Apc Media Leads

  • Home
  • Apc Media Leads

Apc Media Leads page din da yake Tallata Aiyyukan Alheri na masu madafun iko a Jam,iyyar Apc tun daga Shugaban kasa har zuwa kansila

Kungiyar marubuta a kafar sadarwa ta zamani Apc media leads Katsina Hadin gwiwa da Dan majalissar dokoki ta jihar Katsin...
20/08/2025

Kungiyar marubuta a kafar sadarwa ta zamani Apc media leads Katsina Hadin gwiwa da Dan majalissar dokoki ta jihar Katsina Mai wakiltar karamar hukumar Katsina Hon Aliyu Albaba

tana gayyatar Al,umma domin taya Murnar kammala bada horo na sati hudu 4 da wannan Kungiyar tayi wa matasa a bangaren Graphics Design domin su rika samun kudin kashewa da wayoyin su na hannu a maimakon bata data da sukeyi ba tare da sun Amfana ba,
Wannan Taron za,ayi Shi

Ranar Lahadi 24/08/2025
Wuri Katsina local government sakatariya
Lokachi karfe 11:00 na safe

Allah ya bada ikon zuwa Ameen
Apc Media Leads ✍️✍️✍️

Idan Gwamnati Taga Dama chikin Watanni Ukku Zata iya Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Jihar Katsina Inji Shugaban kwamitin ...
02/08/2025

Idan Gwamnati Taga Dama chikin Watanni Ukku Zata iya Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Jihar Katsina Inji Shugaban kwamitin Tsaro na shekara takwas daga 2015 zuwa 2022 Dr. Mustapha Muhammad Inuwa.

Ya bayyana hakan ne a yayin ziyarar da al’ummar karamar hukumar Safana s**a kawo mashi a gidansa karkashin jagorancin Alhaji Mansur Mu’azu Safana.

Wane kokari kayi a shekara takwas da kayi a matsayin Kafi Gwamna a lokachin Gwamnatin masari

Atiku ya shiga jam’iyyar ADC ne domin ba shi da tabbacin samun tikitin takara a jam’iyyar PDP. El-Rufa’i ya  shiga ADC n...
02/08/2025

Atiku ya shiga jam’iyyar ADC ne domin ba shi da tabbacin samun tikitin takara a jam’iyyar PDP.

El-Rufa’i ya shiga ADC ne saboda Tinubu bai ba shi mukami ba Kuma Apc ta kubuche Mashi a jihar Shi

Amaechi ya koma ADC saboda Wike ya danne shi a jaharsa, kuma yana bukatar iska (oxygen).

Peter Obi yana kokarin shiga ADC ne saboda jam’iyyar LP ta fita daga hannunsa gaba ɗaya!

Jam’iyyar ADC ta zama tamkar gidan da babu UBA kowa tashi ce ta kawoshi babu mai yima wani gori saboda Sabuwar tafiya che kowa yanchin kanshi gareshi baza,a fuskanchi Abunda ya kawo kowa ba Sai lokachin takara yayi,

Shi yasa Yan siyasa da yawa suke yi Mata kirari da tsohuwar giya a chikin Sabuwar kwalba
Wasu Kuma suche
Sabuwar tafiya Sabuwar yaudara

Bazamu sanya Ido kamfanin sayar da Hasken wutar lantarki ya rika tilasta ma talakkawa biyan kudin Wutar lantarkin da Bas...
01/08/2025

Bazamu sanya Ido kamfanin sayar da Hasken wutar lantarki ya rika tilasta ma talakkawa biyan kudin Wutar lantarkin da Basuyi Amfani dashi Ba
Hon Aliyu Albaba

Ba Zamu yarda da Shirin da kamfanin sayar da Hasken wutar lantarki na (kedco) tazo dashi ba na biyan kudin Wuta kaso 💯 inji Dan majalissar dokoki na jihar Katsina mai wakiltar karamar hukumar Katsina Hon Aliyu Abubakar Albaba.

Yayi wannan jawabin ne ga manema labarai inda yake cewa Hukumar Dake bada Hasken wutar lantarki tazo da wani tsari Wanda duk Mai Amfani da wutar lantarki sai ya biya Abinda ke Cikin Bill din shi baki daya
Inda yache wannan ba kyautawa bache saboda kamfanin sayar da Hasken wutar lantarkin Baya bada wutar koda kaso 50 ne a yini yache don haka ba Zamu yarda da wannan tsarin ba.

