan kaina da yawa, ko wane irin 'bacin rai na shiga yasan yadda zaiyi ya lallashe ni, gashi da kissa k**ar mace, shiyasa kullun nake 'kara son shi, nake kuma kishin shi.

Amma duk da haka saida ya zagaye yaje ya auri wata!!!

Halima Tabbass!! danasan wannan labarin kafin auren nan, saina lalatashi!! Ba yadda za'ayi in bari ayi shi! nasan shiyasa ya 'boye mani.

Hankalina yana tashi idan na tuna irin kalamai masu daฤ‘i dayake yawan faฤ‘amani a kunnena, sai in tuna cewa ya auri wata, tsawon kwana biyar, itama yana karanta mata irinsu a kunnuwanta, ya tona mani Asiri!!!!"

Dai-dai nan tari ya sar'ke ta, tare da fitar wasu zafafan hawaye, da s**a jika mata kuncin ta.

Halima tahau lallashinta tana fadin.

"Kiyi ha'kuri, karki tadama kanki hankali, donshi namiji babu ruwanshi! sai ya Tarwatsaki!!! Ya haddasa maki ciwon zuciya! kuma ba'abunda yadame shi! Kaih!! Namiji dai-Namiji dai mayaudarine!! Wallahi ya cuceki! Kwana Biyar!yanata sharholiyarsa da amarya bai sanar dake ba!! Hajiya idan kikaga mace da wani hawan jini, ko ciwon zuciya sanadinshi namiji ne, ki ฤ‘auki duk matakin daya k**ata akanshi, ina goyon bayanki! Na tabbata kuma yau ฤ‘in nan saiya biyo ki har kano."

H-Amina ta ce "To me zaiyimin??"

Halima ta ce"Yo me fa zaiyi maki? In banda kalaman yaudara da dama can yaudarar ki yake, aiya gama dake kawai!Sai-dai ki saurareshi kawai!!"

Dai-dai nan ta duba agogon motar ta, ta ce "Yamma tayi, ya k**ata in wuce, bana so inyi dare sosai a hanya."

Halima ta ce "Aff! To ai baki gayamin WACECE MARIYA BA?"

H-Amina ta kalleta ta ce "Ki biyo ni bashi, duk ranar da muka sake haฤ‘uwa,

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“                          NAFATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA Page    33      Nace nifa indai harka da mata ne...
11/05/2025

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“

NA

FATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 33

Nace nifa indai harka da mata ne zan iya cewa kasuwancin ma abarshi!!"

Ya ce "Wannan ma data kira ni a waya ba 'yar nan bace, daga Lagos take zanyi oder wasu kaya ne."

Nace "Wai Alhaji mansur suwa kake nemamma kuฤ‘in nan ne?"

Yace "Ke mana da 'ya'yan ki."

Nace "To zan iya cewa abar neman kuฤ‘in! Kadawo ka zauna cikin gida kullun in tasa ka gaba ina kallon ka, donni gara mu zauna a haka zaifi yemin kwanciyar hankali!!!"


Wannan maganar saida ta bashi dariya, ya 'kara janyo ni a jikinshi yana faฤ‘in, "Aiko wata rana da kanki zaki kore ni, in zo dai in tare maki a cikin gida, habawa ai kema kin faฤ‘a ne, Amina gaba ฤ‘aya na rasa gane irin wannan kishi naki, kuma a zaman da mukayi dake fiye da shekara Talatin, ai ya k**ata ace kin sanyaya zuciyar ki, kin tabbatar da cewa ni bazan yi maki kishiya ba, domin da zanyi da tuni nayi, don Allah Amina ki rage wannan zafin kishin naki."

Humf! nayi ajiyar numfashi, nace "Haka ne, amma wani lokacin ne idan raina ya 'baci akan kishin ka bansan ma ina yin wani abun ba, don gaba ฤ‘aya idona rufewa yake."

Ya ce "To ki buฤ‘e shi kinji ko? Uwar gidan Alhaji Mansur!kuma amarya, babu wata bayan ke, zinariya sarauniyar mata!"

Haka ya cikani da kirari k**ar yadda ya saba, har saida yaga nayi dariya.

Ya ce "Wohoho!! Sarkin kishi, amma ba laifin ki bane, laifin soyayya tane da tayi maki wawan kamu, ni kuma nasan dole sai ana son mutum ake kishin sa."

Nace ai gara dai daka gane hakan, saida ya kwantar min da hankali sosai."