Haka Kuma Hon Albaba yayi kira Ga Sanatoci da yan majalisun tarayya Dasu tarbi wannan Rashin Adalcin da Ake Neman cutar da talakkawan najeria Kuma yache su hada hannu don Dakile wannan manufar ta kamfanin sayar da Hasken wutar lantarki don gudun jefa Al,umma chikin kunchi,

Hukumar   ta Bude bangaren Amsar korafin Al,umma domin tsabtace Aikin,Hukumar Kiyaye Hadurra ta Jihar Katsina (KASSAROTA...
25/07/2025

Hukumar ta Bude bangaren Amsar korafin Al,umma domin tsabtace Aikin,

Hukumar Kiyaye Hadurra ta Jihar Katsina (KASSAROTA) karkashin Jagoranchin D,G Yahaya Garba Garba ta kirkiro Sabon sashen kula da korafe korafen Al'umma. Sashen wanda yake karkashin ofishin Jami'in Hulda da Jama'a na Hukumar, zai yi aiki don karbar korafe korafen Al'ummar Akan yanda jami'an Hukumar suke gudanar da ayyukansu, matsalolin cin hanci da rashawa, amfani da karfi ko matakan da basu dace ba na tursasawa al'umma, ko rashin bin ka'idojin aiki a yayin gudanar da ayyukansu.

Kuma zaku iya kawo shawarwarin akan yanda za,a inganta ayyukan hukumar don tsare lafiya da dukiyoyin al'ummar Jihar Katsina. Wannan mataki yana daga cikin sabbin Matakan da Gwamnatin Malam Dikko Umaru Radda ta dauka domin inganta ayyukan hukumar da kare mutuncin al'ummar Jihar Katsina,

Kafa sashen na da nufin rage yawan korafe korafen al'umma akan cin zarafi, cin hanci da rashawa, ko sanya karfi da ya wuce ka'ida a yayin gudanar da ayyukan jami'an.
Sashen zai rika gudanar da bincike don tabbatar da sahihancin korafe korafen da kuka kawo kafin daukar matakin da ya dace akan Jami'an da abin ya shafa abunda muke bukata Ku kawo kwararan sheda ko sahihiya,

Hukumar tana Kara kira ga al'ummar Jihar Katsina musamman masu amfani da ababen hawa, da su kiyaye dokokin tukin da aka gindaya domin kare lmutunchin su ,Lafiyarsu da dukiyoyin su

daga Karshe Hukumar tana Kira ga masu ababen hawa da su cika dukkan ka'idojin da dokar kasa ta kayyade, tare da kiyaye dokokin hanya a matsayin Ka na Dan kasa Nagari domin guduwa tare da tsira tare

Mustapha Ibrahim Kofar Marusa
Media Assistant to Katsina state
Governor ministry of Works
Housing and Transport.

22/07/2025

_Sakon Jaje zuwa ga mai girma Gwamnan Jihar Katsina Mal. Dr. Dikko Umaru Radda tare da dukkanin Wadanda wannan ibtilain ya faru dasu Akan jarabtar hadari mota da ya same Su Akan hanyar Daura zuwa Katsina,

Amadadin Kungiyar Gwagware Frontiers, tare da
Al'ummar Karamar Hukumar Ingawa,
Da daukacin Al'ummar Jihar Katsina baki daya. Muna Adduar Allah ya bashi lafiya Kuma Allah ya Kara Kiyaye gaba
Sign,
. Mu'azzam Abdullahi.
Premier (Dan Gwamna)

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Ayyana Ranar Litinin 14 ga watan Yuli 2025, A Matsayin Ranar Hutu Domin Nuna Jimami Da Kuma A...
14/07/2025

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Ayyana Ranar Litinin 14 ga watan Yuli 2025, A Matsayin Ranar Hutu Domin Nuna Jimami Da Kuma Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata takarda da daraktan yaɗa labarai na Ofishin sakataren gwamnatin jihar Katsina Abdullahi Aliyu Yar'adua, ya sanya ma hannu.

Takardar ta kuma ce Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, yana ƙara taya al'ummar jihar Katsina jimami da kuma alhinin rashin tsohon shugaban ƙasar, tare da yin addu'ar Allah SWT ya jikan shi da rahama.

Shugaba Karama Hukumar Katsina Hon Isah Miqdad AD Saude  ya kula yarjejeniyar haɗin gwiwa da Gidauniyar UNICEF domin tal...
08/07/2025

Shugaba Karama Hukumar Katsina Hon Isah Miqdad AD Saude ya kula yarjejeniyar haɗin gwiwa da Gidauniyar UNICEF domin tallafa wa ilimin yara, musamman mata, tare da taimaka musu wajen samun ci gaba a fannoni daban-daban na koyon Sanao,i

Hon Aliyu Albaba yayi Kira ga Gwamnatin jihar Katsina da ta fidda Hanyoyin Ruwa a Unguwannin Janbango da Rahamawa domin ...
08/07/2025

Hon Aliyu Albaba yayi Kira ga Gwamnatin jihar Katsina da ta fidda Hanyoyin Ruwa a Unguwannin Janbango da Rahamawa domin gudun Ambaliya,

Dan majalisar Dokoki mai wakiltar karamar hukumar Katsina a zauren majalissar jiha Hon Aliyu Abubakar Albaba ya Gabatar da kuduri wato (motion) A Gaban zaure. majalisa na kira ga Gowamnatin jihar katsina ta fidda Hanyoyin Ruwa a Unguwar Jan Bango da Rahamawa duba da zaizayar kasa da suke fama da ita,

Hon Albaba ya Kara da Chewa idan ba'a Dauki matakin Gaggawa ba Al-Ummar yankin zasu iya Rasa Gidajen su ta dalilin Ambaliyar Ruwa ganin yanda damana tazo Kuma damanar tazo da Ruwa masu karfi Kuma yache kasantuwar An Rushe Jan bangon Wanda Asali shine yake tare Ruwan Baya shigowa Unguwar Amma yanzu mahadar Ruwa biyu zuwa Uku take barazana kawo Ruwa Wanda shine yake zaizaye Hanyoyin Unguwar Wanda yanzu haka ko Hanyar mota Babu,

Don haka yake kira ga Sauran membobin majalissar da su goya mashi baya a Kai wannan kuduri ga majalisar zartaswa don yin Abinda ya Dace ba tare da an dauki wani dogon lokachi ba

Lokachin da ya gabatara kudirin akwai membobin majalissar da s**a Yaba Mashi Kan wannan kudiri da ya kawo domin taimaka ma Al,ummar da yake wakilta kamar Dan majalissar karamar hukumar kankiya Dana karamar hukumar Malumfashi,

Majalissar ta tura wannan kuduri Ga majalisar zartaswa ta jiha don yin Abinda ya Dace.

Apc Media Leads
✍️✍️✍️✍️ 08//07/2025

NOTICE OF NATIONAL EXECUTIVE COMMITTEE (NEC) MEETING Date: Thursday, 24th July, 2025 Time: 11AM prompt Venue: APC Nation...
05/07/2025

NOTICE OF NATIONAL EXECUTIVE COMMITTEE (NEC) MEETING

Date: Thursday, 24th July, 2025
Time: 11AM prompt
Venue: APC National Secretariat, 40 Blantyre Street, Wuse II, Abuja.

Matasa Maza da Mata 634 Gwamnatin jihar Katsina ta koya ma Sanao,I Kala,Kala Kuma ta Basu kalar Kayan Aikin da s**a koyi...
02/07/2025

Matasa Maza da Mata 634 Gwamnatin jihar Katsina ta koya ma Sanao,I Kala,Kala Kuma ta Basu kalar Kayan Aikin da s**a koyi Sana,ar,

Gwamnan jihar Katsina Mal Dr Dr. Dikko Umaru Radda PhD Con ya Jagoranchi yaye matasan da s**a kammala makarantar koyon Sanao,I Katsina youth craft village (KYCV)
Gwamnan ya Jagoranchi yaye Dalibai NE a Yau Laraba 02/07//2005 a Babban filin Wasa na Garin Katsina Muhammad Dikko stadium

A Lokachin yayewar Gwamnan ya gargadi daliban da s**a kammala Amsar horon inda yache Kada Wanda ya sayar da Kayan Sana,ar da aka bashi domin su dogara da kansu harda Sauran dagi da iyayen
Daga karshe ya Jagoranchi bada Kayayyakin ga wasu daga chikin daliban tare da Basu takardun kammala wannan makaranta KYCV)(certificate)

Address

No 140 S Mukhtar Road Kofar Marusa Katsina

Telephone

+2347032043337

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Apc Media Leads posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Apc Media Leads:

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share