*+*+*+*+*+*+*+++*+*+*+*+*+*+*+

Shi yasa nake son Alhaji Mansur, domin shi mutum ne wanda ya iya lallashin mace, ya iya tarairaya, ya iya kalamai, kuma koda yaushe jin shi yake tamkar wani saurayi, yasan kaina da yawa, ko wane irin 'bacin rai na shiga yasan yadda zaiyi ya lallashe ni, gashi da kissa k**ar mace, shiyasa kullun

07/05/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Safiyanu Isah Sheme, Hamrat Faruq, Bunu Baba Kura, Muhamad Rabiu, Hadiza Saidu

๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’ RAYUWAR  SUBAI'AH ๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’  ๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’            NA           ๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’Fatima Dahiru  Funtuwa  Binta๐Ÿ’Page      1      ๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’  2025  ๐Ÿ’๐Ÿ’...
07/05/2025

๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’ RAYUWAR SUBAI'AH ๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’


๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’ NA ๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’

๐Ÿ’Fatima Dahiru Funtuwa Binta๐Ÿ’

Page 1

๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’ 2025 ๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’

ROMANTIC STORY



Wanda baiyi Following ฤ‘ina ba ga link nan ๐Ÿ‘‡

https://www.facebook.com/profile.php?id=61561249522359

Godiya ta tabbata ga Allah mai kowa mai komai daya sake haฤ‘amu cikin wani sabon littafin, tsira da amincin Allah su 'kara tabbata ga shugaban mu Annabin rahama Muhammad (S A W) da sahabban shi da iyalan gidan shi baki ฤ‘aya.

Masoyana inayi mana barka da shigowa sabuwar shekara, Allah ya sadamu da Al-kairan da suke cikin ta.

๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’ Zaune take tana ninke kayan makarantar 'Kannan ta da s**a taso yanzun bada jimawa ba.

Subai'ah ce ta shigo ฤ‘akin tare da faฤ‘in "Kinganni na shigo yanzun ko? Daga tasowa makaranta, nazo kiyimin turi, wane littafi- da wane littafi gareki? Allah dai yasa kinada masu zafi na soyayya."

Asiya ta ce "Dazun na samo wani littafi mai ban Al-ajabi, idan kina karanta shi saikin 'kosa kiji ci gaban shi."

Subai'ah ta ce "Ni duk ba wannan ba, a kwai zazzafar soyayya da rayuwar Aure a ciki? Kinsan nifa bana so ina karanta littafi inji salaf! Nafi so inji ana love ana romantic, inji rayuwar Aure faca-faca a ciki, haba! Ai shine labari."

Asiya ta ce "Allah ya shirye ki Subai'ah, ke ba matar Aure ba, amma ki zauna kina karanta labarin dazai tada maki hankali, kuma kina sane marubutan ma har kashedi sukeyi da kada 'yan mata su karanta masu littafi, amma ke baki jin magana, Allah ya shirye ki, su dai marubuta sun fita ha'k'kin ki, tunda sunce kada ki karanta."

"Attakbiiir!! Kin gama wa'azin, ai ni har so nake inga marubuciya tayi kashedin kada 'yan mata su karanta mata littafi, to ni irin shi nake nema don inji uban me aka rubuta da ba'a so mu sani, in gorin Aure ne ai dai muma zamuyi ehee! Don haka gara in sani, kada inje ma mujina ina gidadanci๐Ÿ’ƒ. Don Allah Asiya turamin littafin sauri nake, ina so inje infara sh

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“                          NAFATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA Page    32         Shekarata Talatin da biyar da...
05/05/2025

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“

NA

FATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 32

Shekarata Talatin da biyar dashi a yanzun haka, haihuwata bakwai tare da shi, ina cikin jin daฤ‘i da kwanciyar hankali sosai, kuma arzi'kin mu koda yaushe 'kara gaba yake, don yanzun Mansur ya fita daga 'kar'kashin Abba na, ya buฤ‘e nashi, don haka gashin kansa yake ci yanzun.

Ni mace ce mai kishi!k**ar yadda yake cewa, na tare gaba na tare baya, bana yadda ko wace mace in ganta da muji na, inba da wani kwakwkwaran dalili ba.

Na kasance ina bibiyar wayar shi, a kowane lokacin duk da dai ina jin na yarda dashi, amma sabo da tsaro, kuma koda yaushe yana 'kara gaya min in kwantar da hankali na, indai maganar aure ce ai shi ya riga ya auru, ba wata macen da zai 'kara gani ta burge shi.

Rannan naje shiga ฤ‘akinshi, kawai sai nayi kicibis!Dashi yana waya da mace.

"Alhaji miye nake ji haka?"

Cikin sauri ya kauda wayar daga kunnanshi, tare dayin wata irin dariya.

Ya ce "Lafiya dai Hajiya?"

Na ce "A ah! nikai nake tambaya, ya nake jin k**ar muryar mace a wayar ka?"

Ya taso a hankali, Ya k**a hannaye na, ya ce "To inbanda abinki jin muryar mace a waya ta wani sabon abune?"

Nayi mai wani irin kallo, nace "Banganeba!"

Ya ce "To amma a matsayi na name kasuwanci, mai harka da mutane kala-kala, ai dole ne kiji murya koma ta wace ce."

Nayi sairin fizge hannu na daga nashi, nace "To anzo wurin! Dama ina jiran haka!Nagaji Alhaji mansur na gaji!!Harka kowace iri ce indai zata haฤ‘aka cuฤ‘anya da mata, to na yafe ta!! Gara abarta kwata-kwata!! Don ni bazan amince da wannan ba!!"

Ya ce "Kin ta'ba ganin inda kasuwanci ya kasance a haka?Ace sai an ware wasu jinsi waฤ‘anda su kaฤ‘ai ne za'ayi mu'amala dasu? Haba Amina jimana, ki kwantar da hankalin ki, yanzun yawancin kasuwancin ma matane, Uwum! Don Allah ki yarda mana."

Nace nifa indai harka da mata ne zan iya cewa kasuwancin ma

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“                          NAFATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA Page    31         Nayi murmushi cike da jin daฤ‘...
05/05/2025

๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“ RUฤŽANI ๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“๐ŸŽ“

NA

FATIMA ฤŽAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 31

Nayi murmushi cike da jin daฤ‘in waฤ‘an nan kalamai nashi, nace "Alhaji Mansur idan da sabo na saba da irin wannan koฤ‘awar taka, amma koda yaushe kake karanto minsu, sai in jisu tamkar sababbi, in kasance cikin jin daฤ‘i da fara'a, sai in tsinci kaina ina mai yin murmushi, idan kana yimin irin waฤ‘an nan kalaman, kuma koda cikin 'bacin rai nake, da zarar kazo shikenan ka wanke shi, nagode ma Allah da yayi haฤ‘uwa ta dakai, ya mallakamin kai a matsayin muji na, koba komai nasan zan kasance cikin farin ciki na har abada, samun jajurtaccen namiji mai sauya tunanin 'ya mace a lokaci guda, wannan babbar nasara ce a wurin kowace mace, sannan babban cikan buri na, gashi zan gama rayuwata ni kaฤ‘ai a wurin namiji, k**ar kai, wannan wani abin al-fahari ne a wuri na, yadda na tashi a gidan mu ni kaฤ‘ai na samu gata, haka zan rayu a wurin muji na ni kaฤ‘ai ba tare da gatan ya goce mani ba."

Ya ce "Ta yaya za'ayi mace k**arke a haฤ‘a soyayyar ta da wata? Idan namiji ya aikata hakan tamkar yayima kanshi gi'bi ne, kin gane abinda nake nufi? Idan mutum ya haฤ‘a ki da wata, to duk ranar daya yanke wasu kwanaki don ya kaima abokiyar zaman ki, tamkar ya yanke ma kanshi wani jin daฤ‘i ne, ya tauye kanshi sosai a wannan rana."

Har cikin kaina naji wannan maganar tayimin yawo, ya wani 'kara tsuma ni, ina jin kaina lallai ni wata ce ta daban.

Nace "Ina son ka MANSUR."


Ya ce "Nima ina son ki Amina."

Muka gama firar, sannan ya fito motar ya shiga tashi ya tafi.

Munyi Aure da Alhaji mansur, irin auren soyayyar dana saki jiki da shi, akan lallai ba wata sai fa ni ฤ‘in, k**ar yadda kullun yake 'kara shaida mani.

Shekarata Talatin da biyar dashi a yanzun haka, haihuwata bakwai tare da shi, ina cikin jin daฤ‘i da kwanciyar hankali sosai, kuma arzi'kin mu koda yaushe 'kara gaba yake, don yanzun Mansur ya fita daga 'kar'kashin A

Address

Lagos

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Littafin Abokin fira Na Fatima Dahiru Funtuwa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share